SAWUN KEKE season 1

*🪻SAWUN KEKE...🪻*

by @auntyindo

Ep-4

Har ya sauka Æ™asa,  binsa  ta yi da kallo cikin tsananin tausayinsa, ji take da   da yadda za ta yi ta hana su tafi da shi da ta yi, Zahra ce ta Æ™araso wajen jiki a sanyaye, har ya fice daga makekiyar harabar makaranta idanunsu na kansa,  sun kasa ko da cewa Æ™ala.

Wajen da ƙoshashshen Dokinsa ke ɗaure ya nufa ba tare da ya bi takan Inspector Khalil ba, ganin haka ya sa Inspector Khalil cewa "Kai dakata min!! Kama ka fa mu ka zo yi amma ka ke shirim guduwa, kar ka wahalar da ni kasa in harbeka.
Kalaman nasa in da dama dariya Akhiee zai yi don kuwa sun fi kama da haka, sai dai dariyar haÉ—ari ce gareshi, ya kalleshi ya kauda kai sannan ya buÉ—i baki cikin nutsatstsiyar muryarsa ya ce "Ba zan hau muku mota ba, ka barni zan je akan dokina."
Fakam-fakam Inspector Khalil ya yo kansa a fusace  ya na cewa "Mu za ka rainawa hankali?  ya za mu kama tantirin É—an ta'adda irinka  amma sabida ka maida mu masu Æ™waÆ™walwar yara sai ka ce za ka tafi a doki??"
Cikin sigar lumana ya ƙara cewa "Ba na son ku cutu ne shi yasa ba zan hau motarku ba!"
Inspector Khalil  ya Æ™ara hayayyaÆ™owa  kamar zai doki Akhiee, jin suna taÆ™addama ya sa Sheikh Auwal matsowa gurin, fuskar sa ba alamun wasa ya ce ''Ba su san hatsabibancinka bane da ka ke tunanin su barka ka tafi kai kaÉ—ai? wuce ka shiga ko ranka ya É“aci." 

Cikin kurari  Inspector Khalili ya ce "Bar ni da shi Ya Sheikh, sai na nuna masa bambancin É—an sanda da É—an ta'adda."
Duk wannan kurarin da Inspector ya ke yi  damisar takarda ce kawai don a gaskiyance tsoron ma kallon fuskar Akhiee yake a wannan lokacin bare har ya je daf da shi hakan ne ya sa ma ya basar da labarin handcuff.

Akhiee  ba tare da ya ce komai ba ya koma ya shiga motar Ƴan Sandan hankali kwance.
Sheikh Auwal ne ya dubi Inspector Khalil cikin ɓacin ran abinda ɗan uwan nasa ya aikata ya ce "Ba na so ku sake shi har sai kun hukunta shi a bisa laifinsa, kar ku biyewa son Zuciyarsa ku barshi ya dawo ba tare da kun ƙwatowa wanda aka cuta haƙƙinsa."
Inspector Khalil ya shaƙi iskar da ke kaɗawa ya busar sannan ya ce "Calm down Ya Sheikh! hakan fa aikina ne, don hakan na kama shi."
Da haka su ka yi sallama, Inspector ya shiga mota  zuciyarsa fari Æ™al kamar anyi masa Albishir da Aljannah.

ƘoÆ™arin kunna motar direba yake amma ina ta ce ba ta san zance ba  ko motsi ba ta yi da sunan ta na da rai,  abun kamar wasa mota ta Æ™i ko da harbawa sau É—aya har an kwashi lokaci me tsayi ana ta fama, Inspector Khalil sai kai kawo ya ke yi  hankalinsa duk ya tashi ya rasa yadda zaiyi  ga jama'a da su ka taru domin kallo sai dariya su ke masa,  zuwa yanzu ya fahimci cewa Akhiee ne matsalar motar don haka ya lallaÉ“a kusa da shi, cikin muryar raÉ—a ya ce "Muhammad  ka sauka to ka hau dokin naka ka ga  motar  ta lalace mu ma tawo daga baya  amma don Allah kar ka gudu kawai tambayoyi zan yi maka  ba wani abu ba."   cikin zuciyarsa mugun Æ™uduri ne akan Akhiee kawai ya faÉ—i  hakan ne a ganinsa ya lallaÉ“a shi zai fi zuwa.

cikin ko in kula Akhiee ya ce "Ƙaramin Sufeto, ka je ka canja shiri ka zo ka same ni a Office É—inka na riga na yi niyar zuwa so zan je ba sai ka yi min Æ™arya ba,  kuma ina so ka sani ba a shiga dawa don Æ™arya."

Ya na gama faÉ—en haka ya dire ya bar Inspector da buÉ—aÉ—É—en baki ya na kallonsa.
Bai saurari kowa ba ya haye dokinsa ya zabure shi.
Inspector Khalil  a tunaninsa  Akhiee ya na sauka daga motar za ta dawo daidai  sai ya ga saÉ“anin haka,  yanzu ya tabbata motar ta riga ta mutu kenan don haka hankalinsa ya  kai Æ™ololuwar tashi,   abubuwa da dama ya Æ™udurce a ransa wanda zai yiwa Akhiee don ya huce baÆ™in cikin abinda ya yi musu.
Wurin su Sheikh Auwal ya koma ya nemi alfarmar su kai shi Office da motarsu,  ba su yi masa gardama ba  su ka amince masa.

Sai da akuyar cikinsa ta juya da ya yi alaragab da Rislaan zaune kan kujerarsa ya É—ora Æ™afa kan teburin gaban kujerar    ya na zuÆ™ar murzazzar wiwinsa,  baki sake ya ke kallonsa  tare da shuÉ—awa duniyar tunani.

Wayarsa ce ta dawo da shi haiyacinsa  ya yi saurin É—auka, a É—aya É“angare Corporal Halil  ya ce "Sir!  yanzu mu ka kammala da gawar nan mun tafi hanyar maida ita gida".
"Wane bayanai aka samu akai??"
"To gaskiya dai ba wata hujja illa iyaka dai rauni ne na wuƙa ba wani abu, sai kuma cewar tin daren jiya ne abin ya faru."
Katse watar ya yi cike da takaici ya soketa kana ya Æ™arasa cikin ofishin  ya na takun isa da Æ™asaita,  cikin sigar wulaÆ™anci da Æ™asÆ™antarwa ya ce "Ka zo ka miÆ™e Æ™afa a teburina kamar na tsohonka, office É—in nan fa ba gidan manyanka bane da za ka zo ka na min shaye-shaye a ciki,  ka na Æ™azami da kai ma har ka isa ka zauna kan kujerata?  ka sauka ko kuma na yi maka abinda zaman ma sai ya gagareka."
Yadda dutse ba ya magana haka Akhiee bai ce komai ba hasalima ko motsi bai yi ba.

Inspector Khalili ya dinga maganganu amma hakan bai sa Akhiee ya yi ko É—ar ba,  gajiya ya yi ya nemi guri ya zauna ya na nazarin ta inda zai É“ullowa lamarin.

"Yanzu ka tsaya mu yi magana, dole kai ne ka kashe  Alhaji Salisu don  kai ne ka gana da shi a daren jiya.
"Don na gana da shi ba shi ya ke nufin ni zan tsara masa ƙaddararsa ba.
"Kar ka yi min zancen banza, kawai ka amsa laifinka ba sai ka wahalar da hukuma ba, ko ka na nufin ka ce ba kai ne baƙonsa na jiyan ba?"
Jan hayaÆ™insa ya yi ya busar cikin salo sannan ya ce "Na baÆ™unce shi jiya, kuma ni na fara yi masa Albishir da mutuwarsa,   amma don ance maka a daren jiya aka yi kar ka yi tunanin irin 12:00am É—innan, No daidai lokacin da ruwan sama ya sakko aka shiga gidan  ana tsaka da ruwa kuma  ruhinsa ya bar jikinsa,   na so na ceceshi sai dai kashhh!  bai yi min abinda ya dace ba  shi yasa na bari ya mutu,  Ƙaramin Sufeto  ka Æ™ara bugu don ba ka buga a daidai ba."
Zuciyar Inspector Khalil tsalle kawai take yi kamar za ta É“alle Æ™irjinsa ta fito sabida É“acin rai, 
"Wannan gadarar taka da rainin hankali za ta jefaka a matsala, bayan duk wannan ka na nufin in yarda ba kai ka kashe shi ba?  ka faÉ—a min gaskiya kai ka kashe shi ko??  sai fa ka amsa mini sannan za ka samu hutu daga gareni  in ba haka ba ka shiga uku da ni.
Banza Akhiee ya yi masa ya ci gaba da zuÆ™e-zuÆ™ensa  sai da ya gama zamansa akan kujerar Inspector Khali kana ya tashi ya na cewa "Haka ake kama mai laifin ba ko handcuff?"
Sai a lokacin ma Inspector ya tuna da hakan,  ya fara cika bakin cewa "Ai so nake na bika ta maslaha  shiyasa nake maka tambayoyi cikin lumana, amma tinda abin naka ya zo da haka dole ne  ai na rufeka, me ka ke ci na baka na zuba?"
Ko kanzil Akhies bai ce masa ba.

Tin safe har Azhar ta doso Inspector  Khalil na  famar tambayar Akhiee amma shiru ba amsa, duk wata barazana da zai yi ya yi amma shiru.
Wayarsa ce ta fara ruri  a Æ™agauce ya janyota gami da É—aga kiran ba tare da ya duba me kiran ba.
"Waye ya sa ka kama wannan?  ya ka ke abu  kamar ba ka san abinda ka ke yi ba?  yanzu ka na da  hujjar da za ka nuna wa duniya ta shaida shine ya aikata?"
Cikin girmamawa Inspector Khalil ya ce "Sorry sir, amma alamu ne su ka nuna shi ya aikata don kuwa shine ƙarshen ganawa da Alhaji Salisu."
a ɗaya ɓangaren ya ce "Wannan rashin lissafi ne irin naka, maza ka sake shi sannan ka ba shi haƙuri, in ba ka yi hakan ba kuma zan cire hannuna daga ciki ko me ya faru kai ka jawa kanka"
"Okay Sir!!!"   bai Æ™ara magana ba ya katse kiran, Inspector Kalil ya bi wayar da kallo ya na mamakin hakan.

"YallaÉ“ai me ya faru? waye ya kira?"  Constable Saleh ya jefo masa tambayoyin a jere.
Cike da tsoro gami da shakka ya ce "Abin mamaki kira ne daga CP  da kansa  wai na saki wancan É—an ta'addar."
Constable Saleh ya ce ''YallaÉ“ai dama na gaya maka ko wuni ba lallai ya yi a hannunka ba bare kwana, na gaya maka  dabi da wancan shaiÉ—an É—in haÉ—ari ne, nan gaba ma za ka iya ganin takardar kora daga aiki ko ta canjin wurin aiki."
Cikin É—aurewar kai Inspector Khalil ya ce "Anya ba shi ka ke yiwa aiki ba Constable? na ga sai faÉ—a min kausasan kalamai ka ke yi akansa."  cikin sauri Constable Saleh ya ce "YallaÉ“ai wallahi ka ji na yi rantsuwa ta muslmi ba na yi masa aiki ban taÉ“a karÉ“ar kuÉ—in wani na yi masa aiki ba, YallaÉ“ai ka tuna da iyalina kar ka sa aikina ya lalace ba ni da hanyar samu sai wannan,  kawai anyi a gaban idona ne ba sau É—aya ba     ba sau biyu ba shiyasa na shaida kuma na ke baka labari YallaÉ“ai."

IP Khalil ya koma ya zauna jaÉ“ar gami da furzar da zazzafar iska, "Ku sake shi!"  ya faÉ—a kamar zai fashe da kuka don takaici.

ya na bada umarni su ka buÉ—e Akhiee, ya kakkaÉ“e jikinsa ya tashi, wurin  Inspector ya nufa ya tsaya akansa sannan ya ce "Kai Æ™aramin Sufeto, idan ka ce uwarka Madam ce  to mu haÉ—u a Coci, ina son ganinta."
Daga haka ya juya, har ya fice  Idanun IP Khalil na kansa,   dogon tsaki ya zabga  gami da dukan teburibÉ“n gabansa ya miÆ™e kamar wanda aka cakawa Allura.

"Ya  Zama dole ma na san da abinda ya ke taÆ™ama Yaron nan, ya zama dole na gane dalilin da ya sa CP ya ce na sake shi"  wannan lissafin IP Khalil ya ke yi cike da É“acin rai.

Akhiee  kuwa tuni ya É“ata a wurin ya san inda dare ya yi masa.

Baya

Cikin sauri sauri Alhaji Salisu ya shigo Falon,, a kusa da Hajiya Laure ya zauna sannan ya ce "Hajiyata na yi baÆ™o za mu tattauna da shi, to kar ki shigo part É—ina  har sai na dawo na same ki"
"To sabida me Alhaji?" 
"Kar ki tsananta bincike don Allah  kawai ki yi abinda na ce"
"To shikenan Alhajina ka dawo da wuri" 
Hajiya  Laure ta faÉ—a ta na kwarkwasa.

gaba ya yi ya na cewa "In sha Allahu"
Akhiee na zaune Æ™afarsa É—aya kan É—aya Alhaji Salisu ya shigo da sallama, bai amsa ba  har ya Æ™araso ya zauna kan kujerar da ke fuskantar wadda Rislaan ya ke kai......