ABUNDA KE 'BOYE...

45

by @surayyahms

ABUNDA KE ƁOYE💫
arewabooks@surayyahm.


⏯️4️⃣5️⃣

Sai Wajajen karfe 8am saura kafin nan ahalin bappa zaidu suka samo isowa, wani irin shiru gidan ya dauka kamar babu mutane aciki in banda safiya da ayaanah da sultana banga wani mahalukin da baya falon hajiya mairo yau ba,
sanadiyar rashin isowar Bappa zaidu agaggauce, yasaka hjya ta umarce ammi karama akan tay musu breakfast while they wait, within few mins ammi karama ta gama aka kawo  dadin qamshin wainar kwai, da su pancakes, kunun madara, da irish pritatas duk yabi yacika hancin prof yanata basarwa da kyar hajiya mairo talallabe sa yadauki abincin ya taɓa kadan dan da wani irin gingimammen rashin mutunci da girman kai tareda mnyance ya taho yana kallon kowa dan iska awajen.

banda ma Hajiya data masa tarban nuna masa tausayi da baiyi tsammani ba da hala ko xaman jiran zaidu bazai iyayi ba.

sun fara ci kenan bada jimawa ba saiganan sallamarsu bappa zaidu idon kowa na bakin kofa ana tsammanin ganin ibaad atare da su sai shiru har suka karasa shigowa aka fara gaishe gaishe nan tay general nasiha game da abunda ya faru da furuci masu cike da nuna son kai da kuma bangaranci tanakan bayyana musu prof a matsayin wanda aka zalunta aka tashi kashe masa yarsa kwalli daya

babu wanda ya tanka har tagama nasiharta snn takore duka matayen gidan aka barta daga ita sai yaranta su ukun a kewaye da ita

wajen atake ya dauka da shiru bada jimawa hajiya mairo tafara magana cikin mita

"kai kuma zaidu ya naga bakazo da uban gayyan rayyanu ba kodan tsabar raini yasa yaga bazai iya zuwa amsa kirana ba?

ba yabo ba fallasa bappa zaidu yace ibaad ai baida raini hajya, zaizo..nine na aikesa!

cikin karkada kai tace kullum acikin shan bakin sa kake toh wallah yau kwata kwata bana son raina ya baci da ku dan wann abu daya faru da yar jikata zainabu sam baiyi min dadin ji ba ace kuna yan uwan jini aima bai kamata azo ana samun hali irinna mugaye marasa tausayi acikinku ba.

kai kuma zayyanu nasan an riga an cuceka amma hakuri zakayi kasan ance zaka haifi da ne baka haifi halinsa ba, aikai kasan waye babban yayan naku marigayi mustapa, mutunin kirki ne sam baida hayaniya, yo aiko uwar rayyanun ma ba haka take ba ni sam bansan a ina yaje ya samu nashi halin ba.

Da wani irin izza prof yace "A ina kuwa zai samu bayan irin tarbiyan da ya taso dashi ajikinsa kenan mama, ni ba nazo nan bane dan in tsaya jin wani hakuri. ke kanki kinsan anjima anaso aga bayana da ba'a gani ba shine aka turo min wani shaidanin yaro yake son ya ruguza rayuwar yata toh wallah bazaiyu ba.

cikin katsesu bappa zaidu yace hajiya ban fahimceku ba wai maganan waye akeyi ne haka?

baki bude ta kallesa tace waye kuma inba rayyanu ba, yanxu kai zaidu abunda yayi jiya da rayuwar yarinyar nan yay mata adalci kenan? aikamata yay ace ka tasosa agaba yaxo ya tsuguna anan agabanmu ya bawa zayyanu hakuri akan tashi kashesa masa yarsa kwalli daya daya tashi yi, dan tsabar daurin gindi ai aikansa kayi kenan shi bazai nemi afuwar kawunsa ba ko??

bappa zaidu yace "aa hajya, yarsa ce dai ta tashi kashe kanta dakanta, ina kuma ruwan ibaad aciki?..snn Abunda ya faru jiya fa ya shafe kowa, bangane kina neman ki dora laifin a bangare daya ba in har abunda kika tara mu akai kenan banga amfanin zuwa na nan ba, dan inhar baza'a yi magana cikin gaskiya ba babu amfanin taro mu anan

da wani irin izza prof yace "wani gaskiya?? yanxu kai zaidu har zaka iya budan baki kay wani magana after all everything dat happened was ur fault, yes ..yaron nan a hannunka ya taso a lalace he is a liar and a manipulator bai ayyana komi ma rayuwarsa ba, kuma na jima da gane take takenka, kaine kake zugashi yana aikata min duk wani abunda yaga dama agidana toh wallah mama kigaya masa zan dauki mummunan mataki akansu dukansu.

kafin ya karasa rufe baki bappa zaidu yace ahhh ahh ahh mataki kam ai akan yarka zaka fara daukawa kafin kayi zciyat juyowa kan ɗan wani, kana magana ne kamar kai kaɗai abun ya shafa, snn Ka manta cewa muma muna da mutunci da xuciyar da kuma son yayan. Ba zaka zo ka yiwa kowa kallon me laifi ba saboda matsalarka da yarka daka kasa magance shi.


da bacin rai hajiya tace kaiii zaidu wallah banason shashanci wai meye haka kuke fada wa junanku kai da zayyanu???ashe bazaku tsaya ku fahimce junan a sulhunta maganan nan kamr na masu hankli ba


bappa yace In dai za a raba tsakanin tarbiya na gaskiya, to mu a nan muna da hujja, snn Kada kowa ya zo ya juyar da laifi ya ɗora shi kan bangare daya..

Da bacin rai prof yace mama ban yarda a yanke wa Zainab Arifah wani hukunci saboda kuskuren wani ba sabida ita akekan cutarwa, dagangan akayi ma yata haka dan anriga an tsaneni, kuma inda jiya ta mutu da kowa sai ya dandana kuɗansa agidan nan dan wallah bazan yafe muku ba

cikin jan tsaki bappa zaidu yace "inda ta mutu da babu abunda ka isa kayi saidai ace yarka ta kashe kanta abanza kuma kasan wuta zataje aiko..

da wani irin hargagi prof ya juyo zai amsa maganan

cikin katsesu uncle moh yace yaa zaidu, dan Allah kuyi hakuri wannan maganan fa mai sauki ce, wanda yay kuskurei a fito fili kawai abashi duka rashin gaskiyarsa, ita zainab macece mai rauni koda dan halacci ba ai akwai yan uwanta ka. we all know yaa zayyan dakyar ya samu haihuwar nan kuma yarsa kenan kwalli daya bazafa mu cigaba da rufa rufa muna kallo ana wasa da rayuwarta haba yaa zaidu ayi magana cikin adalci mana.

da zafin nama hajiya tace yawwa muhammadu gaya masa gaskiya dai yaji dan naga alama babu Allah acikin zuciyar zaidu, inba haka ba kiri kiri kana kallo zaa cuce rayuwar dan uwanka zayyanu wanda kuka zauna acikin tare amma ka rufe idonka kace sam ba haka ba

bappa zaidu yace hajiya inada tambaya, shin yaron nan menene yayi muku guda daya? inhar zaku iya gayamin laifinsa da kuskurensa direct wallh zan amsa

kuka hajiya ta fashe dashi tace aww ynxu kai zaidu duk anan bakaga ga laifin rayyanun ba shifa ya jawo zainab ta tashi zata kashe kanta haba zaidu.

bappa zaidu ya kara hade rai yace "okay shi kenan yaje har gidansun yace mata ta kashe kanta ko?toh inba haka ba ya zaku taru kuna blaming dinsa shikadai akan abinda yarinya taga damar aikatawa kanta ai ita tafimu sanin ita daya ubanta ya haifa da batay la'akari da hakan ba duk bai muku ciwo ba???saishi ne da baida gata agidan nan ake so ace komi lefinsa ne bayan yariga ya gaya mata alaqa bazai yi tsakaninsu ba, mama shine me duka laifin da har za'a turo hukuma su kamashi a kulleshi??? nifa bawai inace miki ibaad baiya kuskure ba, ko ranar da abun ya faru ainay masa fada sosai sabida zainab ai ya mace ce tana da rauni, damuwata yadda kuke kkrin kuce lallai shine yasakata ta aikata wann abun wakanta gaskiya babu gaskiya ko adalci aciki, he is also a victim too, ai ɗa baifi ɗa ba..inkina jin zafi akan rayuwar zainab arifah shima ibaad din ai jikanki ne meyasa bazakiy la'akari da halin da hakan zai jefashi aciki ba wai shin ana soyayya dole ne..ynxu saiki gaya min menene wanda ya kamata yay mata tun dacan wanda baiyi b..soyayya ne yace bayayi
..kuma ya gaya mata toh menene..

da wani irin bacin rai prof ya miƙe har jikinsa na bari zai magana hajiya mairo ta daga musu hannu da muryan kuka da fushi tace "kai Ya isheku haka duk ku nitsu kafin naci muku mutunci karnasake jin bakin kowa anan dan naga alama maganan bazai kare ba, yanxu menene mafita guda daya? zayyanu kaji abunda xaidu ya fada kai meye ba'asinka...

komawa yay wajen zamansa ya zauna yana wani irin hura hanci da wani irin girman kai yafara gaya mata abunda likitansu ya fada akan lafyar kwalwlawar zainab wanda tun yana tsaka da bayanin hajiya ta rafka salati ta fashe da wani irin sabon kuka.

wayyoo Allah ni mairo, zainab yanxu haka rayuwarki ya dawo sai kace me taɓon hankli? innalillh wa inna ilaihi rajiun au dama abun har yakai haka ne zayyanu, Allah ya isa miki zainabu! toh wallah ko anaso ko ba aso dole ne mu dauki mataki, muhammadu kaine shaidata anan kace ma yayunka maza su sasanta kansu a tsaya a kan magana daya rayyanu ya sauke girman kai ayi auren nan kodan yarinyr nan ta samu lafiya bayan haka banason na karajin wani hayaniya..

bappa zaidu yay shiru ya zuba musu ido yana dai jiransu sugama

rimi rimi prof ya dinga kawo kananan magana yana hura hanci da izza yana cewa shima sharawar daya yanke da matarsa kenan duk dama yasan yafi karfin ya bada yarsa ahaka saidan samun lafyarta sabida yariga yasan cutarsa kawai xa'a yi, ana baqin ciki da daukakar da Allah ya masa anyi asiri an juya ma yarsa kwakwala da ciwon so dan kawai aga bayansa, kuma shi dukiyarsa ba'a isa aci abanza ba, inma ana tunanin anyi kulle kulle ne akan yarsa dan aga karshensa toh shiyasan yadda zaiy da mutum

yafi minti ashirin yana ma hajiya mairo magana da izza da zafin rai, yanamai dada gaya mata cewa akan dukiyar sa aka kulla komi, they cant stand the fact that shima Allah ya bashi yarinya me ilimi da tarbiya, hassada da kiyayyar da ake masa agidan ne yasaka ba acigaba, kuma wallah akan maganan zai saka ido, koda kuwa ya bada yarsa aure su sani ba a son ransa bane dan shi yasan cutarsa kawai za'ayi

maganganu dayawa dayake fadan sosai yah ma bappa zaidu zafi dan yaga alamar borin hauka kawai yakey, technically, shine yazo musu yana neman alfarman a aure yarsa amma sai yazo yana wani burga yana zage zage yana habaice habaice yana zargin kowa akan dukiya yana nuna musu kamar shine kawai zai rufa musu asiri yay musu alfarma...

hajiya mairo sai kuka take tana karkada kai batace komi ba gani take kamar eh dagaske ne anaso acuce zayyanu ne kawai akan yarsa zainab

ransa a bace ya cigaba da cewa "Dole ne asan yadda za'ayi hajiya, inaso yata ta dawo hayyacinta, snn duk wani maison ganin bayana shi zai fara faduwa ni xanyi ma yata duk wani gata har karshen rayuwarta dan haka aja kunnen yaro dan wallah next time wani abu makamancin haka ya sake faruwa hajiya kece kika haifi ni amma koke wallah baki isa ki hanani daukar tsatsaurar mataki akan yaron nan ba dan bazai kashe min yata a banza ba haukar banza haukar wofi.

cikin kukan tace kai zayyanu ya isheka haka, maganan nan ya kare, ni wallah ma tausayin yarinyar nakeji yanxu duk wata masifa da kukeji dashi ku aje kuhada kai kawai ayi auren nan, zaidu kaine uban yaro a hannunka yataso kuma yanxu kaine me wuƙa da nama ga zayyanu ya kawo batun yuyuwar auren zainab da rayyanu banji kace komi ba...dan Allah ayi ayi asaka musu rana dan yarinyar nan karta zauce ta haukace tafara shiga bololi tana tsince tsince

dago kai bappa zaidu yay cikin haɗiye bacin ran dake cinsa aransa yace "hajiya na gode da kika tabbatar ma kowa da hakan, haihuwar ibaad ne kawai banyi ba amma nina raineshi tun bai mallake hankalin kansa ba, tnk god da bakinki kince nine me wuƙa da nama..hajiya kiyi hakuri magana ta nasan bazai miki dadi ba amma hukuncin dana yanke shine ibaad bazai aure zainab arifah ba. tunda ubanta yace ita mai ilimi da tarbiyace suje ta sako ilimi da tarbiyan acikin rayuwata i assure u with time xata samu sauki, snn kuma shi uban nata dayake cewa shime dukiya ne kenan yana da halin da zai kai yarsa har bangon duniya dan ta samu lafiya kenan suna da wata hanyar mafita ba lallai sai an kulla aure ba..ni bana son auren da za'a dora ma yaro na dole akansa, snn azo ana zarginsa da kwadayin dukiyan wani ko azo ace hassada ne yasa muka badashi..to avoid all this gara ma kar afara..dama ynxu yagama cemiki baida niyyar hada jininsa damu toh banga amfanin basu auren ibaad ba tunda awajensa ibaad baida amfani, baida daraja, toh meye kuma na neman taimakon aure awajensa... ai a kyalesa kawai ya zauna da halinsa ita kuma zainab Allah ya bata lafiya tareda mijin aure nagari.

miƙewa tsaye hajiya tay in shock tace kan uban can zaidu wai abuge kake ne? waime kake cewa ne ana neman sulhu mai dorewa kai kana warwarewa ba duka rifin asirin mu bane in ayi auren nasu?

yana daga zaune yace aa hajy, wallah auren nan ba rufin asirin ibaad ne dan yafi karfin wani dan adam ya rufa masa asiri..danki ne dai yake ganin kamar zai rufa mana asiri zai mana alfarma hamshakiyar yarsa zata aure ibaad ta rufa masa asiri to wallah bazaiyu ba bama bukatar rufin asirinsu sukai kasuwa.

idonta arufe ta hargitso kansa zata shalla masa mari, uncle moh yau sauri ya riketa hajiya tafara ihu zaidu zaidu ka janye wannan maganan nan bana wasa dakai zaidu kay gaggawar janye maganan nan kafin inci maka mutunci

miƙewa tsaye bappa zaidu yay yana kallonta da taurin kai yace "Babu wanda ya isa yasaka ayi auren nan, inde wai zayyanu shine zai rufa ma ibaad asiri toh abari ibaad har ya mutu asirinsa bai rufu a duniya ba..what nonsense!!
yana gama fadin hakan yawuce ransa a bace yafita daga gidan.

gabaki daya gidan ya karade da ihunta "zaidu,..zaidu mani kake gaya ma wann magana kai zaidu ka dawo nan nace maka zaiduuuuu...

uncle moh na riirrike ta fashe da kukan mai tafe da bori prof daya sha mamakin maganan bappa zaidu ya mike da fushi muryansa harna rawa yace "hajiya ba kinga irin abunda nake gaya mikin ba..babban burin zaidu shine yaga na rasa ƴata, hassada da baqin ciki da kyashinsa yasa har ya mutu baxai taɓa zamowa kamr ni ba. kinga irin rainon da kika masa ko? dama baba saida ya fada baki iya raino ba, aida baba yana raye da ba'a isa amin wann abun ba dama kuma kece kike daure ma kowa gindi ni kin wareni sabida dama can kin tsaneni dan kawai na zabi in kare dukiyata daga wanda basa kaunata

tana kukan tace kar ka sake kagayamin bakar magana xayyanu, ubankan bashi ya lalata ka ba? kaima da kashi a tsuliyarka.. aure kuma dukanku baku isa ku hana yuwarsa ba innhar nace za'ayi ni na haifeku ba ku kuka haifeni ba.

zai magana da tsawa ta daka masa tace maza kasamu guri ka zauna ka gayamin me kake ciki shikuma zaidu zan gamu dashi bai isa ya raina ni haka ba wallah kryansa.

dakyar kura ya lafa ya zauna yana ciccin magani yafara gaya mata dokokinsa da zai shimfida, na farko ya jadadda mata cewa auren nan bada son ransa bane alfarma zaiyi, snn babu wani hidimar family da za'ayi, taron daurin aure kawai za'ayi snn zai gayyato manyan mutanen sa a bainar jama'a a masallaci, snn shi xai dauki nauyin komi har gidan da zasu zauna aciki sabida yarsa ta zama comfortable, zatayi aiki, xatay karatu snn zai hada su da likita da zain yawan zuwa duba lfyarta kwakwalta akai akai. snn duk wani kudin kashewa da sutura da komi shi zai nayi wa yarsa baya son komi awajensu face a tabbata yarsa ta kasance cikin koshin lafya kuma tana raye,..yace ma hajiya mairo ta dauke wann maganan a matsayin kwaji, inshi danta ne dagske zai gani dan ta hanyar wann auren ne kawai zai tabbatar da cewa ba son kashe masa yarsa sukeso suyi ba, snn hassada da tsana da bambamci ake nuna masa ba gaskiya bane.

duk taji abunda ya fadan amma bata yanke wani hukuci ba tace masa yaje zatay tunani daga ta gama kawai saka rana za'ayi ya gayyato mutanensa ranar daurin aure a daura.

su ukunsu suka dinƙe maganar kafin nan prof  ya fita ya dawo gida..

yanayin tashin hankali da rudanin ganin kalar zafin kai da zaidu ya nuna mata datake ciki yasaka uncle moh bai bijiro da nashi batun auren ba

can after like 2hrs bayan komi ya lafa ta kira ammi karama ta sakota agaba tace lallai lallai ta kira mata zaidu awaya yazo tana son magana dashi, tunda ita inta kirashi baya daukawa. duk sanda ammi ta kirashi zai dauka sai tagaya mai sakon yace toh zaixo amma haka suka sha jiransa baizo ba kuma still ya hana ibaad karasowa.

har saida akaci kusan kwana uku bappa zaidu yaki amsa wayar hjiya kuma yaqi yazo gidan gashi ya hana ibaad motsawa, ko maheer da yaxo shima bai barsa yaxo ba kwana biyu shikam ma yay ya koma. akwana na ukun ne abun ya isheta, tana tashuwa daga shago ta naɗe garinta da yamma taxo gidansa ko amsa gaisuwar ammi babba batay ba ta inada take shiga bata nan take fita ba harsaida bappa zaidu ya dawo daga aiki yazo ya sameta a falo

Duk masifar duniya ta masa baice mata uffan ba, dan koda yay kkrin nuna mata rainin wayon dayake cikin proposal din prof kai tsaye cemasa tay yanawa dan uwansa zayyanu mugunta da hassada. yana so ya jawo lamarin da zai saka zayyanu ya rasa haihuwa a duniya, she called him selfish nd heartless. ko ajikinsa bayan ishai ya saka aka kira masa ibaad ya shigo falon yaxo ya samesu suna xaune

fushi takey ko amsa gaisuwar ibaad din batayi ba shikuma dayafita danyen kai sai ya shareta bai kara ce mata uffan a falon ba

agabanta bappa zaidu ya maimaita duka ababen da prof yagaya nabatun cewa bada son ransa ma zai hada jini dasu ba, saidan sabida zargin zasu kashe masa yarsa ne akan dukiya, snn auren nan ma fa alfarma zai bayar dan yarsa ta samu lafiya amma badan yaso ba.

witout any bias ya tambaye ibaad ko ya amince da wannan batun aure snn yasani inhar ya amince shi bazai hanasa ba, dama shi auren dolene baya son yay masa.

tun kafin ibaad ya amsa tafara tsigeshi tana cewa bai isa yaki auren zainab ba tunda shi ya lalata mata rayuwa ya jawo mata ciwon hauka dolene ya aureta su rufawa juna asiri.

ibaad baiko kalleta ba yace ma bappa zaidu shi bai amince ba kawai Abata hakuri Allah ya bata miji nagari

bappa zaidu yace" hjy toh kinji da bakinki yace bazai aureta ba saiki isar musu ds sako.

hajya tay wani irin kukan kura zata cakumo ibaad din yay saurin miƙewa tsaye yanamai kare mata wani irin dakakken kallo wanda batasan sanda ta rusa ihu ba...ni kake min irin wann tsinannren kallon? au dukana zakayi?dukana zakayi rayyanu..tafara tutture shi, toh dakeni. nace ka dakeni..

..darajar bappa zaidu yasa ibaad yay shiru baice mata uffan ba ya tsaya yana kallonta tana hargagi.

she is doing all this to make them know she is very serious and hurt, musmm ma shi rayyanun dataga kmr bai dauki abun da muhimnci bama .

tashuwa bappa zaidun yay ya rikota tana masifa tana ihu tana cewa rayyanu wallah yadda ka lalata ma yarinyar nan rayuwarta ta haukace dolenka ne sai ka aureta
...inkun ga dama kaida zaidu kuyitayi amma maganan aure kam yana nan daram..

tanakaiwa nan ta bankade bappa zaidun ta fita agidan  tana matse ido da bakin hijabinta tana zage zage..

haka lamarin ya kasance kullum cikin tashin hankali, hajiya tana gida kullum tana bori tana rantsuwar sai anyi auren nan, amma bappa zaidu yayi burus yace ai tunda ibaad yace baiyaso baiga uban daya isa yasa a daura masa aure da zainab ba.

week din su ayaana suka gama practicals na neco zasu fara wrting amma gaba daya hanklinta baya jikinta sabida inba a awaya ba bata samun jin muryan ibaad shima kuma ba kullum sabida bappa zaidu har wkend in ma ya datse yahana ibaad lekowa family house sabida baison suyi wani hayaniyar da zata yi amfani da ammi karama ta tursashi

duk wani hanyar wayon hajiya mairo akan auren bappa zaidu ya toshe wanda yasaka duk su uncle moh suka farajin mugun haushinsa, gashi anty safeera tana yawan fita kusan koyaushe taje gidan prof zata dawo musu da labari marar dadi game da jikin zainab arifah.

satin gabaki daya zainab ta lalace dake pretending take she had takes more hard drugs dan tay acting din da kyau wanda kwayar ya fara ramar da ita, sai taki cin abinci tayi ta amai tana birgima da fake ciwon kai da suman karya.

prof zayyanu yajira yaga kiran hajiya batun saka ranar aure amma sai shiru, gashi bai gaya ma zainab din yaje har yay maganan aurenta ba, so yake har sai abun ya kankama snn ya gaya mata dan itama yana da tsauraran dokokin dayake so yasaka mata wanda dolene ta bishi inhar auren ta zaba.

kwana sha biyu da faruwar komi lkcin su ayaana sunfara writing exams dinsu anata shirye shiryen final graduation duk hanklinta bai jikinta sosai ibaad kuma yana can yayi nisa a rubibin kammala nysc tareda tests da su exams dat will get him qualified for his intnl admission da zai yi major course dinsa a kasar waje.


kamar da wasa Hajiya mairo tay ta jiran tsammanin ko zaidu zai shiga hanklinsa ya sauko ya kyale ayi maganan auren nan amma sai shiru..

bata taɓa sanin cewa zaidu yana da wann kalar taurin kan ba ko kadan.

cikin kwanakin nan gabaki daya yabi ya sauya mata, ya canza daga mutum mai kawaici da tsananin biyayya agareta data san dashi ya dawo me taurin kai da kafiya, dan haryau tunda yay magana daya tak bai sauya ba, duk fitina duk bala'i duk tashin hankli datake tayarwa agidan kullum abanza yake karewa..

nd worst part ma da ibaad yay banza da abun dan ko lkcin amsa baqar magnrta bai fiye samu ba bare ma yazo har gidan.

kusan satikai biyu ana wann case din, wanda ya bala'in jawo jiji da kai da ikon da prof yake ji dashi yay sanyi, atunaninsa yana da wani izza da ikon da zai saka hajiya mairo kai tsaye ta amshi batunsa ya zama maganansa kawai akaji, ya dauka dayaje gidan aka zauna akayi magana duk zasu rusuna ne abishi asaka rana.

yana tsammanin cewa kowane acikinsu yakejin matsanncin shakkarsa, he expect them to be worshiping his words as per thr richest son of the entire family, tunda yasan iyayensa sai yasan iya abunda yaga dama yake zanta musu, a tunaninsa aiyafi sauran yan uwansa daraja ne kuma ya isa ne shiyasa tun dacan iyayensu suke yawan bin bayansa akowani case inya taso.

saidai ayan kwanakin nan sosai dan uwansa zaidu ya bashi mamaki, despite all the threats, nd tantrums na hajiya amma wai zaidu bai rusuna ya musu biyayya akan maganan ba..

hankalin prof ya tashi matuka, musmn daya ga kamar he wont be able to have full control of the marriage ayi komi cikin tafin hannunsa kmr yadda yay tsammani, dan yanaso ne ace kowa na karkashin ikonsa ne sai abunda ya gindiya musu gameda yarsa kawai zasuyi.


arana na sha hudu da faruwar Abun tunda anty safeera tazo gidan zainab arifah tay lumi tafara musu eaves droping har saida taji kishin kishin lkcin anty safeeran take kan gaya ma hajiya hamida cewa ga abubuwan dake faruwa acan agida bappa zaidu yace kaza kaza ibaad ma yace bazai aure zainab din ba haryau kuma babu wata cigaban magana akan haka. tunda zainab taji haka tsoron yuwar rugujewar shirin ta sai ya bala'in rufeta
tarasa meyake mata dadi, tay kukan, ta shiga tsananin mamakin jin wai harma kenan tay yunkurin kashe kanta amma ibaad baisauko ya rusuna ba, to kenan batasan kuma me zatay yanxu ba.

her eyes were shut nd soaked in tears cikin rasa nayi tafara jin gara kawai tabar duniyan indai zata rayuwa taga ibaad da wata macen da ba ita ba, gara ta bar duniyan kawai. it was very hard for her to decide to end her life for real tunani tay wanda yakaita har safiya, as early as 5 am ta jawo wani allura da drugs da ake ma sport horses, lkcin tasan an kusa zuwa a dubata dan 6am ake zuwa duba jikinta tana miƙewa zaune kuwa ta danna ruwan alluran a hannunta witout regret for 5 min tana zaune can kafin yafara reacting tafara birgima kasa kafin kace wani abu ta dauke gabaki daya jikinta ya dawo kamar kankara da alama her body is shutting down dakansa dan wann karon dagske takey ba wasa ba.

haka aka sake farkawa da wata sabuwar tashin hankali agidan da sassafen aka rushing inta I.C.U under strick medical attention aka fara kkrin dawowa da circulation inta da oxygen da allurai likito ci sunkai shida akanta

untill it begin to feel like she is really dying hajya hamida tana kuka daga kofa tana faduwa akasa ana riketa, ana fara saka ma zainab shock...jiri ya debi prof ya fito waje jikinsa na rawa idonsa cike da hawaye da kuma fushi

ya dauko wayarsa dacan bappa zaidu ya fara kira da niyyar zaici masa mutunci snn ya jadadda masa cewa inhar zainab ta mutu toh wallah sai ibaad ya mutu..

yakira kira for some reasons bappa zaidu yana ganin kiran amma ya share sai bai daga ba har ya gaji ya dena.

gashi dama baida layin hajiya mairo ma saida ya kira uncle moh kai tsaye, yace ya kawo mata wayar, a hujajn sassafe lokacin ta idar da sallah lenan sai gashi ya shigo..yace hajiya yaa zayyanu ne ke son yin magana dake.

tunda taji ance shi ne gabanta ya fadi da sauri kuma acikin fargaba ta amshi wayar tace zayyanu lafiya kuwa kira da sassafen nan?

tunda taji muryansa ya fashe ya zama abun tsoro yana rawa rawa tamike tsaye tana cewa meye haka zayyanu meye kar kace min zainab ta mutu?

fadin hakan datay yasaka ya fara mata ihu yana gaya mata wasu irin tsauraran kalamai dat contains alot of threath na kisan kai kamar ba acikin hayyacinsa yake surutun ba.

suna gama wayar hajiya mairo ta yanke jiki ta fadi a sume jikinta na convulsing dakansa uncle moh yay maza maza ya daukota a hannu ahannu ya fito da ita awaje gidan ya kara rikicewa da hayya hayya ammi karama ta bishi ruwa ruwa aka kaita asibiti aka samu jinin ta ne yay mummunan hawa atake ashiga ciki da ita ana bata taimakon gaggawa

rudani yasaka kowa yay tsammanin ko mutuwa zainab din tayi, uncle moh yakira bappa zaidu da guntun rashin kunyarsa zai fara masa maganar banza kenan yaja tsaki baima tsaya jinsa ba ya katse wayar ya kira ammi karama

lkcin tuni anty safeera ta wuce asibitin da zainab din take wanda da kyar da wahala da tashin hankli kafin ECG na zainab ya dawo 30% kuma har yanxu bata farfado ba. sai a sann su prof suka dawo cikin hanklinsu saidai sosai suka dau zafi yanxu...


kafin isowar su bappa zaidu asibitin da hajiy mairo take already anty safeera ta kirasu uncle moh da ammi karama ta sanar dasu cewa zainab tana raye but she is not out of danger yet, anadai kan monitoring dinta...

hanklinsu ya dan kwanta amma kowa cikinsu na mata addua isowar su bappa zaidu ke dawuya Ammi babba ta tada sabon gulma tanata tambyr uncle moh abubuwa wanda ko gaisawa da yayan nasa baiyi ba ya hau dokin xuciya wai shi a dole xaa kashe musu uwa

wasu maganan ma da gatse yake gaya ma ammi babba game da halinda zainab din take ciki.. bappa xaidu ko ajikinsa baice musu uhum ba, ko Allah ya sawwaka baice ba, iyaka fatima yay wa few questions game da jikin hajiya tace masa likita yace hawan jini ne.

sun zauna a waiting room for a while kafin nan akaxo akace musu hajya mairo ta farfado ta xama stable, kusan atare suka shiga suka sameta ta kifa kanta tana hawaye kowa ya mata sannu ta amsa bata amsa bappa zaidu ba. sai can da likitta yazo yay musu bayani yace kar asake barin jininta ya hau haka of not zata iya samun temporary paralysis ga jikin tsufa, ana gama bayani ta kalle bappa xaidu tareda nunasa da yatsa cikin tsananin fushi tana cewa zaidu sai ka zuba ruwa akasa ka sha tunda kay amanna saika hada kai da rayyanu kun kashe yar dan uwanka har lahira,..tace itama kawai ya kasheta yaga bayan ranta ta amince zata mutu ta bar masa duniyan ya jika ya sha shida rayyanu.

shide baice komi ba tafara kuka duk su ammi karama suka  taru akanta suna bata hakuri kawai tafara bori tana cewa "zaidu inhar nina haifeka toh ka bari ayi auren nan kodan yarinyar nan ta samu lafya idan kuma kakiji wallah baxaka ki gani ba, kafin ka kasheni saina tsine maka albarka inde nono na kasha ka girma ba tsintar ka nay a bola ba tsinuwata wallahi saiya bika marar hankali kawai taɓabbe.

tana gama koke kokenta ya bata hakuri, shide baice eh ko aa ba. ya kama hanyarsa ya fita kowa nashan mamakin irin taurin kai da kafiyarsa.

wajen aikinsa ya wuce direct ya shanshantr da maganan duk dama kalaman hajya ya balain sosa masa ransa sosai, sosai jikinsa yake bashi wann auren da sukeso su kullan kawai lalata rayuwar ibaad zasuyi dashi. he wil not have  freedom, or will in it, infact he wont have a say in it so suke su maidashi bawa ga rayuwar xainab arifah da mahaifinta sai abunda sukaga dama zasuyi da rayuwarsa ta nan gaba. he knws what he is doing sosai shiyasa yaki sam ya sauko dan inyayi sake tamkar yaci amanan maraicin ibaad ne dan yasan kasancewa surki awajen prof yana tafe ne da kalubale babba.

tunda yaxo office bai kara kula wani kira daga gida ba, har aka sallame hajiya mairo ammi karama ce take wahala da ita kusan komi ita take mata  asashenta. banda raki da baqaqen maganganu babu abunda hajy take xubawa daga ta kwanta sai tafara kuka tana cewa wallah wallah akan wann magana dai ta tsine ma zaidu albarka zata daga masa nono wann furucin nata sosai ya dinga daga ma ammi karama hankli.

da yamma bayan komi ya lafa prof dagacan yayi xuciya already ya fara hada case zazzafa yana neman yay sueing din ibaad a kotu da case me karfi wanda xai gigita musu hankali, kmar kuwa ammi karama tay nazarin hakan babban kawar hajy mairo tana zuwa ammi ta samu sarari ta musu sallama ta koma sashenta ta shirya sharply ta saka doguwar jilbab dinta dark green colour dayay mata kyau sosai, babu dandanin kwalliya a fuskarta ta shafa turare ta sabi jakarta ta dau motarta cikim gaggawa ta nufi ofishin bappa zaidu da yamma

ana daf da zai tashi ta iso wanda tun a mota ta riga tay duk wani nazarin da zatay akan maganan nan ba, tasan in akaci gaba haka za'ay asarar xumunci da zaman lafya atsakanin su dayawa. aganinta tunda dokokin prof bai shafe kar ibaad ya kara aure anan gaba ba, ai zai iya auren xainab din kodan darajar kwacinyr hanklinsu duka inyaso daga baya ya auro duk wacce yakeso ya aura.

da wann tunanin aranta ta shigo ta samu bappa zaidu duk dama baisha mamakin ganinta ba amma dakyar ya nitsu ya kulata, dan kwata kwata baison ta saka baki acikin case din nan, yasha mamaki ma da hajiya bata umarce ta akan ta tursasashi ko ibaad su karbi auren nan ba. duk dama yana mutuwar sonta amma it was hard for her to convince him cewa a radin kanta tazo ba hajiya bane ta aikota ta lallabeshi..she try to convinced him to her best of ability amma inaa, bai sauko ba saida yaga ta xuba masa gwiwa akasa tana hawaye tana kuma jaddada masa cewa ita kadai baxata iya langwasa ibaad ba shine kawai zai iya gayama ibaad abu snn ya amince masa kai tsaye, idan shi bai sauko sun gyara abun acikin nitsuwa da hankali ba mutunci zai zuba, kima da darajar gidansu kwanan nan zai xube a gaban kotu, snn shikansa bazaiso yay rayuwa da tsinuwa da bacin ran mahaifyarsa akansa ba

da kyar da lallami da karya masa murya ta rarrashe shi, tace zata rakasa yanxu suje gida kawai ya bawa hajiya hakuri inyaso ayi magana ta kare daga yau...

har cikin ransa baiso haka ba, amma duba da manya manyan hikima dake cikkn zantukan fatima da inda ta durkusa agabansa tana masa kuka yasa kawai ya hakura yabita sukaxo gidan atare.

wanda tun a mota yake ta fayyace mata illar da wannan auren zaiyi arayuwar ibaad, da yadda baiya kaunar ace shida hannunsa ya jefa ibaad acikin wani yanayn rayuwa dazai cutar dashi...

yana maganan muryansa harna rawa cos at some point zaka rantse shiya haife ibaad
bcos the way he loved him nd cared for him ko mahaifinsa na asali baimasa son dayake nuna masa ba, inda kuwa an barsa da bazai taɓa saukowa ba saidai ayi duk abunda za'ayi bai damu ba dan inda gidansu ne ansha nuna irin wann son zuciyar bayau aka fara ba...

ubansu al-mansur ma halinsa kenan yafi hajya mairo son kai da nuna bangarenci da nuna bambamci, saidai baiyo tsammanin hajiy mairo son ƴayanta zai rufe mata ido harda zata zaɓi ta cutar da maraya kamr ibaad ba. wani bin sai yaga kmr ana wasu abubuwan ne dan anga asalin uban ibaad din baya raye, ammi karama kuma karamar mace ce har yanxu duk sun girmeta nesa ba kusa kai ko muhammadu ya girmeta ko tacema zata karba ma danta yanci bazasu taɓa saurararta ba dukan kawunanta na can maiduguri duk suna bin bayan hajiya ne, saidai ma agaya mata maganan da xaizo ya dameta a zuciyarta.

dada fahimtar irin son dayake ma ibaad din yasa ammi taji sanyi aranta hawayenta na sauka tanajin tausayin shi tare da kaunarsa aranta har suka iso cikin gida

idanunta sosai yay jaa, kafin su sauko sai ta dau lokaci acikin mota tana bashi hakuri da tattausar lafazi ta dinga lallabashi har suka karaso cikin gida...

yamma ne lisss ammi babba tana sama sashen anty safeerah taje jin gulma game da jikin zainab,wani dan uban dadi taji dataji cewa prof ya harxuka ya fara kiran lawyers zasu kafa babban case akan ibaad dan axo a kulleshi a walakanta sa.

lkcin gidan yay shiru ammi karama suka karaso inda tun akofar ashen hajia sukejiyo muryanta tana kan koke koke ma kawarta hajya hajara akan abunda ke faruwa da ita duk ta rasa yadda zatayi da ranta dan bata taɓa sanin zaidu yana da wann taurin kai da kafiyar kafurcin ba

ita babban damuwarta shine kawai a amshi auren kodan kar araba danta xayyanu da yarsa a duniyan nan, cewarta mutuwar matashi ya fi girgiza iyaye gashi itace musu kwalli daya inta mutu bazasu sake samun haihuwa ba har abada.

ammi karama tana gaba bappa zaidu yana biye da ita abaya anitse sunayin sallama a falon hajiya mairo ta kara hade rai tana kan jan majina jin muryan xaidu yasa bata amsa ba ta kauda kanta gefe cikin tsananin fushi..

da sanyin jiki ammi karama ta masa jagora bata barsa ya zauna akan kujera ba suka zauna akasa atare...

tun basu furta komi ba hajy hajara ta kallesa da muryan kuka itama tafara cewa zaidu wallh kabani kunya ko kadan banyi tsammanin zaka mana haka ba. kai da nace kaine zakka shine zaka watsa min kasa a ido, ace kaine dakanka ka rufe idonka akan maganar da bai taka kara ya karya ba?? kana cutar da rayuwar dan uwanka da kuka zauna aciki daya kuka fito atare, haba zaidu haba zaidu habaaa
...yanxu kaji dadi kenan da kasa hawan jinin mahaifiyarka ya tashi?? gaskiya bansan ka da wann mugun halin ba..

cikin katseta da sasanyar muryarsa me cike da dattako yace Hajiya mama hajara ayi min afuwa. daga sai bai kara cewa komi ba, har saida ammi karama ta kalleshi da fuskar magiya snn ya mike ya karaso kusa da hajiya mairon yace "Hajiya kiyi hakuri da dukkan abubuwan dake faruwa, ina sane da cewa ke mahaifyata ce wanda darajarki bai taba gushewa araina ba duk wani hukuncin da kikaga na yanke akan ibaad bawai nayi bane dan na kuntata muku saidan na kare amana da martaban maraya da yaa mustafa ya tafi ya barmana, gadai fatima tana kallo kuma tana zaune akusa dake kusan kowani lokaci tana kulawa dake but at same time kina zagin dan cikinta, kina ambatarsa da mugayen halaya duk da kinsan ba gaskiya bane, kin bijiro masa da auren dole me cike da tsauraran dokoki bakiyi la'akari da yadda abun zai gurbata rayuwarsa ba, shin kin nuna masa kenan farincikin wasu acikin yayanki yafi na wasu?inda yaa mustafa yana raye shima xaiso ne ayi ma dan cikinsa irin wannan kaskantcen auren? agabanki zayyanu yace bayason ya hada jini da mu..kuma alfarma xai ma yaron nan, snn ga zargi, ibaad fa jikanki ne hajiya, kenan farin ciki da rayuwar jikokin ki masu abun duniya da dukiya sunfi miki na shi dayake maraya ko? ke baki tunanin duk wnn abun da kikeyin zai dame zucyar ibaad? kuma zai ce inama da ubana yana raye ya karba min yanci?...shin idan muka taru muka nuna masa shi marayane baida daraja a gidan nan waye ya kamata ya tsaya masa a duniya? ina zaije yaji sanyi, bayan ga fatima anan tare dake bata taɓa saba miki ba...duk da zagin dakike ma danta koyaushe, shin hakan yana mata dadi ne? ke uwace fa hajya bazaiyu kice komi laifi bane, musmn inde har bai sauka an favorites dinki ba.

yana maganan wani irin shiru falon ya dauka cikin sauke ajiyan zuciya hajy hajara tace
hakane zaidu kay magana ta hankali amma kuduba Allah aceto rayuwar yarinyr nan, duk wani uzuri da zaka bayar baikai nauyin rai ba, duk wani qaddarar da ibaad zai dauka bazai kai wanda zayyanu zai ji aransa indan ya rasa yarsa kwalli daya daya haifa a duniya ba..memakon kuyita hayaniya maslaha zaku samo acikin wann matsalar dolene fa sai wani ya dauki mummunn qaddara acikinsu tunda shi soyayya Allah ne ya dora mata bayin kanta bane...yarinya kyakwya haka data taso acikin dukiya da gata wallah bazata so ta kashe kanta ba inba akan abunda yafi karfin tunaninta ba, zaidu ka duba Allah arufe maganar nan

yace "bakomi hajiya ni dama fatima ce ta dauko ni akan inzo abama hajy hakuri kuma in sha Allah zan tuntube shi ibaad din da maganan..saidai muy addua Allah ya bashi ikon cin wann jarabawar..

yana rufe bakinsa hajiya mairo ta fashe da kuka harda shsheka taki tace komi dan bakaramin taɓa mata zuciya kalamansa yay ba, musmn na maraici da kuma yanda yajawo hanklinta akan abunda take yawan furtawa agaban fatima.

tashi yay ya koma wajen da ammi karamar take zauna sukay magana kasa kasa

hajy hajara kuma tana famar lallashin hajy mairo tana bata baki kasa kasa cikin kuka take cewa 'hajara kicewa fatima ta yafeni, wallah na rude ne
haka kawai bazan kuntata mata ba..sosai hjy hajaran ta tausaya mata

sai can ta dago ta kallesu tace toh zaidu yanxu sai munji kenan daga gareka...

a nitse yace in sha Allah..zuwa gobe!..yana gama furta hakan ya miƙe batare da ya kalle hjiya mairon ba da sanyin murya yace fatima muje ko?

mikewa tay da sanyin jiki tay gaba yana biyi da ita abaya har suka fice a asashen gabaki daya tarakasa har jikin motarsa suka cigaba da maganan awajen har ixuwa sallan magrib snn suka rabu ta dawo cikin gida.

kitchen ta shiga dan ta dora masu hajiya wani snacks da shayin da zasu kwana dashi ita da hajya hajara.

dagata bangaren su kuwa ficewarsu bada wuya ba kunya yabi ya lullube hajya mairo tana kuka tana fadin halacci, kawaici da alherin da fatima take mata..

hajiya hajya kuwa batay kasa agiwa ba,sosai ta cire son zuciya tay mata nasiha akan abubuwan datakeyi ta bala'in nutsar da ita musmn akan batun bambamce bambmce datake nunawa.

sunjima suna magana kafin nan ta shigo mata da maganan zaidu da fatima
..tace bata gane me ake jira dasu har yanxu ba?  da sanyin murya hajiya mairo tace "toh Allah ne dai baiyi lokci ba naje wajen malamai sunfi dubu a tudu amma duk ana cewa sihiri akay aka hanasu aure
..kullum sai ace muje mu cigaba da addua gashi lokci yana ta ja sunata tsufa...ai da tuni yanzu ta haifa masa yaya sunkai hudu ko biyar.

hajya hajara ta saki baki tace wann ma maganan banza ce, ke kuwa mai tuwo yarinyar nan fatima har nawa take? inbanda ma karya da kika dinga shera ma mutane fatima fa a yar shekara 16 tazo cikin gidan nan ko kin manta ne? har yanzu fa yarinya ce atata ace anbata shekaru arbain da hudu zuwa da biyar ba toh wallah in zaki mike tsaye ki mike bawai kawai anzauna ana ta cutar yarinya ba duk anbarta da juyi a gado me sanyi kullum ruwan  sha'awa na taruwa mata amara, tunda dai addua bai yi ba ai munjira, ynxu kawai mu hada kai munemar masu mafita.. yau kiga dai inda taje ta lallabo miki shi yaxo har gabanki ya durkusa ya baki hakuri, shin ita wancan balamar matar tasa tay miki hakan ne?shegiya mummuna banda gulma bata iya komi ba tunda nazo gidan nan ko ruwa banga tazo ta aje agabanki ba taje can tana yawo da sakakken duwaiwaka tana jin gulma awajen safeera toh wallah baxaiyu ba, inke yar kungiyar izala ce ni nariga na wuce nan sabida haka xanje
duk inda xanje wallah sai an cire yarinyar nan a azaba an aura mata mijinta ke kuwa maituwo wann uban mugunta har inaaaa kema fa da lefinki akanbyaran nan dan fatima ba yar cikinki bace shiyasa baki damu da halin da zatana shiga ciki ba shekararta nawa babu namiji aikekuwa kya tausayawa rayuwarta

jan ajiyan zuciya mai nauyi hajiya mairo tay tace "kune fa kawai kuke ganin kamar bana tausayawa fatima amma har raina bana tsammanin inada wata a duniyar nan danake jinta kamar yar cikina kamar ita, fatima fa tasha wahala dani. kedai tunda kince zakiyi wani abu akai toh ki gwada mugani nide inhar sihirin nan ya kunce ko yau yaune zan iya sawa a daura musu aure kowa ma ya huta..malamin nan cewa yay fatima zata mutu in akay auren ba a karya asirin nan ba, yanxu so kuke na mata auren da zai kasheta inta mutu ai ni aka cuta

hajy hajara tace yanxu naji magana toh yanxu dai kibani nan da wani lokaci in sha Allah wann aure sai anyishi nan bada jimawa ba, koma waye tay asirin zanje can kauyen mijina na, kinsansu ai kabilar jukunawa ne, dole ne muma mu tashi tsaye mu gwada musu muna da yadda zamuyi haba cutarwan yayi yawa....


#idan kinason cigaba da samun posting kibi shafukata

*AREWABOOKS*
*@SURAYYAHMS*

*WATTAPAD @SURAYYAHMS*


*WASAP CHANNEL ND GROP: SAVE MY NUMBER *** TO BE ADDED*


#SURAYYAHMS
#COMEBACK SERIES
2024/2025