BLOOD CROWN (THE HEIRS APPARENT)
PAGE _______21 & 22
by @swrites22
Kallon kallo akayi tsakanin Amjad da Widad kafin kowannen su ya ɗauke kai, jami'ai ne suka fara shigowa suna bincike tare da karɓar passport ɗin kowanne suna dubawa, tashi Amjad yayi ya wuce cikin toilet ɗin jirgin, hakan yasa Widad shi ma tashi da sauri sai wani jami'i ya sha gabansa da faɗin, "Your passport?"............ Komawa yayi ya zauna tare da miqa masa passport ɗin, karɓa yayi yana dubawa yana kallon sa har ya gama sannan ya miqa masa, tare da sanya portable millimeter wave scanner yayi searching ɗinsa sannan yayi gaba.
Amjad kuwa yana zuwa toilet din ya shige ko kula ma'aikaciyar dake tsaida shi baiyi ba ya shige ya rufo, buga masa ta farayi Amma shuru ba alamun zai buɗe, zuwa lokacin jama'ai uku ne a wurin, kallon su tayi da faɗin, "Make an emergency call"..........daidai lokacin Amjad ya buɗe ya fito yana gyara belt ɗin wandon sa. "hands up"............ ta faɗa tana nuna shi da pistol ɗin ta, ko alamar yaji bai nuna ba sai da ya gama gyara zaman wandon sa. "Search him "...........Ta sake faɗa tana kallon wasu jami'an mutum biyu.
Bai motsa ba haka Kuma bai ɗago ba har suka gama caje shi tare da miqa Mata passport ɗinsa da wasu ID'S ɗin da suka samu a jikinsa, karɓa tayi ta duba da sauri jikinta ya fara rawa, ba tare daya ɗago ɗin ba ya saki wani killer smirk da shi kaɗai yasan ma'anar sa, ita kuwa faɗi take, " I'm very sorry sir, we misunderstood you da ALLAH kayi hakuri akan aikin mu muke ne"....... Baice komai ba ila hannu da ya miqa mata, da sauri ta saka miqa masa abubuwansa, karɓa yayi yana sake janyo P cap ɗin sa ya har wurin.
Komawa yayi wurin zaman sa ya zauna ba tare da ya kalli inda Widad yake ba Wanda shi ma a lokacin ya zauna ko daga Ina yake Kuma oho.
Daga nan aka fara sanar da cewa an bawa jirgin izinin tashi saboda an kama masu laifin.
A bangaren su Ace kuwa sunji sanarwar da akayi hakan yasa hankalin su yayi masifar tashi sai Kai kawo suke, kiara ta ce, " I need to go inside....."
"To do whattt?". Ace ya amsa yana baza hannu cikin gashin kansa cikin yanayi na rashin nutsuwa.
"You know there's gonna be a problem if we don't do something, so let's go do something about it"............. ta amsa masa a zafafe tana wucewa, cikin zafin nama ya fisgo hannunta tana kokarin faɗuwa ya sanya mata ƙafa ta tsaya cak jijjiga mata Kai yayi da faɗin, "kinsan waye boss sannan kinsan waye Widad har meysa zaki tashi hankalin ki".
"But A......"
"Shiii, mu tafi kawai"............. Girgiza masa Kai tayi ta buɗi baki kamar zatayi magana sai Kuma tayi shuru, sanarwa suka faraji cewa jirgi zai tashi a tare suka sauke wata ajiyar zuciya, ɗagowar da zasuyi suka hango Kia na fitowa daga cikin airport ɗin tana tura wani Abu cikin aljihun jacket ɗin dake jikinta taku take kamar ba mace ba, tana zuwa ta wuce su ta shige mota tare da ja ta bar airport ɗin gabaɗaya dan dama da mota biyu suka zo Ace da Amjad da widad, sai kiara da Ashley.
"Ni ka hanani amma Kuma gashi ita taje tayi abinda ya kamata"........Rasa me zaice da ita Ace yayi saboda bai san ya akayi ma ya tsaya riqe Ashley ba a maimakon kiara da duk suka san halinta in ta furta Abu to fa sai tayi gata da brain, she's very smart saidai in bataga dama ba Wanda hakan ne yasa Amjad ke warning ɗinta da Kar ta bashi matsala. Tare Ace da Ashley suka shiga mota ya jasu suka wuce gida su ma.
Tafiyar 6 hours 30 minutes sukayi a sama kafin su sauka a babban birnin Nifaz, ko kallon juna basuyi ba kasancewar Widad shi ma haifaffen ƙasar Nifaz ne. Amjad kuwa yana fitowa ya tarar da kamal yazo ɗaukan sa shiga yayi tare da faɗin, " Livy Street".......... Hakan yasan Kamal gane ainahin gidan sa suka dosa.
--------------------√
Kamar yadda ta saba Kiran sallar farko akan kunnen ta akayi dan daman batayi wani baccin kirki ba saboda duk da maganin sauron data sa abun yaci tura kasancewar yanayi na damuns sauraye sun yawaita, kusan kwana tayi tanawa Shazeen firfita. Miqewa tayi ta wuce toilet ɗin nasu dake cikin ɗakin ta ɗauko buta ta fito tsakar gidan, Duhu ne dan haka tayi amfani da hasken wayar ta wurin haskawa ta daibo ruwa a rijiyar data gani a tsakar gidan daga can gefe ta zuba a butar sannan ta ɗauka ta wuce, tana kokarin komawa ɗakin nasu Sahnish na fitowa daga nasa ɗakin, miqa yayi tare da faɗin, "Har kin tashi ashe? na ɗauka zaki makara ai saboda gwajabniyar jiya".
"Wace gwajabniya kuwa, kaji ka kamar jiya muka fara".......... Ta fads tana shigewa ɗakin.
"Yanzu dai na jiraki kenan ki miqomin butar?"........... Tsayawa tayi da faɗin, "Ba toilet a ɗakin ka ne?".
"Ahh lalle jiya a ruɗe kika shigo gidan nan, Saida fa kika shiga kika duba kowani ɗaki duk a lokacin baki lura ba toilet ba".
"Ina fa na lura, ka shigo to in na gama sai na baka".
"Barni in sha iska kinji ɗakin nan kamar kurkuku Yasin, ke dai in kin gama miqomin ai naga ma ga toilet nan a waje".
Wucewa tayi ta barshi, Saida ta ɗauro alwalar ta dawo ta tashi Shazeen taje tayi itama da ragowar ruwan data rage mata, sannan taje ta ɗauko butar ta leqo ta miqa masa ta koma, hijaban su ta ɗauko musu ta shimfiɗa darduma suka tada raka'atanil fajr sannan suka ɗan zauna har aka Kira sallah sukayi, suna gama azkar Shazeen ta koma bacci ita Kuma ta tashi ta fita, samu tayi rabin mutanen gidan duk sun firfito masu ɗiban ruwa sun bi layi dan guga ɗaya ce haka zalika da yawa daga ɗakunan basu da toilet sai wanna na waje guda ɗaya, ɗakin Sahnish ta wuce inda ta tarar dashi zaune kan Abun sallar da ya idar da sallah zama tayi da faɗin , "Sahnish dole fa mu nemi stove kaga dai ba zai yiwu na kunnawa mutane gawayi a ɗaki ba a zo a samu akasi na babbakawa mutane guda".
"Nima tun jiya nayi wanna tunanin amma Kuma kina da kuɗin ne a hannun ki ?".
"Babu whl dan abinda ke hannu na baifi na ɗan Abun da zamuci ba a hakan ma inaga ba zai Kai mu wata ba, har Ina tunanin ko zan tambayi wani abu daga cikin albashi na, sannan Kuma ga batun canzawa Shazeen makaranta".
"Canjin makaranta Kuma ?".......... Ya tambaya yana jifanta da kallon mamaki.
"Eh suna Ƙare zango nan kuwa tunda dama zangon karshe suke zasuyi canjin aji, zan nema mata wata me haɗe da islamiyya kawai Wadda in ta tafi tun safe sai 6pm ko 5 ".
"Meysa to?"
"Ni da Kai ba yara bane munsan daidai da ba daidai ba amma ita fa? zaman gidan nan zaiyi matukar tasiri akan tarbiyyar ta ya Kuma gurɓata tunanin ta".
Ajiyar zuciya Sahnish ya sauke da faɗin, " ALLAH ya kawo yadda za'ayi, nima yau zan fita lalube na ALLAH yasa na dace".
"Amma kasan Kai zaka ɗauko ta daga makaranta ko, Kuma in ka ɗauko ta karka fita ku zauna a ɗaki sai lokacin islamiyyar su yayi ku fita tare".
"Aiki sabo kenan".
"Haka zaka daure, ni bari kaga naje na shirya ban ma san inda zan samu ruwan ba naga sunyi layi kamar masu karɓar sadaka gwara nasan nayi tun wuri "........... Ta ƙarashe tana tashi ta fice, layin data gani yanzu yafi na ɗazu dan haka tayi saurin shiga ɗaki ta ɗauko bucket ɗin su tazo ta sa a layi sannan ta koma kan wani benci tana kallon masu Kai kawo daga masu ɗaura kirji sai masu vest Kuma harda matan aure wai, wani mutum ne ya fito daga wani ɗaki hannu maqale a kirji sai wani gatsina yake, "Rama ke rama kina Ina ne fatan dai kin samun bokiti na dai, Dan nace Miki yau sammako zanyi zamuyi tafiya da Alhaji".
Rama dake ebo ruwa ta ce, "Da ALLAH Shamsy karka dameni ni, ladanka na samu ma da zan ebo ma ɗin".
Sake noke hanci yayi da faɗin, "To yar masu gida, kema kinsan ko banza da bazata kike rawa, in kika min rashin ta ido kuwa ki gani a ƙwaryar ki".......... Ya ƙarashe yana murguda baki tare da dafe hanci sama.
Ita dai Hushaima dariya take a zuciyarta amma a zahiri wani ɗan guntun murmushi me siririn sauti tayi tare da tafa hannu a zuciyar ta ta ce yau Kuma ga inda rayuwa ta juyo daku Hushaima.
"Wace shegiyar ƙafar ke mun dariya ne anan, ni whl ƙaramin aiki na ne in kwaɓe mu daku da kowace shegiyar karuwar da takejin ita balagaggiya ce, ba abinda ya Sha min Kai , to in banda ma iskanci taya mutum yana magana ana masa dariya dan dai anga mutum bai shiga harkar kowa ba".
Taɓe baki Hushaima tayi tare da duba wayar ta ganin suna neman yin late especially Shazeen me makaranta gashi su kuma sun tsaya kace nace basu iba ruwan ba basu bar wasu sun ɗiba ba, tashi tayi ta ɗauki bucket ɗinta ta matsa gaban rijiyar ta ajje, gugar da wata mata ta danne da ƙafa ta janye tare da ƙoƙarin zurawa cikin rijiyar, wata irin danka taji ta bayanta tana juyowa sukayi ido hudu da wata budurwa kana ganin ta kaga tatacciyar Yar duniya. "Ke wani kikafi ne anan wurin da baza ki iya jira layi yazo Kanki bane saboda ke gaki shafaffiya da Mai, to baki isa ba kauce ki ban wuri".
"kiyi hakuri uzuri ne dani ba wani me yawa zan iba ba ".
Dukan kafaɗar ta tayi cike da tashen iskanci dake fisgar dusar kwakwalwarta ta ce, "ke baza ki iba ba har sai na ɗiba yaso su sokayen in sunga dama su hakura su zuba Miki ido ki ɗiba".......... ta ƙarashe tana matsar da ita ta warci gugar ta jefa a rijiyar.
Girgiza Kai Hushaima tayi tare da ja baya ta bata wurin, "Duduwa kawomin kapilas ɗin nan na Ƙara dashi".
"Ke kin ma isa"........ Wadda take Kan layi ta faɗa tana watsa Mata wani kallon banza.
"Wani irin na isa ni da gidan uba na, ke zan tambaya ma kina yar kale"..........Ta faɗa tana riqe kugu.
"Ke da ALLAH dakata uban naki ai ba kyauta muke zaune a gidan nasa ba, zaman kuɗin mu muke yauwa".
"Ke kowa layi yazo kansa sai ya iba iya adadin abinda ya ke so, Dan haka baki isa hana ni iban ruwan nan ba whl"........Hayaniya ce ta barke a tsakanin su kamar zasu bawa hammata iska kowa na mayar da martani cikin zafi.
"Tou Tou ALLAH yayi dare gari ya waye tsoffin guzmaye an tashi za'a fara halin da aka Saba "......... Da mamaki Hushaima ke kallon Baba ilerika da ya shigo ashe ba'a gidan ya kwana ba dan baiyi kama da wanda ya kwana gida ba, yana hangota tsaye ya ƙaraso yana faɗin, " Hajiya kece nan tsaye, ba dai hanaki ɗiban ruwan sukayi ba".
Ba yabo ba fallasa ta ce, "Layi ne baizo Kai na ba ai, mun tashi lpy?".
Wani ashar ya lailayo tare da faɗin, "Duk Ku gyara ku bawa hajiya wuri ta ɗiba"....... A tare sukace bamu gane ba ita hajiyar wankakkiya ce data fi kowa kenan".
Warce gugar yayi Yana faɗin, "Ke ban wuri dan uwar ki, bana son tumasanci ".
"Amma dai Abun da kake yi kasan ba daidai bane ko"........... Yarinyar da ya warci gugar a hannunta ta faɗa tana harararsa ƙasa ƙasa, fasa zura gugar yayi tare da ɗaga ta da nufin buga mata da gudu ta bar wurin. "Na dauka kin girma ai, to ko uwarki bata isa in tsaya ta tsaya Ina magana tana ce min ba haka ba dukda nasan duk wani iskanci uwayen ku ke koya muku, to whl ku shiga hankalin ku dani a gidan nan kafin na shata muku tsagwaron rashin mutuncin da yafi naku, ƙananun yan iska kawai".
"Bari na ɗiba ruwan Baba ilerika"........... Hushaima ta faɗa a ƙoƙarin ta na karɓar gugar ganin Baba ilerikan ya buɗe wata sabuwar chapter magana.
"Bari na ɗaibo Miki mana".........Ya faɗa Yana katse masifar da yakeyi ya ja ƙwafa ya zura gugar. Cikin jin daɗi Hushaima tayi masa godia tare da komawa gefe ta tsaya, Nan fa yan ƙananun maganganu da habaice habaice suka fara tashi dan dai ba yadda zasuyi da Baba ilerika ne saboda tijirarsa tafi ta kowa a gidan mutum ɗaya yake tsoro shi ma wato babbar yar sa wadda ta kasance uwar dakin duk wata me bakin uwa ita Kuma ba cika zama tayi a gidan ba sai tayi wata nawa bata leqo ba gidan ba.
Saida ya cika Mata ruwan a bokitin taf sannan ya ɗauka Yana faɗin, " Muje a Kai Miki, Ina aka taɓa tarbar bako haka, banda ma mutanan gidan nan da ba mutunci suka sani ba"......... Ita Hushaima ma nauyin abun ta fara ji ganin sa babba Wanda zai iya haifar Wadda ta fita ma amma shi ko a jikinsa da alama ya saba irin wanna fadancin, a ƙofar ɗakinta tace ya ajje mata zata ƙarasa dashi sannan ta sake masa godia ta ɗauka ta shige.
A gurguje tayi Wankan ta tashi Shazeen ta shiga , kaya tasa ta fita ta kaiwa Sahnish kuɗin da zai siyo musu waina da kunu, sannan ta Koma ɗaki ta ƙarasa shiryawa. Tana cikin maqalawa Shazeen igiyar takalmi Sahnish ɗin ya shigo ya miqa Mata ledar sannan ya zauna yana faɗin, " wai me ya faru naga duk inda na gifta a gidan nan daga masu nuna ni da hannu sai masu yi da baki sai kace wanda yayi wani abun kunya".
Sai da ta juye wainar a kwanu sannan ta ce , "Kai yanzu miye abun faɗa ma, in kana da damuwa da hakan zuwa zakayi Ka samu duk Wanda ya nuna Ka ɗin ya nuna ma abun nunawa a jikin Ka"..........Ta faɗa hakan dukda kuwa tasan ko za'a sa masa wuqa a wuya bazai iya ɗin ba. Hararar ta yayi tare da dauke Kai bai Ƙara cewa komai ba harta turo masa nasa cup ɗin gabansa tare da ajje Kwanun wainar a tsakiya ta miqawa Shazeen nata cup ɗin kunun ita Kuma ta riqe nata da ɗayan hannun tana fadin, " Shazeen shaf shaf (sharp) fa Kar mu makara".
A gurguje suka gama sannan ta ɗauki Jakarta suka fito gabaɗaya, kulle ɗakin tayi ta miqawa Sahnish makullin, "Gashi nan Ka Kula saura kazo Ka cemin ya ɓata".
"Ba zance ba, a dawo lpy"..........."Sai mun dawo yaya". Shazeen ta faɗa tana ɗaga masa hannu.
" To Shazeey a dawo lpy, ayi karatu sosai".
Tunda suka fito bata ɗaga ido ta kalla kowa ba harta fice a gidan dukda kuskus ɗin dake sauka cikin kunnenta. A kofar gidan ta tarar da wata sabuwar kasuwa kowa da abun da ya kasa me awara, me kosai, me waina , me dankali, me kunu, me shayi kowa na Kai kawon sayan abinda zai karya, jijjiga kanta tayi kawai taja hannun Shazeen suka wuce bakin titi, kasancewar babban titi ne yasa basuyi wahalar samun abun hawa ba, saida ta Kai Shazeen makaranta sannan ta wuce wurin aikin nasu.
Tana shiga da Jumayma ta fara cin Karo, ko nuna ta ganta batayi ba ta fara ƙoƙarin wucewa, tsayar da ita jumayma tayi, "Hey wait tsaya Nan".......... Ja tayi ta tsaya fuskar nan ba sauki Amma bata ce komai ba. "Jiya me ya hanaki zuwa? sannan kuma baki yi report ba".
"Kece me wurin ko ke zanwa refot din?".
"Amma ni ke da alhakin supervising ɗin Ku ai tare da sanin ya performance ɗin ku yake, Amma ke daga farawa kin fara skipping Kuma a haka in wata ya cika ba'a baki salary ɗinki daidai ba kice an miki rashin adalci".
Dukda bata fahimci English words ɗin ba amma a jimlar da sukazo yasa ta ɗan fahimci wani abun. Dan haka ta gyara tsayuwa da faɗin, "Ashe kin samu qarin matsayi bayan gadin masu shige da fice da aka baki, to in kina da hannun jari a wurin nan karki barni na wuce sa'o'i 3 kinji, ɗaya biyu uku "........... Ta ƙarashe tana irgawa da yatsunta. "In kuwa har sa'a uku ta wuce ina nan wajen to kin cika banza marar abun yi me gadi". Tana gama faɗa ta wucewar ta ciki ta bar Jumayma baki Buɗe.
"Ni kika fadawa haka ? lalle talaka bai san samun wuri ba, ni kuwa nace har tulu yayi dariyar tukunya bayan duka ƙasa ne. "To Bari hajiyar tazo zakuwa kisan ni ba banza bace, jaka me kwakwalwar kifi bata gane komai sai iskanci".......... Ita dai Hushaima ko juyowa batayi ba tayi shigewar ta.
Lokacin da hajiya tazo da baƙi suka shigo hakan yasa Jumayma bata samu damar Mata magana ba har saida suka tafi sannan ta samu shiga office ɗin nata, saidai me tana shiga ta samu Hushaima ciki suna magana, turus taja ta tsaya yanayin ta na nuna rashin jin dadin ganinsu ɗin a haka. "Yauwa gwara da ALLAH ya kawo ka Jumayma, ƙaraso".........Hajiya ta faɗa.
Cikin sanyi jikin da bata San yadda akayi ya lullube ta ba ta ƙaraso tana harara Hushaima ta nemi wuri ta zauna. "Jumayma meke faruwa ne tsakanin ke da Hushaima?".
"Me tace Miki hajiya?".
"To ai ke na tambaya ko, tunda ita naji nata?......... Abinda ya faru da safe ta faɗa Mata tare da maganganun da Hushaima ta faɗa Mata sannan ta ɗora da, "Hajiya tunda ta fara aiki haka takeyi min, Kuma ko ba komai duk ma'aikatan wurin nan suna bani girmana, Amma ita sai tai ta wani jijji da Kai kamar wata yar sarki".
"Ya isa to, ke Hushaima kinji haka ne?".
"Ko kusa ba haka bane ranki ya daɗe, abinda dai da na gaya Miki Shi ne daidai, don ni tunda na fara aiki wurin nan Jumayma bata so na kamar na tare mata wani Abun, ƙarshe ma cewa tayi taci alwashin sai tasa kin koreni, hajiya bansan abinda zai faru ba a gaba gwara tunda mutunci na kawai na hakura na bar wurin nan, na nema a wani wurin tunda abun ba zai yiwu ba".
"Baza ayi haka ba Hushaima, ka kwantar da hankalin ka ai ni ke da wurin ko, ba Jumayma bane ke da ikon korarka dan haka karka damu, kai kuma Jumayma dan ALLAH Kar naji Kar na gani, Bana son irin wa annan ƙananun zancen masu Kai kawo. Ba sanin juna kukayi ba ba komai ba anan fa kuke haɗuwa kawai daga an tashi Kuma shikenan, Kuma in ma Hushaima ya bar aiki anan miye ribarka Jumayma, wani ai baya tarewa wani Abun da ALLAH ya bashi. Da ALLAH Kar na ƙara jin Abu makamancin haka".
"In sha ALLAH Hajiya". Jumayma ta faɗa Amma a zuciyar ta kuwa wani haushin Hushaima take ƙara ji.
"Haka nake son ji, kuna iya tafiya, Jumayma kai kuma ka kawomin lissafin nan"........ Da "To"......ta amsa sannan ta tashi ta fita, gyara zama Hushaima tayi da faɗin, "Ranki ya daɗe dama ina da wata yar magana ne?".
"To inajin ka"......... Hajiya ta faɗa tana bawa Hushaiman duka hankalin ta.
"So nake a bani wani Abu daga cikin albashi na a karshen wata sai a Zara"...... Shuru hajiya tayi kafin ta ce, " Gsky there's no way da zan iya Baka wani Abu daga albashin ka, saboda kai sabuwar ma'aikaciya ne ko albashin farko baka fara karɓa ba, ka dai yi hakuri ko ka nemi rance wani waje in watan yayi saika biyasu".
"Shikenan Nagode Hajiya ba damuwa"....... Daga haka ta miqe ta fita ta koma bakin aikin ta .