Chapter 23
🌀 *HAƊIN ƘADDARA* 🌀
By
AyshaNalado
Sadaukarwa ne a gareki ƴar uwa rabin jiki *RUKAYYATU* (Aunty Ummi) Son so fisabilillah😍
BOOK 1
Page 23
Wannan dare sam bai ya wa iyalan Abie daɗi ba, gaba ɗayansu babu wanda ya iya cin abincin kirki saboda damuwa da halin Aysha take ciki, ga fargaba da tunanin, ina ta je? Me ya faru da ita? Su wane ne suka sauke ta a mota? sai dai babu wanda ya kuma ɗago maganar kamar yadda Abie ya yi musu umarni. Har cikin dare Ammie bata huta ba kwana ta yi karya tsakanin ɗakinta da ɗakinsu Salmah, tana duba jikinta da ruwan da ta daura mata daga baya. Washegari ta tashi jikin da ɗan sauƙi,sai dai sam babu walwala a tare da ita, don haka ta yi wanka da taimakon Salmah, daga zaune ta ranka sallolin dake kanta, da kyar ta idar, a wajen ta kuma zamewa ta kwanta, saboda kanta da ke ciwo, “Sannu Sister. Ya jikin?” Salmah dake zaune akan darduma ta faɗa tana kallon ta, bayan ta idar da azkar ɗinta. Lumshe ido ta yi ta bude a hankali sai kuma ta ɗan jinjina kai alamar amsawa. Kafin Salmah ta sake cewa komai wayarta dake maƙale a jikin caji ya ɗauki ƙara. kasancewar ya fi kusa da Aysha, yasa ta yi karfi miƙa hannu ta zare mata shi daga cajin, “Waye?” Salmah ta tambaya fuskarta dauke da mamakin wane ne ke kiranta a daidai wannan lokacin, tambayar da ta yi ya bawa Aysha damar kallon screen ɗin wayar, dan sunan ido ta yi gabanta na faduwa kafin ta ce “YA A.” Zaro idanu Salmah ta yi irin na kaɗuwa, sai kuma ta yi murmushi kafin ta miƙa hannu da sauri ta karɓi wayar, tare da miƙewa tsaye, cikin ɗan inda inda ta ce, “Laa Yayana ne.” Sai kuma ta juya da sauri za ta fice daga ɗakin ba tare da ta ɗaga wayar ba, saura ƙiriss su gobza karo da Ammie da ta sawo kai a bakin kofa, hannunta dauke da kofin shayi mai zafafa da kuma ledar magunguna mai dauke da tambarin asibitin da take aiki. Baya ta yi da sauri ta kauce mata tana faɗin, “Ya Salam! Sannu Ammie. Sai kuma ta raɓa ta gefenta ta fice a gaggauce kamar za ta tashi sama. Bin bayanta da kallo Ammie ta yi har ta ɓace, sai ta girgiza kai ta ce “ Allah ya shirya.” Kafin ta juyo da kallonta kan Aysha da ta yi kasaƙe cike da mamakin yanayin Salmah, ko me suke boyewa ita da Ya Anas ɗin oho, “ Surprise ɗin dawowarsa mana, da yake shirin yi mu ku.” zuciyarta ta ba ta wannan amsar, sai kuma ta yi yar murmushi kawai.
“Sannu Aysha, kin tashi?” Muryar Ammie ya katse mata tunani, “E Ammie.” “ Ya jikin?” ta sake faɗa tana taɓa goshinta, bayan ta ajiye kayan hannunta “Alhmdlh da a sauƙi Ammie.” “Har yanzu jikin ki da zafi, anya ba za mu tafi asibiti ba kuwa.” Girgiza kai ta yi kafin ta ce, “A'A Ammie ciwon kan ne yafi damuna yanzu, amma jikin da sauki.” “ Ba zan biye miki ba, Aysha don nasan halin nukufurcinki zuwa yamma idan banga irin saukin da nake son gani ba, dole zan yi addimting ɗin ki a asibiti.” Ɗan kwaɓe fuska ta yi cikin salon shagwaɓa. Ammie ta harareta, sai kuma ta dauki kofin shayin da ta shigo da shi ta mika mata tana faɗin, “ Oya ungo ki sha, mu yi allura ki sha magunguna maza.” Ƙarba ta yi ta fara kurɓa a hankali tana ya mutsa fuska saboda rashin jin daɗin shayin da take yi, bakinta babu test.
A haka Salman da Abie su ka yi sallama, dawowarsu kenan daga Masallaci kai tsaye suka zarto ɗakin domin duba jikinta. Cike da tausayawa Abie ya tambayi yadda ta kwana haka ma Salman. Ammie ce ta yi musu bayanin yanayin jikin duk su ka bada goyon bayan zuwa asibitin anjima idan idan jikin ya ƙi.
A haka wunin wannan ranar ya shige, sosai Aysha ke samun kula a wajen waɗan nan halin ta ko'ina, yadda suka nuna tsananin damuwarsu yasa ta yi ta kokarin karfafa kanta, amma abu ya ci tura, zafin jikin da sauki matuƙa amma fa ciwon kai tamkar karuwa ya ke yi, har ya kai matsayin da, ko ido bata iya budewa da kyau balle ta yi kwakwaran motsi, , ga tunanin abinda ya faru da ita a gidan AA ya gaza barinta, idan ta tuna har wani zabura take yi saboda tsoron da ke kamata.
Ganin babu sauƙi, kamar yadda Ammie ta faɗa rana na yin sanyi, ta shiryata ta dauketa a mota suka tafi asibitin da take aiki, bayan ta kira abokin aikinta Dr Lukman, kwararren likita sosai yana da baiwa ta musamman akan aikinsa, shiyasa Ammie ta kirasa, don ta yarda da shi duk abinda ya shafi iyalinta wanda ya sha kanta taimakonsa take nema.
Kai tsaye emergency aka nufa da Aysha, sosai ya dubata, ya bata gado, bayan ya yi mata test, ya gano jininta ne ya haura, hakan ya yi sanadiyar haifar mata da ciwon kai, sai kuma buguwar da ya gane ta yi a kan wanda shima ya ƙara hassasa ciwon, sai zafin jiki da rashin kuzari wanda stress da tension ɗin da take ciki suka haifar mata.
Godiya Ammie ta yi wa Dr Lukman bayan ya gama yi mata jawabi, jiki a sanyaye ta fito daga office ɗinsa, zuciyarta babu daɗi, kalmar hawan jini nata nanatuwa a zuciyarta, ta san Aysha na da hawan jini a baya, amma tun daga lokacin da su ka rungumeta suka kwantar mata da hankali tare da nusar da ita rayuwarta tana da muhimmanci, sai suka nemi larurar suka rasa, to menene musabbin motsawarsa a yanzu? Ƙarar wayarta ne ya katse mata hanzari, ganin Salmah ce ke kiran yasa ta ɗaga ta kara a kunne, “Ammie ya ake ciki, ya tsare ta ne.” ta tambaya cike da damuwa, “ E Salmah.” Ta amsa mata a sanyaye, “ Ya Rabbi! To gamu nan biyo ku yanzu.” “Ok ku taho da duk abinda ya dace.” Bayan sun gama wayar, Abie ta kira shima ta sanar masa da halin da suke ciki, don baya gidan bai san ma sun zo ba, ya san dai za su je. Shima ya jajanta, kuma ya ce idan ya gama zai biyo.
Kimanin awa daya bayan nan, su Salmah su ka iso, lokacin anata kiraye kirayen magriba. Suna nan tare har wajajen karfe tara na dare, lokacin Abie ya zo shima, sai wajen karfe goma har ma ta gota, sannan ya hada kan Salmah da Salman kasancewar gobe za su fara test, su ka tafi duk da Salmah ba ta so ba, don rigima ta saka akan su barta ta kwana Ammie ta wuce amma Abie ya ki amincewa ya ce ta je ta yi karatun jarabawa, a haka suna tafi yayinda Ammie ta zauna za ta kwana.
Suna zuwa gida ta shige ɗakinsu, ta mayar da kofarta ta rufe ba tare da kula Abie da Salman dake ta kokarin tsokananta ba, zama ta yi a bakin gado ta yi waya na kusan mintuna shidda, kafin ta mike ta fara rage kayan jiki ta, sai da ta kammala duk wani abu na al'ada irin wanda su kan gudanar kafin kwanciya barci kamar wanka alwala da sauransu, sannan kwaso handout ɗinta ta fara dubawa, saboda gobe, sai da ta ga ji, ta ture littafan gefe, ta janyo wayarta, missed calls din Zahra Bukar, da na wasu daga cikin friends ɗin su har uku ta gani a wayarta, da sai lokacin ta kula a silent yake, “Lafiya kuwa? ” Ta furta tana miƙewa zaune maimakon kwanciyar da ta yi, Zahra ta fara kira, user busy, don haka ta canza akalar kiran kan Sofiyyah, ringing ɗaya ta daga kamar jira take yi dama, “Salmah Mu'az ina kika shige yau ne, tun jiya bakya online kina da labarin abinda ke faruwa kuwa?” cike da wani irin annashuwa ta yi maganar, gaban Salmah ya faɗi ta ce, “No tun jiya da safe ban kunna data ba, saboda bana cikin natsuwa me ya faru?” Dariya Sofiyyah ta kece da shi, hakan yasa Aziza Bello dake kusa da ita ta karɓe wayar, ta ce “Salmah hau online faka faka ki ga me ke faruwa.” daga haka ta kashe wayar, tsaki Salmah ta ja, ta san halin iskancin ƙawayen nata idan ya motsa, yanzu haka ma ba wani abin kirki bane ko kuma wata gulmar ce may be, kamar ta share sai kuma zuciyarta ta gaza hakuri, sub na data ta yi, sannan ta hau WhatsApp, sannu a hankali messages suka fara shigowa, ganin tagging ɗinta da aka yi ta ko ina a duk wani groups da take ciki wanda ya shafi makaranta, kama daga kan general group, group na yan year ɗinsu, na yan department ɗinsu, na friends da sauransu, ga kuma sakonni ta private hada bakin lambobi mara suna, sai ta ji hankalinta ya tashi, zuciyarta ta tsananta bugawa, sai ta shiga maimaita Innalillahi wa Inna ilahi raji'un, sakon Zahra ta rufe ido ta fara shiga, bidiyone sai kuma voice kusan guda biyar, bidiyon ta fara shiga hannunta na rawa. Abinda ta gani a bidiyon ne ya sanya wayar kusan subucewa, “Kutumelesi! Surajjjj!” Ta furta da wani irin sauti tana ƙanƙance idanunta cike da bala'i........
Wacce ta shirya payment yanzu kafin mu gama Book 1, 800₦ ne saura page 2 mu kammala, a saka a wannan account ɗin 7041130088 Aisha Alhaji Yahaya Opay, a turo shedar biya ta ***.
Ina shaida muku ko shafin farko ba mu bude na littafin hadin kaddara ba, ku hanyarta biya kada ku bari nishaɗin nan ta wuce ku, ga wadanda suka san rubutu sun sani, ba za ku yi kaico ba, labari na gaba tafiya ce miƙakkiya wacce za ta gamsar da ku in Sha Allah.