Part 27-28
بسم الله الرحمن الرحيم.
اللهم صلي وسلم على نبينا محمد.
*🖤AMNA DA SAFNA🖤*
Part 2️⃣7️⃣▶️2️⃣8️⃣
📱Writing✍🏼
Aisha G Umar
_*🌹𝑍𝑎ℎ𝑟𝑎-𝑡𝑢𝑙-𝑄𝑎𝑙𝑎𝑚🖋️*_
WASHE GARI.
Abu kamar wasa basu ji kiran Baba ba, Mamma ce tayi tinanin kiran wani daga cikin 'Ƴan-uwan Takori, sakamakon wayar da sukayi yasa su shiga cikin tashin hankali, domin kuwa an tabbatar musu da cewa Baba bai je ba, ko alamar sa ma basu gani ba.
Amna da kamar ta fara fahimtar wani abu ta je ɗakin Ummee, ta jira Ummee ta idar da Sallan Azahar, sannan taƙarisa dab da ita ta ce, "Ummee inason zuwa gidan Uncle Tukur". "Me za kije yi"? Ummee tayi mata tambayar daidai shigowar Mubarak.
Zama yayi a gefe shima, lokacin Amna ta ce, "Haka kawai Ummee please ki bar ni inje, ba daɗewa zan yi ba" ta ƙarashe faɗi haɗi da marai-raice fiska, dan so take taje sabida wani dalilin ta, "muje tare" cewar Mubarak, "a'ah ba inda za ka, kaida kake fama da jikin ka" Amna ta faɗa mai haka, Ya ƙara cewa, "naji sauƙi ai yanzu".
Maida kallon ta tayi gurin Ummee tana ƙara roƙon ta, "kije amma karki daɗe kamar yadda ki ka ce" "toh Ummee na gode sai na dawo" ta faɗi tana miƙewa tafita a falon, Mubarak yana mata maganar tare za su, amma ko juyowa bata yiba, saboda ba ta son rakiyar ta sa, 'yar ƙaramar shiri tayi, sannan ta sa glass ɗin ta, sai wayar ta a hannun ta, shiga Napep ɗinda ta tara tayi.
A ƙofar gidan sa aka sauke ta, da sallama ta shiga, gaishe da matan sa guda biyu tayi, suka sanar da ita bai dawo ba yana office, babu ɓata lokaci ta fita daga gidan ta kuma taran wani napep ɗin zuwa gurin aikin Tukur.
Wayar ta ce tayi ƙara, numbern abokin ta Wali ne akai, tana ɗagawa tace "Wali ya kake, sorry ina ɗan wani uzuri ne, inna gama i will call you back". "No Amna listen, wani abun tashin hankali zan sanar dake, nasan kinfi Mubarak dauriya shiya sa nake..." sai kuma yadakata, sabida abinda yake son sanar da ita shi kansa, ya shiga cikin tashin hankali da ganin sa, amma yana da tabbacin bata gani ba sabida Amna ba gwanar shiga internet bace.
"Wali faɗamin mana, meyafaru dan daga jin ƙarar kiran da ka mini na tsinci kai na cikin wani yanayi" cewar Amna haɗi da buɗe kunnuwan ta dan jiye mata abinda Wali keson faɗa, "Kin kalli labaran GT kuwa? kina ina ne?" Yayi mata tambayar, "a'ah, just tell me what you want to say"? "Bazan iya faɗa ba, saboda, amma dai ki shiga labaran GT dake wakana yanzu, sabida suna ta nanata lamarin, Gidan Radion nan na Kaduna".
Katse wayar tayi ba tare da ta yi masa wani magana ba, ta buɗe Data, dan ganin meke faruwa, tashin hankali ba'a sa maka rana, hoton Baba taci karo da shi an maƙala a kan labarun GT mai kawo rahoton yana cewa.
"Labarun GT kuke saurara, Assalamu alaikum Jama'a barkan ku da wannan lokaci, labarin mu na yau shine, yau an tsinci gawan wani bawan Allah anan garin Kaduna, ya mutu ne bayan yayi shaye-shayen sa yayi maƙil, a gefen titi aka tadda shi, a binciken hukumar, gawan ba na yau bane, a ƙalla zai yi kwana biyu, hakan yasa aka bada damar yi masa jana'iza ba tare da nemo iyalan sa ba".
Saurin fita daga wurin tayi ba tare da ta ƙarashe jin maganar ba, ta rintse Idanuwan ta da ƙarfin gaske, gaba ɗaya jikin ta ya ɗau kyarma, buɗe idanun tayi har sun fara canza kala, ambaton sunan Allah ta farayi cikin tashin hankali, ganin abinda ke faruwa yasa mai napep ɗin cewa, "Hajiya lafiya dai?" Baki na rawa tai masa magana da ya maida ta Gida, tare da sanar dashi sunan unguwar.
Tinanin zasu iya sake labarin nan a tashan labaran da Ummee take gani ako da yaushe tayi, hannun ta na rawa ta duba numbern Mubarak, yana ɗagawa cikin ɗimuwa ta ce, "Mubarak ina Ummee?" "Mamma na ɗakin ta, Ummee kuma i think taje kallon labaran duniyar da take gani da rana" ƙara shiga tashin hankali tayi ta ƙara cewa "yi maza kaje Kasan yadda zaka hana Ummee kallon labaran nan".
"Sabida me? lafiya kike kuwa? Ya naji voice ɗin ki haka?" "Stop asking, just do what I say" Cike da rashin fahimta yace, "ok" tare da nufan falon Ummee, sai dai mai afkuwa ya afku, domin kuwa daidai lokacin da aka kawo fiskar Baba ya shigo, yayin da mai kawo rahoto yake zubo maganganu.
Zaro ido waje Mubarak yayi yana faɗin, "a'ah, no, noooo" Ummee kuwa numfashin ta ne ke niyyar barin jikin ta, saboda tsaban shock da tayi da jin abinda aka faɗi a kan mai gidan ta, Mamma ce ta shigo tana tambayar "lafiya"? Sai dai itama idon ta ya gane mata, kunnen ta ma ya jiye mata.
A take shock ɗin Mamma ya fi, domin kuwa ita sakin jikin ta tayi, tayi ƙasa, tashin hankalin su ne ya ƙaru, ganin abinda ya samu Mamma, lokacin mai napep ya sauke Amna a ƙofar gida, sai dai fa yau duk wanda yayi tozali da idon Amna sai ya tsorata, sabida yadda fiskar ta yake ɗauke da tashin hankali muraran, duk da bata cire glass ɗin ba.
Tun daga Ƙofar gida take jin ƙarar Ummee da Mubarak, yadda ta iske Mamma sai ya ƙara ɗora ta cikin wani tashin hankalin, ba tare da ta ƙarasa ciki ba, "Muje Asibiti, mu kai ta kada wani abun ya same ta" Cewar Ummee cike da fargaba sai kuka take, Mubarak kuwa duk da cewa namiji ne shi, amma hawaye ne ke ta zarya a kumatun sa.
Da sauri ta ƙarasa inda Mamma take tare da cire glass ɗin idon ta, tayi wulli da shi "Ummee ku dai na kuka ba sai an kai ta hospital ba zata tashi" ta faɗi bayan ta taɓa kai da wuyan Mamma, ita kaɗai ta ɗaga Mamma ta mayar da ita ɗaki zuwa kan gado, ta lulluɓe ta da bargo ta koma gurin su Mubarak, sai dai har lokacin ko ɗigon hawaye bai fito daga cikin manyan Idon ta ba, sai launin ja da ya kewaye farin, yayin da zuciyar ta kuma ke cike da tashin hankali, amma gwara ta daure taji da na familyn ta.
A yadda ta barsu ta dawo ta same su, "Mubarak ɗin Baba ka daina kuka ka ji, kaida yakamata ka rarrashi Ummee amma kake kuka?" Ta faɗi tana riƙe masa hannu alamar rarrashi, komawa gurin Ummee tayi, tana bin ta da kallon tausayawa, tace "Ummee nah ki daina kuka..." katseta Ummee tayi da faɗin.
"Amna cewa fa su kayi Baban ku ya mutu ko baki ji bane? kuma wai sanadin....!" sai kuma ta fashe da kuka, ana haka sai ga shigowar wasu daga cikin maƙoftar su, jin kamar da matsala a gidan, nan suka fara taimakawa Amna gurin rarrashin su Ummee.
Lallai gaskiya Amna jaruma ce, irin wannan jarumta haka, yadda ta daure ta ɓoye duk tashin hankalin dake zuciyar ta--
Komawa ɗakin Mamma Amna tayi, lokacin kuwa Mamma ta fara motsi, wucewa kitchen tayi da sauri ta ɗibo ruwa a glass cup ta dawo, a hankali ta ɗago ta haɗi da gyara mata zama ta bata ruwan ta sha, hawaye masu zafi Mamma ta fara fitar wa, tana faɗin, "shiyasa na hana shi zuwa amma yaƙi, me yasa zai min ƙaryan zuwa ziyara, ashe abinda zai je yi kenan".
"Dan Allah Mamma nah kar kice haka, kece mutum ta farko da zaki ba da labarin Baba, kinsan ko à mafarki bazai aikata hakan ba" kuka Mamma ta sa tana ƙara cewa "nasan haka, amma me dalilin sa nayin ƙarya?" "abinda yakamata in sani kenan" cewar Amna a cikin zuciyarta.
Su Wali, Zarah da Nabila ne suka zo suma, dan su rarrashi abokan na su, kusan magriba suka koma, Ummee da Mamma ko magana babu sai ido kawai musamman Mamma, suna zaune gaba ɗayan su a ɗakin Mamma, Amna ce ta tashi kamar antsikare ta, ta wuce uwaɗɗakan Ummee, tana shiga ta durƙushe a ƙasa, sai a lokacin take ji kamar yanzu ne abin ya faru.
Kukan da ta jima bata yi ba ne ta fara sakin sa mai ratsa zuciyar mai sauraro, kuka take sosai kamar ran ta zai fita, komawa gefe tayi, ta haɗe ƙafafuwan ta da hannu guri guda, tana ci gaba da kuka, idon ta ya canza kala, gashin ta da ya warware daga ƙullin da tayi masa tun da safe, sai ya barbazu a kan fiskar ta.
"Me nene yake faruwa ne? Baba menene yasa ka ƙi sanar damu dalilin...?" ba tare da ta ƙarashe maganar ba ta miƙe tana tinanin wani abu, sai kuma ta ciro wayar ta dake cikin aljihun wandon ta, da sauri-sauri take ƙoƙarin ƙara kamo labarin, zama tayi tana ƙara sauraron abinda suke cewa a ciki daidai wurin da, "a binciken hukumar, gawan bana yau bane, a ƙalla zai yi kwana biyu".
Tsaidawa tayi, tana faɗin, "taya zai zama kwana biyu?" Nan kuma ta ƙara tina lokacin tafiyar ta sa, "Allah ya baka nasara akan Ƙungiyar POSPA Aboki na, dan Allah duk abinda ake ciki ka rinƙa sanar da ni" "tabbas haka naji Uncle Tukur ya ce masa wancan ranar" . Cewar Amna a fili sannan ta ƙara cewa "ya kamata inje in samu Uncle yanzu ya faɗamin abinda Baba na yaje yi Kaduna" ta ƙarashe faɗi tana share hawayen ta, ta fice daga ɗakin.
Ba tare da ta sanar da su Mamma fitar na ta ba, ta fice daga gidan ko glass bata sa ba, kai tsaye gidan Uncle Tukur ta sake nufa, tana shiga suka fara mata kallon tausayawa, sabida sun san abin da ya faru, sai dai sunyi mamakin ganin ta ba tare da tabarau ba, koda yake tashin hankalin da take ciki ai zata iya mantawa da komi.
Wannan karon bata gaishe su ba, kawai tambayar su Uncle Tukur tayi, uwar gidan sa ce ta sanar da shi zuwan Amna, yayin da ta tadda shi shima yayi tagumi sabida tashin hankalin mutuwar abokin sa, dama yanzu yake son zuwa gidan su Amnan.
"Kice ta zo" kawai ya furta ba tare da ya kalle ta ba, fita tayi ta sanar wa Amna, ai kan ta ƙara sa, Amna ta yi hanyar ɗakin na sa, yanayin yadda ta shigo ne yasa shi saurin miƙewa, kallon ta yake yi cike da tausayi, da kuma ganin yanayin fiskar ta da bai taɓa gani ba.
"Amna kiyi...!" katse sa tayi da faɗin, "Uncle please tell me, ka faɗamin gaskiyar abin da na gani yau, kace min ƙarya ce haɗawa kawai a kayi, ai kasan Baba bazai aikata hakan ba ko?" Tana ƙarashe faɗi ta durƙusa tana zubar da hawaye masu zafi.
--------------------------------------------
Chakwakiya, ina tausayawa su Amna na rashin jigo da su kayi🥺.
To amma anya babu wani abu a ƙasa kuwa? Tabbas a kwai abinda ke faruwa wanda sai nan gaba zaku fahimta.
_*🌹𝑍𝑎ℎ𝑟𝑎-𝑡𝑢𝑙-𝑄𝑎𝑙𝑎𝑚🖋️*_