KOMAI TSANANI

19

by @oumfatima33

🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂
    *KOMAI TSANANI* 

             *By*

         *KANSA'U* *BELLO* 
    
   *(OUM FATIMA)* 
🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂


   *PAGE 019* 


 *BISMILLAHIRRAHAMANIRRAHEEM*




    Mamu sai da ta share hawaye sabo da tausayin irin rayuwar da jikarta tayi alhalin tana raye cikin jin daÉ—i da wal-wala, ji tayi sam basu kyauta wa Khamis ba don da ace zai dawo ya ga yanda suka kasa kula wa da amanar daya bar musu ba Ć™aramar kunya zasu jiba. Amma yanzu komai yazo Ć™arshe in sha Allah zata É—auki matakin daya dace, zata yi Ć™oĆ™arin gyara kuskuren da suka yi.

    Yau za'a gudanar da Mother's day a cikin katafaren hole É—in taron dake cikin Mansion É—in, Ć™arfe 5 na yanma za'a fara gudanar da taron don haka tun bayan sallar Azahar masu decorations suka zo suka Ć™ayata wurin yayi matuĆ™ar kyau. Duk abin nan da ake Nanah na É—akin Mamu abinta ta É—auki wayarta tana ta danne dannenta, yayin da sauran yaran gaba É—aya duk sun bazama cikin gidan kowa ya haÉ—e da wan da tasu tazo É—aya. 

   Bayan sallar la'asar Nana na kwance saman gadon Mamu tana karanta littafin azkhar wata kyakykyawar budurwa ta shigo É—akin da sallama tana Ć™wala kiran suna Mamu.

   "Bata nan ta sauka Ć™asa." Nanah ta faÉ—a da siririyar muryarta wacce ta janyo hankalin Anisa gareta.

   "Masha Allah." Ta furta lokacin data É—aura idona a kan kyakykyawar matashiyar yarinyar dake kwance saman gado tana karanta littafin azkhar É—in Mamu data É—auka. Sosai yarinyar ta burgeta ganinta kyakykyawa Masha Allah, gata da manyan idanu farare Ć™al masu É—aukar hankali don lokacin data kalleta dasu har wani maiĆ™o-maiĆ™o ta gani kwance a cikin su. Cikin natsuwa ta shiga Ć™araso wa in da take tana kallonta.

   "Wacece ke?." Tayi mata tambayar tana Ć™ara zuba mata ido. Tashi zaune Nanah tayi tana gyara wuyan rigarta daya É—an zame ta kalli Anisa tace.

   "Sunana Maryam ana ce min Nanah." 

   "Nice name, wurin granny kika zo?." Anisa ta faÉ—a tana kallon ta. Nanah na Ć™oĆ™arin bata amsa Mamu ta shigo É—akin da sallama. Ganin Anisa zaune kusa da Nanah yasa tace.

   "Yauwa Anisa gara da kika zo, dama yanzu nake neman wanda zan haÉ—a da wannan mai tsoron mutanen." 

   "Granny wacece ita?." Anisa ta mayar da tambayar kan Mamu.

   "Ćłar'uwarki ce Ć´ar waje Kawunku Khamis daya rasu." Mamu ta bata amsa.

   "Lah dama ita ce wannan kike bamu labari, amma me yasa bata taÉ“a zuwa ba ita?." Anisa ta faÉ—a cikin farin cikin jin cewa Ć´ar'uwarta ce don haka kawai jininta ya haÉ—u da yarinyar.

    "Mamanta ta tafi da ita wani gari mai nisa shi yasa baku santa ba." Mamu ta bata amsa a taĆ™aice.

   "Tana da kyau sosai Mamu." Nisa ta faÉ—a sannan ta miĆ™awa Nanah hannu tace.

   "Sunana Anisa, zamu iya zama friends?." Murmushi Nanah tayi mata wanda ya loÉ“a kyakykyawan dimple É—inta dake duka kumatunta ta gyaÉ—a mata kai.

   "Kina da kyau sosai Kamar Hammanah shima yana da irin naki." Anisa ta faÉ—a tana saka yatsarta a kumatun Nanah Murmushi Nanah ta kuma yi mata bata ce komai ba.

   "Wai ke bakya magana ne?." Anisa ta faÉ—a kasancewarta mai surutu sosai.
   
   "Ina yi mana Nanah ta bata amsa a hankali.

   "Kin ganta nan tun da suka zo take zaune a É—aki tamkar mai jin tsoron mutane." Cewar Mamu.

   "Shike nan yanzu kizo muje É—akina mu shirya a akwai event da za'a yi yau a gidan." Cewar Anisa tana kama hannun Nanah.

   "Bari na É—auki kayana to." Nana ta faÉ—a.

   "Ok." ta faÉ—a tana sakin hannunta, school bag É—inta data zubo kayanta a ciki ta buÉ—e ta fito da sabon É—inkinta a cikin wanda Yaya Khalid ya mata.

   "Kinga ki bar waÉ—an nan akwai anko da Ammy tayi min Tailor É—in ya É—inka yayi min kaÉ—an aka sake wani na san zai yi maki." Anisa ta faÉ—a tana riĆ™e hannunta suka fice, da kallo Mamu tabi su tana murmushi, sosai taji daÉ—in yanda Anisa ta jata suka tafi ko ba komai zata saki jiki ta.

   Kai tsaye É“angaren Hajiya Raliya suka nufa tare da Anisa, har É—akin Ammy ta kaita suka gaisa take mata bayanin wacece ita. Da fara'a sosai Ammy ta amsa mata suka wuce É—akin Anisa kasancewar Ammyn na tare da Ć™awayenta da suka fara taruwa domin gudanar da Mother's day É—in. Suna zuwa mai make up É—in da Anisa ta É—auko ta kira ta a waya ta sanar da ita isowarta, mai aikinsu ta bawa umarnin zuwa ta shigo da ita sannan ta kalli Nanah tace.

   "Sis ga bathroom ki shiga ki fara yin wanka lokaci ya fara tafiya, don yanzu an kusa kammala yiwa Aunty Aimana make up na san." Bata yi musu ba duk da cewar tayi wanka a É—akin Mamu É—azu, bathroom É—in ta shiga wanda ta É“ata lokaci wurin Ć™are masa kallo da mamakin yanda aka tsara shi tamkar wani wurin kwalliya ba bayi ba. Kasancewar Mamu ta koya mata yanda ake amfani da abubuwan yasa kanta bai kulle ba tayi wankan tayi alwala ta fito tana goge gashi ta data wanke sabo da yana É—an damunta.

   "Masha Allah kina da gashi sosai Sis, amma sai dai ba kaya gyara shi kin bar shi ya sarĆ™e, yanzu dai lokaci ya Ć™ure ki É—an taimaka mata a gyara shi kafin gobe da safe muje ayi masa abinda ya dace." Anisa ta Ć™are maganar da bawa mai make up É—in umarni kafin ta shige bathroom É—in don yin wankan ita ma.

  Budurwar data É—auko don yi mata make up hair dryer ta É—auko ta busar da gashin Nanah ta shafa mata mayukan gashi masu kyau ta daure mata shi sabo da babu lokacin da za'a yi stretching É—in sa.

   "Kina buĆ™atar make up ne?." Ta tanbayi Nanah dai-dai lokacin da Anisa ta fito daga bathroom.

   "A'a bana son kwalliya ni dai." Ta bata amsa a taĆ™aice. Kallon ta Anisa tayi da murmushi tace.

   "No Sis ki bari ayi light zata yi maki kyau sosai." Ba don tana so ba ta bari aka yi mata light make up iya powder kwalli da lips gloss. Wani irin sihirtaccen kyau tayi wan da ya sa mai make up É—in da Anisa kasa daina kallonta.

  Lokacin data saka atamfar ankon É—inkin doguwar riga T buba sai ya zama kamar dama ita aka É—inka ma kayan kasancewata doguwa kuma marar jiki, atamfar tayi matuĆ™ar yi mata kyau kasancewarta mai duhu sai ta haska farar fatarta. SassauĆ™an É—auri ta soke mata wan da ya zauna É—as a saman kyakykyawar fuskarta yayi mata kyau, sarĆ™a da É—ankunne da siririn agogo Anisa ta bata ta saka ta bata Ć™aramin mayafin daya shiga da atamfar ta É—ora shi saman kanta tayi mata irin yafin da ake kira da Akuya style sabo da yanayin É—inkin jikinta. Subhanallah idan kaga yanda Nanah ta sauya gaba É—aya kai ba zaka taÉ“a cewa ita ce wannan wacce tayi rayuwa a Ć™auye cikin wahala ba.

   Tayi wani shahararren kyawu irin wanda ba zaka iya É—auke ido a kanta ba idan ka kalle ta.

   "Kai Sis kar fa ki cinye taron yau É—in nan don yan da kika yi kyan nan bana tunanin akwai wanda zai doke ki." Anisa ta faÉ—a tana murmushi lokacin da aka kammala shirya Nanah. Tattausan murmushi ta saki wanda ya Ć™awata fuskarta dai-dai lokacin da mai make up É—in ta haska ta d Camera, sai hoton ya zama na musamman yayi bala'in kyau.

   Kasancewar lokaci ya Ć™ure don tuni an fara gudanar da taron sabo da Ammy ta kira Anisa a waya don jin inda ta tsaya yasa aka yi maza aka shirya Anisa itama cikin irin atamfar Nanah wacce ba Ć™aramin kuÉ—i aka zuba wurin sayar ta ba. Tayi matuĆ™ar kyau itama kasancewarta kyakykyawar, hotuna aka yi musu kafin ta sallami mai make up É—in ta bawa Nanah plat shoes da bag mai kyau suka fice sunanta baza Ć™amshi.

   Lokacin da suka isa Hole É—in da ake gudanar da taron tuni shagali ya fara kan-kama amare suna zaune a wurin da ka tanadar musu, haka ma Iyaye da Ć´an'uwa sai Mc dake gudanar da taron. Wurin su Ammy suka fara zuwa suka gaishe su kafin suka nufi wurin amaren wan da a nan ne Nanah taga Aunty Aimanan Anisa suna matuĆ™ar kama da juna.

   A nan suka haÉ—e da sauran Ć´anmatan gidan wan da a nan Nanah taga su Nawal, su Ya Yusrah anci kwalliya ana ta iya yi, baki da hanci suka saki suna kallon Nanah don da farko basu gane ta ba kasancewar sun ganta da ankon Ć´an gidan. Kai gaba É—aya ma shigar dake jikinta babu abinda ya dace da nata, don haka nan take baĆ™in ciki da hassada ya motsa. Nihal ta fara zuwa in da suke tsaye da Anisa tana gaisawa da Ć™awayenta da suka zo mata.

   "Hi sis." Ta faÉ—a tana taÉ“o Anisa. Juyowa tayi ta kalle ta tace.

   "Hi ya kike." Ta juya ga Ć™awayenta. Haushi ya kamata don a ganinta Anisa ta wulaĆ™anta ta a gaban Nanah, don haka cike da jin haushi ta juyo wurin Nanah ta Ć™are mata kallo a wulaĆ™ance tace.

   "Ita kuma wanan baĆ™auyiyar yarinyar waye ya bata aron kaya har ta samu damar shiga cikin mutane take wani jiji da kai gaka?." Tayi tambayar cike da rainin wayo wan da ya janyo hankalin su Anisa dake kusa dasu, dariya Nawal ta sheĆ™e da ita tace.

   "Shish-shigi mana daga zuwa an fara maĆ™alewa Ć´an gida ana aron kaya don ayi Ć™arya, sai dai kuma a banza don baki ganta ba kayan da ban ita da ban don ba saba saka wa aka yi ba." Ta Ć™are maganar cike da hassada don ko ita kanta ta san Ć™arya ta faÉ—a. Mabaruka zata yi magana Anisa ta É—aga mata hannu rai a É“ace tace.

   "Ya isa haka dan Allah, waye yace aro tayi aka bata, ai itama Ć´ar gida ce kamar yanda kuke jin kuna da matsayi a gidan nan itama haka ne sabo da abu É—aya ya haÉ—a mu. Sannan maganar cewa kaya da ban ita da ban wannan Ć™arya ne kowa ya kalle ta ya san ita É—in mai kyau ce kuma kaya sun dace da ita sai dai mahassadi!." Ta Ć™are maganar rai É“ace tana makawa Nihal harara sabo da bata son wulaĆ™anci, ita dama can yaran basu yi mata ba sabo da sun cika rawar kan tsiya da shegen son nuna su wasu ne.

  "Sis ku muje don Allah kar raina yafi haka É“aci a wurin nan." Anisa ta kuma faÉ—a tana kama hannun Nanah suka wuce suka bar su Yusrah da baki a sake, baĆ™in ciki tamkar zai kashe su don ganin yan da Nanah ta samu shiga daga zuwanta ace har ta samu shiga a wurin Anisa wan da su da suka jima suna neman hakan basu samu ba, musamman Yusrah dake haukar son Muhammad take neman kusanci da Ć´an'uwansa tako wane hali.

   Wani wurin da ban suka samu suka zauna suna hirar su yayin da biki ke ci gaba da gudana, koda aka kira amare fili Iyayensu Mata na musu liki duk miĆ™ewa suka yi suna É—auka a waya bayan photo grapher dake aikinsa. Lokacin da aka buĆ™aci Ć™annen amare a fili Anisa ta kama hannun Nanah suka je wurin Ammy ta basu bundle É—in 1k sabbi kowa guda É—aya suka je suka yi liĆ™i wan da baĆ™in cikin hakan ya kama su Yusrah, ganin hakan yasa suka je suka matsawa iyayensu suma suka basu kuÉ—in suka shiga suka yi liĆ™in don dai kar su zama Ć´an kallo.

   Sai da aka kira sallar magrib kafin aka tashi a wurin taron cike da murna, har first gate Anisa da Nanah suka raka Ć™awayen Anisa da suke ta jan Nanah da hira don yarinyar tayi musu kyau sosai suna don ta haÉ—e dasu. A É“angaren Nanah kuwa ta kasa sake jiki sabo da rashin sabo da hakan, don ta saba da kyara da hantara daga wurin mutane bata saba da janta a jiki da nuna mata soyayya irin haka ba. A hanyar su ta koma wa ne Anisa ke bawa Nanah labarin Hammanta take sanar mata cewar gobe zai dawo daga London a can yake yin master's É—insa yama kusa kammala wa. Ita dai Nanah zata so taga wannan Yayan nata da ake ta zuzutawa, kamar Anisa ta shiga zuciyar Nanah tace.

   "Ai gobe muna da manyan baĆ™i domin basawan gidan zasu dawo Hammanah da Ya Ammar, kin san kaf a gidan nan an fi jin tsoronsu fiye da kowa, sabo da basa wasa da yara a kwai tsare gida musamman Hammanah. Amma fa duk da haka yana da kirki sosai sannan kuma yana matuĆ™ar ji dani. Ammy ta taÉ“a bani labarin cewar lokacin da yana Ć™aramin yaro yana da fara'a sosai tun da wani tsau-tsayi ya samu Aunty Amirah yayi sanadin rasuwarta shike nan ya sauya ya daina dariya da fara'a ya zama fuskarsa kullum a haka!." Ta Ć™are maganar fuskarta na sauyawa da alamar damuwa.

   "Wacece Aunty Amirah?." Nanah ta samu kanta da tambayar Anisa dai-dai lokacin da suka shiga cikin É—akin Anisa. Maimakon ta bata amsa sai cewa tayi.

   "Kin ga lokacin sallah zai wuce ki bari wani lokacin zan baki labari duk da dai nima labarin aka bani ban santa ba a zahiri sabo da lokacin da abin ya faru ba'a haife ni ba in ji Ammy. Anisa ta faÉ—a tana shigewa bayi sabo da fitsarin É—aya matse ta.

  A É“angaren Nanah kuwa haka kawai maganar ta tsaye mata a rai taji tana son jin labarin wan da ake kira da Muhammad É—in nan duk da cewa bata taÉ“a ganinsa ba......