DUHUN DARE

PAGE 59

by @oumameer2671

D U H U N D A R E

A 2026 N O V E L

BOOK ONE

ADABI WRITER'S ASSOCIATION

AMEENA IBRAHEEM

OUM-AMEER

Arewapen: @Oumameer2671

Wattpad: @Ummu-Amir

BOOK ONE

PAGE 59

Wani irin shiru ne ya ci gaba da ratsa ɗakin na tsawon lokaci. Numfashi ma sai ya zama kamar ana jin sa a sarari tsabar yanda kowa ya nutsu yana nazari akan waɗan nan maganganu na Abiyh.

Maheer ya tsaya cak, idanunsa ƙyam akan Abiyh yana mai ƙoƙarin fahimtar shin anya da gaske kuwa yake yi ko ko dai mafarki ne.

"Grandpa…?"

ya furta a hankali muryarsa har tana  cracking, ƙoƙarin yake ya furta masa kalmar A'a amma kuma ya kasa hakan.

"Ameeduddeen Na faɗi abinda na yanke tun kusan shekaru biyu da suka wuce. I waited for the whole 2years Ko zai kawo wata yarinyar da ya ji yana so ya aura, but har yau babu wani labari, hakan yasa a yau na yanke wannan hukunci. Babu wanda yasan gobe sai Allah, ta yi yu ba zan kai gobe ba..."

Nan take ya ji zuciyar sa ta sake bugawa a karo na barkatai. Nazlin ce zai aura a yau? Aure dai sai ka ce wani abun wasan yara? Daga can wani ɓangare na zuciyar shi kuma yaji yana tunasar da shi cewa Kana da mata...Maryam ɗinka, farin cikin ka, you promised her alot kada ka amince da wannan auren domin hakan zai rusa tsakaninku.

Miƙewa suka ga ya yi da sauri yay excusing kansa ya fice daga parlourn ya koma bakin ƙofa tare da ɗora hannayensa akan wani ƙaramin pillar dake zagaye da wasu kyakkyawan flowers ya dafe kansa.

Cikin zafin nama Maami ta tashi ta bi bayansa. Bai ji time ɗinda ta zo wurin ba, sai saukar muryanta da ya ji ta ambaci sunan sa a hankali.

Waigowa ya yi idanunsa cike da tashin hankali ya riƙo duka hannayenta a diririce ya ce.

"Maami..."

Itama cikin tsananin mamakin irin wannan ruɗewa da taga ya yi ta katse shi mishi hanzari da faɗin.

"Wai miye kake haka Maheer? Miye matsalarka?"

"Maami please talk to him..Nazli fa Maami? Maami please ni bana son wannan auren..."

"Okay.."

Ta ambata tana mai jinjina kanta ranta na yi mata babu daɗi. She thought cewa zai karɓi wannan maganan with single minded. She thought har abada ba zai iya ja da umarnin Abiyh ba kowane iri ne a rayuwar nan. Miye matsalan Nazli? Nazlin ce baya so ko kuma dai auren ne baya so?

"Ina so ka faɗamin one single reason da yasa ka ƙin wannan auren?"

Kai tsaye ya runtse idanunsa tare da girgiza kansa ya ce.

"Nazli Maami..."

"Na ji, Miye matsalanta?"

Shiru ya yi tamkar ruwa sun cinyesa ya haɗiye sauran maganansa domin yasan cewa Nazli ba ta da wata matsala.

Muryan Maamin ya ji softly tana faɗin.

"Nazli tana da duk wasu qualities ɗinda ake buƙata wurin auren mace ta gari Maheer. Tana da ilmi na addini da na zamani,tana da tarbiyya, tana da wayewa, ta iya girki,tana da kyau  and....abu mafi muhimmanci shi ne kun fito daga family ɗaya, ka san ta ka san iyayenta ba ka da wata fargaba. Maheer ba kawai mata nake so maka ba, ina so maka Uwa mai nagarta ga yaranka, ina so maka bangon jingina a duk lokacin da ka gagara tsayuwa, ina so maka hasken da zai zamto marar gushewa a cikin gidanka."

"Maami Nazli tana da girman kai da jiji da kai, tana da alfahari da jin cewa ita ɗin wata ce. Zamu iya shekara without talking to each other because tana da wani hali na jin cewa ita ɗin kaman ta fi kowa..."

Hannunshi ta ƙara jimƙewa tare da ƙara sassauta murya tana kallon fuskar sa ta ce.

"Maheer...kada ka manta fa ita ɗin mahaifiyarta daga gidan sarauta ta fito! Akwai wannan jinin mulkin da yake gudana a cikin jinin ta da yasa take acting haka. A duniya kowane mutum yana da irin nature ɗinsa da kuma halayyarsa. Ita ɗin mace ce kai kuma namiji, kai ne wanda yake da makullin ƙulla kyakkyawan alaƙa a tsakaninku. Nazli mace ce da ta cancanci a so ta sannan duk wanda ya same ta ya cancanci ayi masa barka. Ita ce Mace amma kuma bata musa da wannan umarnin na kakanta ba, mahaifinta ma bai musa daga umarnin mahaifinsa ba, dan Allah ina roƙonka kada ka kunyata ni a wannan maganan, yanda suka karɓa hannu biyu kai ma ka karɓa ka yi addu'ar mafi alheri a tsakanin ku. Idan har kace ka juya baya to ni ɗin nan ni ka tozarta a cikin dangina ba kowa ba. Ka tuna kana da dangin mahaifi amma kuma nawa dangin su ne suka yi maka komai tun kana ƙarami har zuwa yau, please kada kace za ka yi musu butulci. Idan na isa da kai to ina so ka amshi wannan auren kuma ka tsaya a ɗaura shi a yau. "

Tana gama faɗin haka ta juya ta koma ciki. Ɗakin sa dake gidan yaje ya shige tare da faɗawa kan makeken gadon sa yana jin yanda kalaman mahaifiyarsa ke amsa kuwwa a cikin kunnuwansa. Ta riga ta gama ɗaure shi da igiyar da komai rashin hankalinsa dole ya tsaya ya saurare ta. Wannan wace iriyar bahaguwar ƙaddara ce ta sake shigowa rayuwarsa? Bai gama da matsalan Maryam ba ga shi ya sake faɗowa cikin wani tarkon da bai san yanda zai yi ya fita ba. Miye abinda zai faɗawa Matar sa Maryam wacce ta kasance fitila kuma hasken rayuwarsa a yanxu.?

A gefe guda kuma…

Nazli gabaɗaya lokaci guda ta nemi nutsuwarta ta rasa. Anya Abiyh ya san abinda yake faɗa kuwa? Kodai zafin ciwo ne ya ruɗasa? Ita fa tana da wanda take so ba Maheer ba. Ko kaɗan tsarin rayuwarta da rayuwar sa ba su yi kama da juna ba. Magana wannan idan za su haɗu sau goma bai fi su gaisa sau ɗaya ba. Ta kan ji shi da su Zarah suna fira idan ya so wanda ko shi sai can baka rasa ba. Yanzu ta ya za'a aura mata wannan mutumin sai ka ce ta rasa mai son ta? Gaskiya Abiyh bai duba mata ba. Girman ajinta da alfaharinta sun ƙarfin wannan wulaƙancin da Abiyh ya yi mata.

Muryar mahaifinta ta ji yana faɗin.

"Hakan da kayi shi ne daidai Abiyh, kuma mun yi matuƙar farin ciki. Maheer da Nazli dukkan su abu ɗaya ne, Allah yasa wa wannan aure da za'a ɗaura albarka ya basu zaman lafiya."

Cikin farin ciki Uncle Abdallah da Uncle Ibrahim suka amsa da Amin because ba su yi expecting ba. Sun ɗauka Uncle Ameed zai nuna rashin amincewa domin shi ne yake da ɗan tsauri wani lokaci, but unfortunately sai ga shi ya amince kai tsaye cike da zallar farin ciki.

Nan take abu kamar wasa suka tara mutane wanda duk su ne familyn da kuma familyn mahaifiyar Nazlin domin suna girmama Abiyh suna jin maganar sa. Duk yanda Nazli ta so ta kasa gardamawa Umarnin Abiyh ɗin duk da cewa mahaifiyarta itama bata amince ba kawai dai iyayenta ne da 'yan uwanta suka dakatar da ita amma ba don ranta ya so ba.

Ba za ta ce tana ƙin Maheer ba kai tsaye because ya kai kowane irin namiji da ya cancanci a so shi sai dai babu soyayya kuma ta san babu wata kyakkyawar alaƙa a tsakanin su and again she will never bow on him Wai da sunan biyayya matuƙar yace zai nuna mata rashin daraja a gidan auren na su. Auren ma da take gani kamar almara kaman wasa kaman kuma mafarki. But tana jin cewa wai da gaske an ɗaura kawai ta fashe da wani irin kuka na tashin hankali da rashin makama.

Arwah da ke tsaye a gefen ta ne ta kalle ta cike da tausayi ta ce.

"I'm sorry sis..."

Cike da wani irin baƙin ciki ta miƙe tsaye jikinta har yana wani irin ɓari ta kalli Arwah ɗin murya cike da kuka ta ce.

"Arwah da gaske ne Abiyh bai ga wacce zai tozarta ya zubar mata da mutunci da irin wannan auren ba sai ni? Sai ka ce ya samu wata ɗiyar Baby? I swear...."

Saurin haɗiye maganar ta yi bayan sun yi ido biyu da mahaifinta.

A hankali Arwah ta janye jiki ta sulale ta yi waje.

Hannun ta Uncle Ameed ya riƙo wanda hakan yasa ta ɗago kanta ta kalle shi. Murya cike da ƙwarin gwiwa ya ce.

"Mahaifina shi ne gaba da komai a rayuwata Nazli, yi masa biyayya ya zamemin dole, and kema yi masa biyayya ya zama dole a gare ki. Na yarda da zaɓin da ya yi miki domin kin samu miji wanda ya dace dake. Da bai cancanta ba Abiyh ba zai taɓa aura masa ke ba. Lailah uwa ɗaya uba ɗaya muke, Maheer kuma ɗan ta ne, kaman yanda kike ke ɗaya tilo a garemu shi ma haka yake ɗaya tilo a wurinta. Zumuncinmu ɗaurarre ne wanda muke da cikakkiyar amana da yarda a tsakaninmu, kada ki bari a samu matsala daga ɓangaren ki domin ba zan taɓa yafe miki ba."

Yana gama faɗin haka ya fice fuu daga ɗakin wanda a hanya ya yi kiciɓis da mahaifiyarta, wani kallon ya yi mata sannan ya ce.

" Rumana kada ki ce za ki turza yarinyar nan kisa ta bijirewa wannan auren. Idan har aka samu wata matsala tabbas ba zan ƙyale ki ba."

A hankali mahaifiyarta ta taka ta shige ɗakin ba tare da ta furta masa komai ba, hannayenta ta kai ta yi curving kyakkyawar fuskanta ta juyota idanun su suka sarƙafe sannan ta jinjina mata kanta ta ce.

"Nazli ko kaɗan ban yi farin ciki da irin wannan auren da aka yi miki na nuna fin ƙarfi ba, a matsayin ki na 'ya ɗaya da nike da ita ace wai auren ki ne ya ƙare a haka dole nayi baƙin ciki. Kuma ki kwantar da hankalinki, in sha Allahu muddin naga alamar cewa za ki cuta ni ba zan zuba ido ina kallo ba, matuƙar na ga cewa bai amshe ki hannu biyu ba ni kuma ba zan ji fargabar neman a raba auren ba domin farin cikin ki ya fiye min komai a duniya duk abinda zai faru sai dai ya faru. Iyaye na sun riga sun amince kuma sun gargarɗeni akan kada na ce zan nuna rashin amincewa, hakan yasa kika ga dole na yi shiru Nazli, amma wallahy tallahy duk naga wani abunda ban yarda da shi ba daga wurin shi to dole a raba auren nan ko sun ƙi ko sun so."

*******

Zaune yake a jirgi amma gabaɗaya hankalinsa baya jikin sa. Ana gama ɗaura auren ko kallon cikin gidan bai ƙara yi ba kawai ya fito ya wuce abinsa. Har yanxu jin komai yake kaman a mafarki domin babu yanda za'a ƙirƙiri maganar aure cikin mintuna sannan kafin 2hours cikakku su cika ace har an ɗaura kaman wani wasan yara.

Maami ba ta san irin halin da yake ciki ba da ko ance ta karɓi wannan auren ba za ta yi ba. Ya so ya kauce, ya so ya ƙi amincewa amma damar hakan ba ta samu ba, domin ta bi duk wata hanyar da za ta bi domin hana shi magana wanda sai da ta yi nasara sannan hankalin ta ya kwanta. Akwai abubuwa a ransa waɗanda yake neman mafita da su, yaso ace duk abunda ya ɗebo ya tsaya tsakaninsa da mahaifiyarsa ne kaɗai. But yanzu abubuwan da yake fuskanta sun dulmiyo wasu mutane a ciki waɗanda yake hango babbar ɓaraka da za ta janyo rugujewar ahlin mahaifiyar tasa baki ɗaya.

Idan suka ji abinda ya aikata sannan ga auren Nazli da yake kansa a yanxu bai san yanda abubuwan za su kasance ba.

And again Maryam! Ya zai yi da maryam kenan? Mahaifiyarsa da dangin ta gabaɗaya sun san cewa mahaifinta ne ya kashe masa mahaifinsa. And ita kuma She is always thinking of cewa ba da gaske yake sonta ba. A lokuta da dama tana yawan faɗa mishi cewa ita ɗin tasan cewa ba ta kai a kira ta da matar shi ba domin zubi da tsarin rayuwarsu sun bambanta, dole akwai wata wacce yake da wacce ta fita komai wanda watarana zai aure ta ita kuma ya nemi rabuwa da ita.

"Yah Allah!"

Abunda ya furta kenan tare da runtse idanunsa jin wani irin sabon tashin hankalin da ya sake mamaye masa zuciya.

Babu abinda bai zo masa a rai ba har ya sauka garin Abuja wanda duk juyin duniya idan ya yi sai fuskar Anaam ta zo masa a tunanin sa.

Bai ƙara jin tashin hankali ba sai da ya shiga gidan ya ga ta taso cike da farin ciki ta rungumesa a hankali ta kai bakinta saitin kunnen sa kaman yanda yake yi mata ta ce.

"Welcome Babe. Your Maryam misses you so much..."

Ɗagota ya yi ya kalle ta cikin idanun ta yana mai jin yanda zuciyarsa ta karye ganin irin farin cikin da take ciki da ganin sa. Hakan yasa ya sake saka hannayensa ya rungumeta gam a jikinsa tamkar wanda zai maida ta ciki.

Jin kaman jikin shi da zafi yasa ta janye hankalinta a tashe tana kallon sa ta ce.

"Are you sick? Na Ji kaman jikinka da zafi..."

Ta ƙarashe maganan tana mai kai hannun ta akan forehead ɗinsa zuwa wuyansa.

Hannunsa ta ja suka shige ciki ta zaunar da shi akan kujera sannan ta je kitchen ta haɗo mai Tea only ta kawo. Hannu ya miƙa ya karɓa har yanzu ba tare da ya yi magana ba.

Tana ganin ya shanye ta ja shi zuwa ɗakin shi da kanta ta rage mai kayan jikinsa abun da bata taɓa attempting yi ba tun farkon auren su har zuwa yau, sai ga shi kanta tsaye ta aikata tare da jansa cikin toilet ta bar shi ta fito.

Koda ya fito ta ciro masa wasu lallausan sleeping dress na cotton sannan da kanta ta taimaka masa ya saka wanda gabaɗaya ya ji lokaci ɗaya ta ruɗar da shi.

Towel ɗinda ya cire ta ɗauke da nufin kai wa ta yi hanging kawai ta ji ya riƙo hannunta ta faɗo jikin shi ya sake rungumeta sosai kaman ɗaxu da ya iso.

Shiru ta yi tare da kwantar da kai a ƙirjinsa na dogon lokaci wanda daga ƙarshe ta ɗago ta kalli cikin idanuwansa da suka gama rinewa tsabar damuwa hankalinta a tashe ta ce.

"Babe...miye yake damunka?"

Tamkar zai fashe da kuka ya ce.

"Komai ma damuna yake Noori! I'm not okay.."

Ganin ta yi ya kamo hannunta ya riƙe yana mai bin ta da wani irin karyayyen kallo ya ce.

"Please ki yi min alƙawarin cewa komai zai faru ba za ki bar ni ba..."

Ido ta zuba tana kallon sa tare da nazarin irin halin da yake ciki. Definitely he's not okay kaman Yanda ya faɗa. Gabaɗaya baya cikin nutsuwarsa, fuskansa da idanunsa sun nuna damuwa wanda ita kanta a yanzu ta gama fahimtar hakan.

"Noori...."

Lumshe idanun ta tayi ta buɗe a hankali tana kallon shi jin yanda kalmomin sunan suka daki har tsakiyan kanta. kallon shi take kaman yanda yake kallonta softly ya ce.

"Do you love me?"

Jinjina kanta ta yi alamar eh wanda da gaske take ta amsa har cikin zuciyarta cewa tana son shi.

"Ki faɗamin in ji da kunnena Noori ki faɗamin domin zuciyata ta ji cewa kin amsa ke ma kina so na kina ƙauna ta kaman yanda nima nake son ki. Kunnuwana su na so su ji yanda kike ji game dani..."

A hankali ta kai cute lips ɗin nan na ta da ba sa rabo da ƙyalli ta haɗe bakin su wuri ɗaya ta shiga kissing ɗin shi romantically. Gabaɗaya ji tayi dukkan wata jijiya dake jikinta ta amsa tare da gaɓɓan jikinta jin irin kalaman da yake furta mata. She is burning in love a yau domin kalamansa sun shiga kowace gaɓa ta jikinta ba kaɗan ba.

Cikin wata irin zazzafar ƙauna ta shiga sarrafa kanta daga lips ɗinsa zuwa wuyansa kaman yanda yake rikita ta idan ya tashi. Ta sani cewa ita ce wacce ta katange shi da cika sunnar su ta aure domin ganin take kaman ba za ta iya ba. Gani take kaman za ta cutu hakan yasa take jin tsoro kuma take ta ƙoƙarin hana masa Kanta wanda har yau bai taɓa yi mata complain ba ko ya nuna mata cewa ran shi ya ɓaci. Lokaci ɗaya ta shiga unbuttoning ɗin yaloluwar rigarta da ke da wasu maɓallai guda uku a gaba waɗanda da su da babu su duk ɗaya. Tana gama zare buttons ɗin ta sake manna jikinta da na shi tare da kai lips ɗinta ta sake locking bakinsu wuri ɗaya.

Gabaɗaya ta gama rikita shi ta gama ruɗar da shi. Wani irin shock yake ji wanda ke shigar sa tun daga tsakiyan kansa har zuwa tafin ƙafar sa. Wata irin wuta yake ji tana ci ko'ina na jikinsa ta yanda duk yanda ya so ba zai iya hana kan shi ba a yau.

Lokaci ɗaya suka faɗa kan makeken Bed ɗin nasa wanda ya yi mata rumfa yayin da idanunsa suka sauka akan tsayayyun breast ɗinta wanda komai ya zo masa a ba za ta.

Ya kiɗime, ya ruɗe ya gigice gabaɗaya ya fice daga hayyacinsa. Ba wannan ne buƙatansa ba a yanzu. Amma kuma ta riga ta zurma shi, ta riga ta kwance masa notukan da bai isa yace zai ɗaure kansa ba.

Itama ɗin she's just doing it Saboda Kawai ta bashi comfort na irin damuwa da tashin hankalin da ta ganshi a ciki. A yau ta miƙa masa wuya domin ta bashi tabbaci akan cewa ta amsa kalamansa kaman yanda shi ma ya amshe ta da hannu biyu. So take a yau ta mayar da shi namiji kamar sauran mazajen da suka yi aure kaman shi. Ta sani cewa ba za ta iya bashi ɗa ba, amma kuma duniyar nan da kowane namiji yake mafarki da burin kasancewa a duk lokacin da ya ji ransa ya amsa nan take so ta samar masa mafaka ta har abada. A yau ta sadaƙar ta kuma yarda har cikin zuciyarta cewa duk zafi, duk raɗaɗi za ta jure domin kawai ta ba shi haƙƙin sa da ya rataya akan wuyanta. Da hakan ta kafe zuciyarta tare da runtse idanun ta ta yi shiru tana jin yanda yake sarrafa kowace irin gaɓa ta jikinta.

Daren ta na yau ya bambanta da wancan daren da ya kasance mummunan dare a gare ta. Domin yau cikin ɗakin aurenta take tare da Mijinta wanda yake taɓa ta a hankali tamkar yana taɓa ƙwai sabanin wancan lokacin da ta shiga azabtuwa tamkar wanda ya samu dabba.

Komai haka ta shiga jinsa kaman a mafarki wanda ba ta ji ta raina kanta ba sai da ta ji ya yi addu'a ya ɗauki hanya. Ruɗewa ta yi gabaɗaya ta shiga ture sa amma kuma ta riga ta makara domin gabaɗaya ya fice daga hayyacinsa abin kawai ya ke ji da gani.

"Babe..please stop...."

" Relax kin ji Noori tah! Ki dai na jin tsoro kin ji, ba zan cutar da ke ba, ba zan yi miki da zafi ba I promise...idan har wani abu ya same ki har abada ba zan yafewa kai na ba..."

Cike da soyyaya da tausayawa ya tafiyar da wannan daren na su cikin wata irin zazzafar ƙauna mai tsaya a rai.

Bambancin da ta ji daga waccan ranar zuwa wannan shi ma haka ya ji. Wancan ke ta haddi ne ba bisa yarda ba wanda a wancan ranar gabaɗaya baya cikin hayyacinsa saɓanin yau da ita ce ta amince masa kuma da yarda ta kamar yanda yake cikin hayyacinsa shi ma.

Kukanta yake ji can ƙasan zuciyarshi tamkar ana watsa masa ruwan zafi, hakan yasa ya rungumota tare da sake jan Duvet ya rufa su da shi. A hankali ya kai yatsanshi ya shiga goge hawayenta tare da saka ɗayan hannun yana bubbuga bayan ta a hankali alamar rarrashi sannan daga ƙarshe ya buɗe bakinsa muryar nan a narke ya ce.

"I'm sorry mah Noori."

Fuskanta ta kai a hankali ta goga akan faffaɗan ƙirjinshi ta share hawayenta sannan ta kwanta luf tare da ƙara ƙanƙame shi tana sauke ajiyan zuciya.

A hankali ya ji yanayin numfashinta ya shiga sauyawa wanda hakan shi ne ya tabbatar masa da cewa bacci ta yi.

Lumshe idanunsa ya yi a hankali ya buɗe yana mai jin yanda komai ya shiga dawo masa bit by bit. Ji yake komai kamar ya na yi masa tamkar a mafarki, maryam ce ta sakar masa jikinta tare da ba shi yarda akan ya tara da ita a matsayin domin su kasance abu ɗaya. Ya nemi kalaman soyyayarta da baki ita kuma ta gamsar da shi da ruhi da gangar jikinta. Haƙiƙa ta riga ta gama masa komai a rayuwa wanda yanzu yake ji duk abinda zai faru ba zai taɓa iya rabuwa da ita ba.

Ya ɗauki tsayin dare yana ta tunani kala-kala wanda daga ƙarshe ya janyo wayarsa ya duba time. Ƙarfe huɗu saura minti bakwai abinda agogon wayarsa ya nuna masa kenan.

A hankali ya zame ta zuwa lallausan pillow ɗinda yake kai sannan ya ƙara lulluɓe ta da kyau ya sauka ya shige toilet ya yi wanka ya fito ya shirya cikin jalabiya ya shimfiɗa sallaya ya hau jera nafila yana addu'ar mafi alheri da kuma Alkairan da ke cikin auren gabaɗaya. Fatansa da addu'arsa shi ne duk abin da zai je ya dawo ta fahimcesa, matukar ta amince da shi to duk wani tashin hankalin da zai riske sa mai sauƙi ne.

Haka ya jima akan sallayar wanda duk wani motsinta akan idon har aka gama kiran sallahr asuba.

Stroking ƙafanta ya shiga yi a hankali yana hura mata iska a ido zuwa cikin kunnen ta.

A hankali ta buɗe idanunta waɗanda suka gama yi mata nauyi tsabar kukan da ta sha ta kalle shi sai kuma ta kawar da kanta.

Ji ta yi ya tallafo ta gabaɗaya sannan ya zare Duvet ɗinda ke lulluɓe da ita ya shige toilet da ita. Kawar da kanta tayi tare da saka hannayenta ta kare ƙirjinta ta ce.

"ni dai ka fita.."

Waje ya yi bai ce mata komai ba ya wuce masallaci.

Ruwan zafi ta haɗa a bathtub ta shiga tana mai lumshe idanunta jin yanda zafin yake ratsa ta a hankali. Haƙiƙa ko yau ta ji zafi, amma bai kai kaman na waccan ranar ba domin bata san ma a wace duniya take ba wancan, amma yau zafin kaɗan ne.

Ta jima tana gasa kanta wanda tunanin maganganunsu Yaa Amina ne ke ta dawo mata na wannan ranar da suke ta bata tabbataci a kai. Ga shi komai ya faru kaman a mafarki.

Sai da ta gama duk bukatunta sannan ta yi alwala ta fito ta yi sallah, tana cikin yin azkhar ɗinta wani bacci mai nauyi ya sake kwashe ta tsabar kasala da gajiyar da ta tarar mata.

Yana shigowa ya ganta kawai ya ji tausayinta ya kama shi. A hankali ya ɗuƙa ya ɗauko ta sai gashi ta buɗe ido ta kalle shi.

"Good morning Wife...."

Sake kawar da kanta ta yi wanda a yanxu wata kunya take ji dangane da irin abinda ta aikata a daren jiya.

Gefen gadon ya ajiyeta sannan ya kwaɓe jalabiyarsa ya bita suka Kwanta suka sake komawa bacci wanda bai farka ba sai misalin ƙarfe tara na safe. A hankali ya sauko gudun kada ya sake tayar da ita ya koma parlour inda ya yasar da kayayyakin tafiyarsa tun a daren jiya, ciki har da wayoyinsa wanda ya tarar da miss calls da yawa har da Maami ta kira shi da Hamad.

Maamin ya fara kira wanda sai yanzu ya tuna da wata Nazli ganin kiran Maamin tasa. Wallahy gabaɗaya ya manta da wannan auren nan nasa da aka ɗaura masa daren jiya.

Tana yin picking ya gaishe ta amma sai ya ji muryanta can ciki ciki alamar tana fushi.

"Maami kina fushi ne?"

"Eh,.."

"I'm sorry..."

"Yanzu Maheer ya kamata ka tafi ba tare da ka tsaya ka yi magana da Nazli ba? Maheer don't complicate things please.! Yanda iyayen yarinyar nan suka yi accepting you have to accept it too matuƙar dai kana son farin ciki na..."

"I'm Sorry Maami, but ina ƙoƙarin yanda zan yi na iya sarrafa kai na ne a wannan maganar. Maami I don't want to do anything stupid da zai sa abubuwa su je yanda bai kamata ba, ki yi haƙuri..."

"Na san cewa gobe ne rananka ta ƙarshe. Idan ka kambala zai ɗauke ka zuwa yaushe ka kambala komai ka dawo gida?"

Dum-dum! Haka ya ji zuciyarsa ta buga lokaci ɗaya. Wannan fa abu ne mai yiyu ba kai tsaye ace yabar Nigeria wai har abada. Ba zai taɓa iya barin maryam ba har abada...

" Maheer magana fa nake..."

"It can take me a month Maami."

"A month??"

Ya ji ta ambata a mamakance domin ita kanta ta ji abin a ba za ta. Wata ɗayan lafiya?

"Maami wasu abubuwan har yanzu ba su kambala ba..."

"Maheer a tsarin da management ɗin Maritime suka gabatar min babu wani additional month a ciki. Is only 12month and gobe kuma wa'adin zai cika..."

"haka ne Maami but ni ina da wani kasuwancin da na yi investing wanda zai iya ɗauka ta a month kafin na gama handling komai na dawo."

"Na ji! To ita Nazli fa?"

"Maami to ai ba ta sa ran cewa ma za'a yi mata wani aure a jiya ba ballantana ta saka rai da wani jiran namiji kawai ta zauna sai na dawo..."

Cike da jin tsabar mamakin da ya kusa kashe ta zaro ido tamkar suna ganin juna ta ce.

"Maheer..."

"Maami ina busy yanzu, idan na kambala abinda nake zan kiraki."

*******

Daga Ammie sai Abbah da kuma shi Faris ɗin suka san abinda yake faruwa. Hatta kayan gadonta da aka rufe da su aka kai wa Alhaji Gimba makulli Abba cewa ya yi a ƙyale shi a nemo mata wani, daman ko banza idan aka ce a ɗauko kayan to wannan gidan da ya kama haya ya yi musu kaɗan domin ɗakunan ba su yi girman waɗan can ba.

Umma na can tana ta gayyato mutane kamar wata mahaukaciya wai su zo raka Rabibinta gidan Mijinta Allah ya kai ta.

A parlourn Baba Salisu Abbah ya saka a kai masa ita a hankali bayan ta zauna ya kira sunanta.

Amsawa ta yi kanta a ƙasa ba tare da ta ɗago ba ya ce.

"Wane ne ya zaɓo miki Faris?"

Sai da ya maimaita kusan sau uku sannan ya ce.

"Rabi'a tambayarki fa nake?"

Sai yanxu ta amsa murya can ƙasa ta ce.

"Abba ni ce."

"Ke ce kika kawo sa kuma kika ce kin amince da auren sa ko?"

"Eh Abbah..."

"To abinda zan faɗa miki shi ne, rayuwar aure gabaɗayanta hak'uri ne, kuma idan kana son mutum babu inda ba za ka iya binsa ku zauna ba. Daɗi baya zama kullum haka zalika rashin daɗi baya zama kullum. Faris namiji ne wanda ya san abinda yake ki bi mijinki sau da ƙafa ku zauna lafiya. Idan kuma wani abu ya biyo baya na wulaƙanci ko na take haƙƙi to ki sanar dani in sha Allahu zan yi abinda ya kamata. Allah ya baku zaman lafiya ya baku zuriya dayyaba."

Ba tare da kawo komai a ranta ba ta amsa da amin suka fito. Ammie ta so ya fito fili ya yi mata bayani domin ya ja mata kunne don ta san halin ta amma sai ya ce ta ƙyale ta Mijinta shi zai fahimtar da ita.

Haka suka fito hannunta cikin na Aunty Shema'u suka shige mota suka tafi.

Unguwar ko ita ba laifi tana da dama dama, amma daga shiga unguwar zuwa cikin gidan da 'yan kai amaryar suka shiga daga nan zance ya sauya sai gulma ta kacame tamkar filin wunin buki. Shima gidan ƙaramin gate ne sai matsakaicin harabar gida. Parlour ne da bedroom a haɗe Wanda ke da toilet ciki, sai kuma wani single room dake waje shi ma daban da aka sanya mata wani gado a ciki.

Sai kitchen a waje da kuma toilet ɗin tsakar gida. Gidan ba laifi domin tiles ne a parlour sai breaking tiles a tsakar gidan.

Hankalinta ne ya ta shi ganin ɗakin da aka shigar da ita ga maganganun mutane dake tashi a kunnen ta ɓaro-ɓaro ta na ji.

A ruɗe itama Aunty Shema'u ta ce.

"Kutumar uba! Rabi'a miye haka nake gani? Ya naga wani gidan ba wancan aljannar duniyar ba?"

Yaye mayafin kanta ta yi tare da miƙe tsaye ta fashe da kuka tana kallon mutane ta ce.

"Nima abinda na gani kenan Aunty Shema'u. Miye abinda yake faruwa haka?"

Leƙowa Mummy Jamila ta yi ta ce.

"Ku fito jama'a mu tafi dare yana ƙara yi.."

Mayafinta suka ga ta figa itama tana faɗin.

"Wallahy tallahy ni ma ba za'a bar ni a wannan gidan ba, wallahy gida zan koma.."

Zaro ido Aunty Shema'u ta yi tace.

"Ki rufa min asiri Rabi'a ki yi hak'uri ki zauna, ki jira idan mijin ya dawo sai ya sanar dake abinda yake faruwa. Idan kin ga wurin zama ki zauna. Idan kuma ba ki gani ba sai ki san inda dare ya yi miki. Amma Mukam ba za ki barmu da mummunan tarihi ba ace mun kawo amarya mun koma da ita. Ko kuwa jama'a na yi laifi?"

Ta ƙarashe maganar tana mai kallon mutanen da suke ɗakin.

Komi Mummy Jamila ba ta ce musu ba, daman su Yaa Na'ima suna shigowa suka juya suka koma abin su.

A haka suka zame suka barta ita kaɗai tana wani irin kuka mai ban tausayi. Tana ganin sun fice ta ɗaga waya tun kafin su isa ta kira Umma ta shaida mata halin da ake ciki.

Bayan ta kashe wayar ta sake Leƙowa waje ta shiga ƙarewa tsakar gidan kallo, Generator ɗinda ta hango yana aiki shi ne abin da ya ƙara baƙanta mata zuciya ta sake rushewa  da kuka. Babban Gen ɗin wancan gidan ta tuna wanda yake da ɗaki mai zaman kansa tsakar gida mai interlock da abubuwan more rayuwa shi ne zai yi mata baƙin ciki ya kawo ta nan.

Tunda 'yan rakiyarta suka fita bata zauna ba har ta ji an buɗe ƙofar an shigo.

Wani kallon banza ne ta watsa masa mai cike da takaici da baƙin ciki.

        ✍️ OUM-AMEER  ✍️