ABUNDA KE 'BOYE...

41

by @surayyahms

ABUNDA KE ƁOYE💫
arewabooks@surayyahm.


⏯️4️⃣1️⃣
wajajen yamma liss daga asibiti ayayin da na’urar E.C.G ke famar kara wata siririyar hawaye guda daya ta sulalo daga cikin idon Zainab Arifah ba tare da ta farka ba, kusan ba'a cikin hayyacinta ba tafara wani irin gane ganen mugayen halittun aljanu masu muni da matukar tsoratarwa tareda gigitarwa dakyar da wahala ta kwaco hanklinta duk dama time to time haka zakana tana yawan razana ita daya..

zazzabin ne me tsananin zafi yake yawan rufeta ta ciki haka za tay ta ɓarin sanyi, saida har tay kwana biyu akwance anan asibitin amma ba agane meke damunta cos duk dama tana jin zafin zazzabin amma duk na'uran gwaje gwaje yakan nuna musu cewa lafyarta kalau ne gabaki daya kan likitoci yabi ya kulle sosai...

babban asibitine da kwarrarun likitoci it was hard for her to believe its imcompetnce ace tanajin ciwo ajikinta snn ace wai ba aga komi ba, gashi ta hana sam a kira babanta sbda tanaso ne ita ta fara fahimtar abunda dake damunta kar ya kasance matsalarta da ibaad ne.

arana na biyun ne nala ta kirata awaya da zimman zata shimfida mata karya akan batun sihiri da sukaje yi kamar yadda ta shirya...

saidai ko samun daman furtawa batay zainab arifah ta tsareta da labarin abubuwan dake faruwa da ita da irin mafarkin datakeyi da kuma razana datakey sosai,..

bakaramin faduwa gaban nala yayi ba tace zata kira Ani qompas taji me ake ciki, after like one hour da yin wayansu nala takira zainab da rudani aranta tace mata kawai tabar asibitin taje gida ciwon bana asibiti bane Ani qompass tace zata duba musu abunda ke faruwa nan. babu shiri zainab arifah  ta tattara inata inata batama jira sallama ba ta kira drivernta aka kaita gida, she took a break from class, cut contacts, tay ma babanta karya cewa zataje boot camp a singapore har sai ta dawo zata nemesa.

tunda kuwa tay wann karyan ta dawo gida jikin ta ya zama babu kanta, dan tamkar asbitin ma yafi mata sauki dan agidan nata ne komi yafara mata afresh aljanu suna hanata baccin dare, hka kawai saitanajin motsi ko tanajin dariya, ko taji ana kiran sunanta abayan labule, koda kuma ta samu baccin daga ta kashe lamp sai taga an sake kunnawa..

she remain very scared nd traumarized lamarin daya jawo nala tazo UK tafara jawo ta cikin shaye shayen kwaya dan ya bugar da ita tana samun bacci.

rukayya kuwa tunda ta wuce dubai bata sake kiransu awaya ba, she just ghost them, gabaki daya sukuma sun bala'in tsorata sun gigice, sunkira Ani gompass yafi sau akirga amma shiruuu ba a dagawa gashi mahaifiyar nala ta dada tsoratasu, ta dinga musu masifa tace meye kaisu har wajen manyan matsafa? da ma wani local boka kawai suka nema ya musu aiki amma zuwa har can nepal dolene akwai consequences, koda kuwa aikin yayu.

sukam ma gabaki daya suka bar batun wani magani aka dawo neman wa zainab arifah mafita, dan tunda ta aje kaskon ranar shikenn ciwo ya nadeta waje guda bata kara maganansa ba, nalan ce kawai tazo suna zama tare sunajira desprately suji me Ani gompas zatakira tace musu, shiru shiru har suka ci sati guda zainab arifah gabaki daya ta dawo wata abar tausayi kullum sai tay kuka ga tsoro ya kamata sosai gashi tasha kwaya da kayan maye sosai wai danya cire mata tsoro ko yasata bacci har taji babu dadi.


karatun ta da walwalan ta gabaki daya ya tsaya cak, da tsananin damuwa tafara tunanin kawai gara ta kira gida tagaya babanta komi karta mutu ba asan asalin meya kasheta ba.

suna kan wnn rikicin da nala har tay bacci, on the 8th day sai tay mafarkin cewa drwer inta inda ta aje kaskon yana ci da wuta wutar kuma har ya kama mata jiki da wani irin balamammen tsoraccen ihu da firgici ta farka saida nala dake bacci agefenta tay wani wawan tambul ta rikoto akasa amugun tsorace tafara ihu tsakar dare.

"zainab..zainab lafya "meye haka?? jikin zainab na rawa rawa cikin tsoraccen kuka ta sauko akan gadon da sauri t tana kuka me cin rai tace nala wallah wallah i regret following ur advice wann wani irin tashin hankali ne for god sake what is happening to me... ur evil magic ppl are traumatising me..

nala zata riketa tay wani kukan kura tawanka mata mari a rikice tana kukan sosai,

da mugun fushi ta juya zata bude drawa ta dau passport dinta ta kama hanyar airpot a daren danta dawo gida tana budewa sai taga sholl babu kaskon data aje.

wani cak kukan ya tsaya mata ta daga ido a mugun tsoroce ta juyo hawauynta na zuba bakinta na rawa rawa ta kalle nala tace "na...n...n..nala The clay pot is no longer here sun dauke abunsu, .

da sauri nala ta karaso wajen tace "but dats...impossble!
arikice zainab arifah tace wallah anan na aje shi anan na aje ranar, nala tace a'a maybe ure just confused baridai mu kara dubawa..

ahujajan suka hau birkita waje tsakar dare wajajen karfe uku da rabi suka haukata dakin da dube dube saida suka leka ko ina basu gani ba..

nala tace tabbas bacewar abun nan ne ya jawo musu wann buhun bala'i atake atake sai suka laka ma masu aikin gidan laifin komi..

maids suna bacci sukaje suka daddasa musu mari suna masu tuhumarsu inda kasko yake..duk sun rikice sun ma manta da cewa rukky tazo kowa yay rantsuwa yace bai dauka ba.

Haka har safiyar ranan yay zainab da nala suna ci mata mutanen nan mutunci jira ma suke safiyar yagama washewa su mika su wa police sosai suka razana maaikatan gida har mai gadi basu kyaleshi ba

suna cikin wann rikicin ne Ani gompass ta kira, sukaje daki nala ta saka musu a handsfree tace musu basu suka dauka ba, kuma anyi musu wasa ne da aikinsu shiyasa aljanun da akayi binding sihirin dashi suke bibiyarta dan haka ta nemo wanda ta dauki abun sunan ta kawai ake bukata kuma har sai ta nemota kafin nan su samu sauki.

bakaramin rudewa zainab arifah tay ba, musmn da ta san wai zuwa gidanta akay aka dauki kaskon nan, ranar wuni sukayi suna bincike, boyayyer CCTV footage na jikin flower vase a dakin wanda ko nala bata san dashi ba shine ya nuna musu zuwan ruqayya dakin da daukarta da duk maganan da tafada.

jikinsu yana rawa rawa suka kalle juna yau bakaramin mamaki suka sha ba, dan gabaki daya a rayuwa basu taɓa kawowa cewa rukkaya zata iya aikata haka ba, cos she always appear yar baruwanta kuma yar gaskiya itace me bada shawara me kyau me gayan musu gaskiya.

kai tsaye nala ta gane cewa Rukky tana son ibaad ne shiyasa ta furta wancan maganan ita kuma zainab arifah tace sam kishi da hassada ne rukkyn ta rike ta dashi...

tunda suka gano bakin zaren suka kira Ani gompass suka gaya mata sunan rukkyn sai a sann Arifah ta dena jin wasu abubuwa ajikin ta duk dama taji zafin da tay asarar kudinta da lkcinta sosai.

Ani compass tace ma nala dama babban curse ne rukky taso tajawo ma zainab arifah data ƙona abun, sam sam bataso data kona ba, cos burning a magic is d same as destroying the spell forever dan bazata iya sake hada mata wani ba. nala bata ji dadi ba but atleast she thank God da bata gaya ma zainab arifahn Amfaninsa ba dan tasan da bakaramin bura uba zasuyi ba dan zainb arifah bazata taba yarda ace mata only chance inta na samun soyayyar ibaad kenan aka mata asararsa ba

she kept lying to her, tace mata ai yanxu maganan aiki ya dan tsaya kawai su dauki revenge akan rukky su san meyene  asalin manufarta na sace ma zainab kasko...

hassada da kishi ne ko dagske ne akan ibaad ne...dakyar suka samu nitsuwa, bayan kwana biyu suka harhada tarko sukata bincike har suka san inda taje haka suka dinga spying har saida suka san yadda zasuy ta dawo tun hutunta bai kare ba sabida zainab arifah ma tanakan shiri zata koma gida hidimar mika mata kujera da babanta yace zaiyi..

shafewar basira yasaka Rukky ta dawon kuwa after a day of convincing, taci kwlliyarta ran asabar da yamma liss tazo gidan zainab arifah, but dake zainab din bata da hakuri, tana zuwa tafara daddaure mata fuska, haka sukaje can sama  saman balcony inda babu kowa daga su saisu dama kuma sunyi niyyar daureta ne da igiyaa su mata lilis sai ta fada musu gaskiya, but zainab decided to question her akan ko dagsken ibaad take kauna.

suna hawa sama taga sun sakota a tsakiya nan aka fara magana tun anayi cikin habaici ya dawo baqaqen maganan suke jefawa junansu sosai

rukky tanata so ta juya maganan akan nala, she was busy insinuting cewa ai nala ce take zama da ita ba tsakani da Allah ba snn nala ta tsaneta tana kishinta aboye..

koda zainab ta nuna mata videon abunda ta sace mata sai bakinta ya mutu she have no choice bakinta na rawa  tafara tono asiri ta gaya mata gaskiyar cewa karyafa nala ta mata bokan nan cewa tay bata da future da ibaad kota auresa is going to be her karma nd misery kuma nala is only after her money.

tunda rukky ta saduda tay tone tone snn tay admiting cewa she was also obssessd with ibaad kuma yafara ne tun ranar da tafara ganinsa lkcin da suke ss1 da prof ya dinga matsa masa yana zuwa schll dinsun dauko zainab a makrnta idanun zainab arifah ya balain rufewa da mahaukacin kishi da zafin betrayal

she was begin zainab cewa wallah ita iya abunda yake damunta aranta kenan amma bata tsaneta ba kawai ibaad take so kuma shiyasa ta fasa kaskon sihirin nan.

gabaki daya ita kuma nala ta haukace da bori tahau kara wuta ta zuzuta maganan tace wallah karya rukky takey tana shifting blames ne dan tanaso ayafe mata, they kept accusing each oda agaban zainab

itakuma zainab baqar kishi da haushi ya rufe mata ido, ynxu cewa da rukky tay tana son ibaad yafi ci mata rai fiye da komi bata batun nala take yi ba. kan kace wani abu suka kama dambe duke duke suka taru ma rukkyn akai...

agarin zata fixgota a hannun nala tay wani irin loosing balance cikin kiftawar ido da bismillilah ta tureta tun daga saman bene rukky tasa wani irin ihu jin tafara rikitowa daga gidan sama zatay kasa caraf ta rike rigar zainab arifah  tana ihu tana cewa help me zainab pls help me..

wani irin kallo zainab ta mata azafafe tace 'help u? ai wallah  saidai ki mutu rukky, i trusted u but u stab me at my back, da abokai irinki gara in mutu ko inje mana ina kwana da macijin dana san sareni zaiyi wata rana, wawiya kawai butulu, inda asrinki be tonu ba danima kasheni zakiyi akansa kenan..ba ibaad kikeso ba? toh saikije lahira ki auresa..

idonta a rufe da fushi ta kara hankadeta tace 'he is mine..

da wani gudu nala ta miƙe daga kasa zata hana zainab karasa ture rukky kasa amma inaaaa kafin nala ta karaso harta fincike riigarta da karfin tsiya tare da kara hankadeta da hannu cikin kiftawa da bismilla sukaji saukar ta akasa gwaraf aikuwa sai gawa...

wani irin tsoraccen ihuuu nala tay tace "what did u do?..u pushed her, u killed her...wayyo Allah mun shiga uku

arikice zainab ta dago kai sai kuma jikinta ya fara tsananta rawa rawa tama rasa me zatace suka sauka kasa da gudu Allah ya so su bayan gidan ne taciki inda babu kowa.

suna zuwa kasa suka gan rukky laying on the ground cold dead dan kuwa kanta tafasa

rungumar juna sukayi sukasa ihu zainab taje arikice zata taɓata dan ta tabbarta nala ta janyeta da sauri cikin rikicewa da ihu tace dont touch a dead body are u insane????

zainab arifah tana kukan firgici duk ta gama rudewa tafara tambayarta me zasuyi dakyar suka nitsu, gashi yamma ya fara rufawa sosai jinin rukky yana malala akasar wajen sosai.

bata da yadda zatay she just called her dad tanata kuka kuma a mugun tsorace ta gaya masa they got into a fight with rukky kuma ta tureta amma ta fado ta mutu mata a agida.

yanacin abincine amma da wuri ya bari ya miƙe tsaye yace 'what??  nala ta amshi wayar ta kara masa bayani atake atake yace musu kar su sake suje kusa da gawan su matsa gefe su tsaya har saii ya turo mutane...hakan kuwa sukayi, bada jimawa ba wasu gardawan maza sukazo da plastic bag suka dauke gawan rukky aka clearing duk wani tiny evidence cikin daren suka discarding bodyn rukky, aka goge traces na waya, he had alot of ppl dat are doing a clean job for him that night dan kawai ya kare rayuwarsa dana yarsa cikin gaggawa


before morning rayuwar
ruqqy ya zama tarihi with no traces of her, nd her last knwn location was shifted to be dubai, call history, chats, komi aka cire na ranan da kisan ya faru yay kamr sunyi sati biyu basuy magana da su arifah ba


ranar ko bacci basuyi ba dan tsoro, gashi babanta ya zare mata ido yace maza maza ta dawo cikin hayyacinta ta koma yin rayuwarta normal kar tasa ayi suspecting inta snn yay assuring inta cewa inhar yana raye babu abunda zai sameta har abada

dake bata taba kisan kai ba Abun ya taɓa mata kwakwalrta sosai, nala was forced to stay with her, tun bata saba shaye shaye ba ya zamo ita dakanta yanxu take sayan kwaya su sha sosai suje clubs dan su mance da komi.

in oda to make thing less suspicious shima baizo US din ba, mamanta ma batazo ba, itama basu barta tazo nigeria ba..nan baban nata ya daga duk wata hidimar da zasuyi na bata kamfani akan har sai abun yafice mata aranta kafin su dawo da rayuwarsu normal.

shakuwa mai karfi ya shiga tsakaninta da nala within this days duk dama aranta tana tuna maganganun rukky time to time, daga suje england sai su zauna manhatan, yawan shaye shayen kwaya yasaka tuni suka fara mancewa da abubuwan da suka aikata.

within a month suka hada babban party awajen da rukkyn ta rasu time to time haka suke zuwa gidanta suna nemanta gashi dama rukky bata da mahaifi mum dinta ne kawai me bala'in kudin, for one good month ana nemanta until rukky was declared missing in dubai with no traces of her where abouts.


daga nan nigeria kuwa ibaad yana cikin watan sa na hudu dafara bautar kasa su ayaana suka yi jamb result din ta ya fito taci sosai so he gifted a sport car key tsakaninta dashi amma basu nuna ma kowa ba kawai hoton motar ya nuna mata da zimmn tana gama schll din gabaki daya sai tay deciding intanaso akawo mata nan gida saiya kawo mata, she was soo happy da wann babn kyautar, her first car was given to her by her love..shakuwa me yawa yana dada ninkewa acikin kolulwar zukatansu

bayan nan suka fara rubuta waec dinsu, Wann lkci ne kuma uncle moh ya sako kai sosai shima, ynxu baya ma fiye boyewa har hajya mairo tay kamar zata gano meyake nufi amma dai tay shiru ta zuba masa ido batace komi ba.

week din da zasu gama waec din ya zama wata guda da kusan sati biyu kenan da mutuwar rukky a hannun arifah. su hajiya mairo suna zaune aka aiko musu katin gayyata wajen hidimanta wanda za'ay ne agidansu ranar asabar mai kamawa.

kowa yanata mamaki dan prof bai taɓa gayyatar su gidansa ba sai gashi da zai naɗa yarsa akan kujera yau ya aiko musu gayyata har gida wann abu bakaramin dadi yay ma hajya mairo ba cos she secretly wishes yaranta su hada kansu yadena ware yan uwansa sabida abun duniya

Haka ta taro meeting tun daga kan bappa zaidu tace dole ne kowa saiyaje wann hidimar zainab da za'ayi ko dan a karfafa zumunci.


atake atake tasaka aka fara shirye shiryen abubuwan gudumawa da ire iren abincin da suma zasu kai ranar

week din ibaad yaje UK duba gidansa, ranar kuma ayaana suka gama waec tana fitowa kawai tazo taga uncle moh yazo har schll dinsu  tsabar kunya dataji duk wani abu daya kawo bata iya karba ba sabida kowa daukawa yay ko babanta ne ma

da girmansan nan duk wani shirmen red rose da bonquet da akewa yan mata haka shima yaje ya jajibo, safiya kuwa suna isowa gida tsabar kishi ko cire uniform batay ba taje ta gayama anty safeerah komi da yafaru.

tun daga wnn ranar anty safeerah ta fara mugun daure ma ayaanah fuska har takaiga inba a cikin mutane ba bata amsa gaisuwarta bare tay mata wani magana

da ita da safiya suka sako ayaanan agaba da silent anger turned into pure hatred..hutun sati biyu ne tsakanin Waec da neco gashi ibaad bai dawo nigeria ba bare taji sanyi tasan kuma dole zaijeshi wajen jamal ko farhan, kuma bata isa taje gidan ammi babba wajen sultana ba haryau dai Ammi babba can't even stand her. saidai suyi waya, ko in zataje gidan tare da hajy mairo.

ganin kowa ya daure mata fuska agidan yasa ta maida hankli wajen zuwa shagon hajy kullum sai ta bar musu gidan taje ta wuni acan tana kan koyan abubuwa masu amfani, but still hanklin anty safeera yana kanta, she is secretly spying on her, takan sa mutane awaje suna dubawa ko in ayaana taje shago mijinta yana zuwa wajenta hira dan haryau bata gama gane meyake nufi akan ayaanan ba.

ranar da safiya ta kawo mata gulman ma bakaramin habaici ta masa ba amma sai ya nuna cewa ai ayaana is exceptional shiyasa yake mata haka...

tun kuma aranar ta nuna masa she is no longer okay with relshp dinsa da ayaana tunda ayaanan ta mallake hanklin kanta yanzu, kuma gasu bappa zaidu, su ammi karama da uwa uba ibaad suna kulawa da ita. kuma ai su basa yin abunda shi yakeyi..sosai ya lura cewa da anty safeera ta fara ganosa but he just ignored her ya maida abun wasa sai bata kara cewa komi ba ta kyalesa tacigaba da saka ido ma ayaanan kuwa sosai.


Satin ayaana daya da fara zuwa shago zainab arifah da kawarta nala suka dawo nigeria aka fara shirye shirye, yanxu tana shan hard drugs, zaka sha mamaki yadda ta dawo big girl kamar ba ita ba
but deep deep inside her brain is soo damaged da guilt na abubuwa dayawa da suka faru.

yanxu haka bata da lafyar kwalkwalwa sosai she is living with a supressed mental depression wanda yake fara kkrin dawo mata full blown schizoprenia tunda tay kisan kai innn, amma fuska da hali normal mutum zaka ganta burbbling nd alwys hot like nothing has ever happend to her. ciwo brain inne kawai yake damunta aboye amma ynxu bata iya tuna komi data aikata


kusan kullum ayaana tana tare da ruthy a restaurant in hajiya but dabiun ruthy yanzu ya sauya bakamar da can ba, dan hiran da sukeyi ma duk ta dena tafara shiru shiru saidai suy aiki a rabu,..

sosai ayaana tazo ta fara gane cewa kmr ruthy tana cikin wani matsala da damuwa kuma kamr matsalane ta samu da abokanta da suke ankon jan kaya, saidai ko ta tambayeta bata gaya mata komi saidai tace mata stress ne yanxu bata da saurayi she barely have sex shiyasa batajin dadin rayuwa.

jin maganan ruthyn ya fara ma ayaana nauyi sai ta kama kanta tama dena tambayartan.

alhaj ameer dake kkrin kara aure dake ya saki first wive dinsa zai karo wata haka ya tsaya ma uncle moh a wuya akan lallai yay inviting ayaana suje dinner awani waje kawai yay proposing mata batun aure.

shikuma anan yagama lura da anty safeera yanxu ta hankaro gabaki daya baison ya kunna wata hayaniya yanxu duk dama niyyarsa kenan yaga ya gabatar da niyyarsa ma ayaana cikin satin nan

ana saura kwana daya hidimar zainab arifah ibaad yay dawowar cikin dare dake ranar friday ne anan agida wajen amminshi kawai ya sauƙa 8:30pm bayan ya gama gaiswa da kowa ayaana takai masa abincin data dafa masa har dakinsa suka ci tare snn suka sha soyayyarsu me sanyi da saka nitsuwa har wajajen 10;30pm snn ya sallameta taje daki ta kwanta suna chating akan hidimar gobe..

he asked her if he can take her out on gobe da yamma bayan hidimar zainab arifah sabida prince hassan zaizo da wife to be insa yasmin zasu halacci wani taron siyasa na babanta a kano nd he invited them tunda sune kawai close mutanensa daya sani a garin kano..babu tantama ayaana ta amsashi da eh at same time taga sakon uncle moh he is also requesting if they cud meet sumwher else on sunday evening sai tay ignoring bata amsa ba tay maza ta share saqon suka gama chat dinsu da ibaad tau addua tay bacci


washe gari gidan ya tashi a rububi, ahalin bappa zaidu da sassafe sukazo haka anty safeera tay ma sultana da safiya wata mayyar make up professional standard amma banda ayaana, yau bakaramin kyau su sultana sukayi ba.

hakan kuwa ko kadan bai dame ayaana ba dan tasan ibaad baiya ma son ta fiye fenta fusksrta sosai dan haka sama sama tay nata make up, dayay balain fito da glowing natural beutynta, koda ta fito kowa saida ya kalleta anfita kwalliya amma ko kadan ba fita kyaun fuska ba. dukansu tsadaddun laces suka saka su ammi ne kawai suka saka manya manyan atampopi masu bala'in tsada da kyau , ammi karama tasha mamaki yadda su anty safeera da ammi babban suketa wani nuki nukin boye kayan da suka siyo irinnata awajen mum ramlat collection dariya ma abun ya bata sosai

#idan kinason cigaba da samun posting kibi shafukata

*AREWABOOKS*
*@SURAYYAHMS*

*WATTAPAD @SURAYYAHMS*


*WASAP CHANNEL ND GROP: SAVE MY NUMBER *** TO BE ADDED*


#SURAYYAHMS
#COMEBACK SERIES
2024/2025