GADAR GIWA... (Toro ke buga mata ganga)
GADAR GIWA
by @auntyindo
*🪻G
Maa ta ɗan murmusa ta ce "Kin ji abun wani iri ko?, to misalin haka ne, ni ma babu yadda za a yi in manta da Yayyena da Ƙanne, bare kuma Iyayena, gidanmu gidanmu ne don haka sai naj e Taron nan ko me zai faru babu ruwan ki, sannan ke da Khalil ma sai kun je wannan Umarni ne!" Ƙasa ta yi da kai gami da sauke wani gwauron numfashi, Khalil kuwa sai rarraba idanu yake yi. Maama ta cigaba da cewa "Rabona da zuwa Taron fa an kai Shekara Biyar tun Mahaifinmu yana Shekara ɗaya da rasuwa, yanzu ina son ƙara zuwa kuma zan cigaba da zuwa, ke da shi ma haka, ki ma dena faɗen ba za ki je ba ɗin nan!" gyaɗa kai kawai Hibba ta yi tana jin kamar ta fashe da kuka, Maa-ma ta ce "Yanzu dai tunanin da na fi yi koma shi ne, abin da zan kai wa Ummina, kawai ki yi min girki mai daɗi irin na Zamani sai in kai mata, ba wata burga zan yi ba, kawai zan yi daidai Ƙarfina ne, duk wani abu na san tana da shi shi ya sa gwara a yi girkin yadda za ta yi ko lauma ɗaya ne ta sa Albarka!" "Toh za a yi in sha Allahu, Gobe za mu je ni da Khalil mu siyo duk abin da za a nema ko? tun da Abincin zamani kike so Maama" "Eh shi nake so, Allah ya kaimu sai ku je da wuri ku dawo da wuri"
"Amma fa ni Jibi akwai Taro da za mu yi , kuma ba a so in ƙi zuwa da wuri bare kuma ƙin zuwan duka" Hibba ta faɗa fuskarta ɗauke da damuwa "Wannan ba matsala, za ki iya haɗawa biyu, ban ce dole sai kin wuni ba!"
Ba don ranta ya so ba ta ce "To Allah ya kaimu Jibin".........
Ranar Taro....
Cikin sauri-sauri suka gama shiryawa sannan suka É—auki hanya a cikin Adaidaita Sahu.
Dukkan su sun yi matuƙar kyau son Kowa ƙin Ɗan Hassada, kuma sutturunsu masu tsada ne a wajen mai ƙaramin Ƙarfi, Maa-ma da Hibba Atamfa ce riga da zani suka sa amma kowacce kalar tata daban, ba anko suka yi ba, Khalil kuma Shadda ya saka.
Hibba ba ta yi wata kwalliya ba kawai manleɓe ta shafa sai kwalli da ta saka a idanunta wanda yake matuƙar ƙara kusanto da Kyaun da Allah ya zuba mata, idanunta kaɗai suna da matuƙar kyau da Ɗaukar hankali.
Baƙa ce amma ba irin wuluk ɗin nan ba, za a iya saka ta a jerin masu ɗan haske daga fannin baƙaƙe, ba za a kirata Doguwa ba hallau ba za a ce mata gajera ba, kuma a dire take ta ko,ina ba aibu shap ɗinta ya fita sak! gata yar dumurmur tubarkallah...... Son kowa Ƙin Maƙiyi.....
Har ƙofar Gida Ɗansahun ya ajiye su suka sallame shi ya yi gaba, Maama ta kalli Hibba da ke ta famar yin waya ta ce "Za mu shige idan kin gama kya shigo" kai ta gyaɗa tare da yin baya su kuma suka shige.
Wayar ta cigaba da yi tana kallon gidan wanda ke ɗaya daga cikin Manyan gida mafiya girma a layin, kai tsaye ma ana iya cewa ya fi kowanne kyau da tsari domin an sabunta ginin ya ƙara zama na Zamani ba kamar sauran ba, hallau ba ya rabo da shan Gyara.
Ta ɗan jima nan a tsaye kafin ta katse wayar ta numfasa gami da cewa "Dole Maama ta sha Wulaƙanci tun da ta Auri Talaka!" karaf! idanunta ya sauka cikin na wani bawan Allah da take ganin duhu-duhunsa tun ɗazu, sai dai ba ba tsaya kallon inda yake ba ma bare ta san me yake yi, sai yanzu ta lura kawai ita yake kallo.
Yaro ne haɗaɗɗe kuma tsadadde, daga ganinsa bai wuce shekaru Ashirin da uku zuwa da huɗu ba, amma fa zabgege ne mai Ƙirar Sadaukai.
Kawar da kai gefe Hibba ta yi kamar bata san da Mutum ba ta sa kai zuwa cikin Gidan.
Wayarta ce ta sake yin ƙara ta yi saurin ɗauka ta kara a kunnenta tana faɗin ''Zan zo fa, kin san muna da Taro ne yau na Dangi abin ya haɗe min!"
Duk hankalinta na kan wayar da take yi duk ba ta lura da Rukuni Uku da ke a tafkekiyar Harabar ba.
A gefe Ɗaya Maza ne su Uku Matasa majiya Ƙarfi kuma masu ji da kansu...
ÆŠayan gefen kuwa sun kai su Bakwai har da Mata guda Biyu sun sha wata Shiga ta banza mai bayyana surorin jikinsu, kuma sun yi dumu-dumu kafaÉ—a da kafaÉ—a da Maza suna hira suna tafawa har sai da suka ankara da Hibba sannan Wutarsu ta É—auke suka dawo kallonta.
ÆŠayan gefen ma Maza ne zasu kai huÉ—u, su ma Æ´an saffa-saffa masu tsadar Gaske, abin mamaki kaf kallonta suke yi kamar sabon watan Ramadan.
Takaici da kuma bugawar da zuciyarta ta fara yi da sauri ya sa ta yi saurin tsinke wayar ta cigaba da tafiya.....
"Ke!!" ta ji an kira ta cikin tsawa, da sauri ta juya tana kallon inda ta ji muryar, daga cikin rukunin da suka fi yawa ne, "Zo nan!" wanda ya kiratan ya ƙara faɗe.
Ba musu ta ƙarasa inda suke tana ƙaƙalo murmushi ta ce "Sannun ku!" "Wace ce ke? daga ina?"
"Daga Gidanmu, sunana Hibba!" ɗaya daga cikin ƴan matan wanda suke bin ta da kallo mai cike da Tsana ta ce "Na ganki wata Ƴar Matsiyata da ke!, me ye haɗin ki da gidan nan!"
Ta ɗan murmusa ta ce "Oh! ashe ba ku gane ni ba, ai matsayina ɗaya da ku ni ma Jika ce" a Tsawace Budurwar ta ce "Ke!?? wa ya ce miki Matsiyaci da mai Arziƙi ɗaya ne?, Wane Shegen ne Ubanki a cikin Mazan gidan nan da har kike wannan gadarar??"
"Ya ilahi!" Hibba ta faɗa gami da ɗan dafe goshi, cigaba ta yi da cewa "Wai kina nufin duk Ƴaƴa Maza da Kakarmu ta haifa Shegu ne?? ki ce gwara da Allah ya sa Mace ce ta haife ni a cikin su ba Namiji!"
Ashar budurwar ta luntsuma gami da É—ago hannu a zafafe ta kaiwa Hibba Mari......
Da sauri ɗaya daga cikin ƴan Samarin ya riƙe hannunta gami da hankaɗa ta Baya wani a ciki ya rungumo ta yana faɗin "Sorry Sister!" .
Shi kuwa wanda ya harbo ta baya Miƙawa Hibba hannu ya yi don su yi musabaha tare da cewa "Sunana Sabran!" Ta ɗan murmusa ta ce "Sannu" a ɗan kunyace ya janye hannunsa sai kuma ya ce "Am... Ikram ta ɗan yi maganganu masu tsauri, amma ke kuma taki tanfi zafi, ita banta fayyace ba duk da maganar ta yi kama da hakan,, ke kuma duk sai kika zage mana Iyaye!"
Ƙare musu kallo ta yi ɗaya bayan ɗaya ta ga dai kallon ta kawai suke yi wasu dai da alama sun ji haushinta wasu kuwa da gani kallon neman wurin shiga ne kamar dai shi Sabran ɗin.... a tausashe ta ce "Ku yi haƙuri fa!, kawai kun san zuciya wani lokacin da wuri take fusata!"
Cikin zafin rai Ikram ta fizge daga hannun Hafiz da yake ta famar shafa ta ta juyo kan Hibba tana faɗin "An gaya miki ke kaɗai ce mai Zuciya? to wallahi za ki ga abin da zai biyo baya, Za ki gani banza Ƴar Matsiyata!" banza Hibba ta yi mata sai ma kallon Sabran da ta yi ta ce "Ku yi haƙuri fa!, ni zan shige ciki!" ba ta jira amsa ba ta juya gami da watsa idanunta don tana sane da sauran da ta gani a Harabar wanda tana da tabbacin duk sun girmi Waɗannan Fitinannun Yaran, mamakin ta ɗaya ya akai aka rasa mai tsawatarwa??? duk da suna wani gefen amma alamar faɗa ko kurma zai gane ta, bare har an kai ga kawo duka.
Dayan gefen suna nan, Manyan ciki ne dai saura ɗaya a cikin uku, biyun duk sun watse, yana jingine a jikin wata Farar Mota hannunsa harɗe a Ƙirjinsa, ga mamakinta shi ɗin ma fa ita yake kallo kamar dai sauran.
Duk ta tafi tunani ba ta san ma tana kallonsa ba sai da ta ga sun yi ido huɗu ,,,, ba ta san ma sanda ta ja Tsaki ba, ta yi saurin canja akalar tafiyarta zuwa cikin gidan, zuciyarta cike fal da takaicin su manyan banza da ba za su iya tsawatar wa na ƙasa da su ba.
Cikin wani taku me kama da sanÉ—a ya rufa mata baya, Wasu daga cikin abokan rigimar ma suka biyo bayansa.
Cikin wanda suke su huÉ—u ma Mutum biyu ka sa jira suka yi sai da suka bi Sawu.
Ikram kuwa fizgar hannun abokiyar cin mushenta ta yi wato Inayah, suka zagaya baya suna mita da bala'i, cikin hirar tasu za ka gane ba wai Maganar Hibba ce ta ƙona musu rai ba kawai ganin Yadda duk hankalin samarin nasu har ma da na gefe ya koma kanta daga shigowarta ne ya tsaya musu a rai, musamman jin yadda Ƴan Samarin suka fara santi suna yaba mata, jin hakan kuwa ya sa suke ganin kamar za ta Ƙwace musu Kambunsu , wanda suke ganin sun fi kowace Ƴa farin jini a Family ɗin, duba da yadda suke juya ƙwaƙwalen Samari suke Karɓe Ƴaƴan Banki, gashi gani suke sun fi kowacce kyau da Ƙira da iya kwalliya da shiga ta alfarma kawai don suna shiga irin ta jan Ra,ayin maza da kuma tonawa kai Asiri.
Taɗi suka cigaba da yi akan abin da zabsu yi su ƙuntatawa Hibba sai dai sun rasa yaya za su yi don ba a cikinsu take ba bare su wulaƙanta ta, ƙarshen abun kenan a nuna mata bambanci tsakanin Talaka da mai Kuɗi.
Duk wannan abun da suke yi , su ma Ƴaƴa ne na ɓangaren Mata a gidan, Ikram ƴar Ƙanwar Maa-ma ce , amma ita Babanta yana da ɗan Kuɗinsa hakan ya sa ita ma Ummanta Hajiya Nafisa ba raini tana murza kuɗi, sai dai ba kamar Ƴaƴa Maza na gidan ba. Inayah kuwa Ƴar Yayar Maa-ma ɗin ce, ita Kuwa za a iya kiransu Talakawa akan sauran, Da, suna da ɗan kuɗin daidai gwargwado daga baya Lamura suka koma baya, hakan ya sa ita ma Hajiya Karima ta zama Ƴar bayan Ƙeya a cikin gidan, sai dai ba kamar Maa-ma ba don duk da haka Hajiya Karima tana da ɗan nata ita, da ma Maa-ma Talaka ta aura tun farko, kuma yanzu ma Talakan take Aure, ita kuwa Inayah duk da su ba komai ba ne akan sauran ita ɗaukar kanta take ta fi kowa,,, don tana matuƙar wankar kuɗin Samari a cikin Family da waje, halinsu ya zo Ɗaya da Ikram, shi ya sa Abotarsu take tsawon rai kuma ake zama lafiya, aikinsu kenan yaudarar Maza da ci musu kuɗi kuma babu yadda suka iya suna ji suna gani, gashi kafin Namiji ya yi zuciya da su aiki ne, Allah ya yi musu baiwar Abun, ba dai su kafa ƙwaƙwa akan Namiji kuma ya tsira ba, shi ya sa ita Inayah ba ta san wata ƙamfa ko lallaɓa rayuwa ba, kawai rashin Mutunci take zubawa son ranta.
wannan kenan
A cikin gida.......
Maa-ma tana falon Farko a tsakure kan Carpet kanta a ƙasa lokacin Hibba ta shigo, Tsugunnawa ta yi har ƙasa tana gaishe da Hajiya Mommy sai da ta maimaita sau uku sannan ta amsa da "Lafiya" ta cigaba da cewa "Ke Rabi! Rabi!! zo ki je ki kai Abincin nan a bayar ga mabuƙata kar ma ya ruɓe, ai ganganci kika yi Amina ai kin san ba ni da yunwa babu abin da Abincinki zai yi min , ni a Ƙoshe nake su ma Yaran babu mai ci duk sun wuce ajinsa"
Cikin wani mugun baƙin ciki da takaici Hibba ta zuba wa Maa-ma ido tana jin tamkar zuciyarta za ta yi tsawa.
Hamdan ya ƙaraso wajen yana cewa "Rabi! Ki ajiye min Plate ɗaya kafin ki Bayar!"
daga haka ya wuce gaba yana jin Hajiya Mommy na cewa "Ba ka ci Abincin banne ko an ce maka babu ne?? , ga Abinci can mai rai da lafiya ka ci ka bayar sai ka ce...." ganin ba saurarenta yake ba ya sa t aja tsaki ta yi shiru.
Wanda suka biyo Hibba a Baya wasu dariya suke wasu Mutum biyu daga ciki kuwa sun yi kicin-kicin da fuska. Miƙewa Hajiya Mommy ta yi tana cewa "Ke Amina tashi ki kai Ƴaƴanki su gaida iyayensu sai ki dawo, ni ma yanzu wucewa zan yi can Mmu sha hira!" "to" Maa-ma ta ce gami da tashi tana gayyatar su Hibba...
Jiki a sanyaye suka rufawa Hajiya Mommy baya har suka isa wani ƙaton Falo kuma Ƙawatacce, duk iyaye Mata suna nan ana zaman jin kai, zaman Na isa, ke ba ki isa ba, ado da kwalliya kuwa kowacce tana wane wata!.
A gefe guda akwai Tsirarin Æ´an mata, da Yara.
Sallama Maa-ma ke ta rafkawa amma an rasa mai amsawa , sai da Hajiya Mommy ta ce ga fa Amina nan ku gaisa.
sai lokacin suka kalle ta ita da tawagarta wato Hibba da Khalil, wata Farar Mata haɗaɗɗiyar Hajiya ta ce "To fa! yau kuma a taron namu har da Gajiyayyu da marasa Ƙarfi?" Maa-ma ta yi murmushi mai ciwo ta ce "Har da mu!, ina wuninku " "Lafiya!" wasu a ciki suka amsa.
Hajiya Nafisa ta murmusa ta ce "Hajiya Madina tawa!, Gajiyayyu ma ko su gayyar SoÉ—i!"
"Ai duk ÆŠaya!" wata Matar ta faÉ—a tana dariya.
Hajja Mommy ta taɓe baki ta ce "Hmm! ta kawo Abinci ma, amma na ce a kaiwa Mabuƙata don babu buƙatarsa anan, shi ne na ce bari in gaya miki don an ce gwara a dinga faɗen alkairi ko?"
wasu dariya abun ya ba su , wasu kuwa kallon sheƙeƙe sukai wa Maa-ma suka taɓe baki.
"Ku Yaran nan ba a koya muku Gaisuwa da girmama manya ba ne?"
Faɗar Hajiya Nafisa tana bin su Hibba da kallon ƙasƙanci.
Hajiya Madina ta ce "Wannan ita ce wannan Agolar ko?" "Ita ce mana, kin ga ta girma ko?" Hajja Mommy ta faɗa cikin kauɗi da zaƙin murya irin nata.
"Ah!, ta fa girma, shi ya sa ta tsaya mana a tsaye" FaÉ—ar Hajiya Madina.
"Wai ba ku ji abin da aka ce ba ne?" Maa-ma ta faɗa cikin tsawatarwa, durƙusawa suka yi suka gaishe su amma sai mutum biyu ne suka amsa.
Hajiya Mommy ta ce "To ai kun gaisa ko? ku koma Ƙasan ai za su Fito"
kafin ta rufe baki Hibba ta juya ta nufi hanyar fita, caraf suka sake haɗa ido da Maridin Ƙaton da yake neman addabar rayuwarta da kallo (a cewarta), ba shi kaɗai ke kallon ta ba amma za ta iya cewa duk ya fi su Ƙwarewa wajen sa ido don kuwa kallon nasa matuƙar kaifi yake mata.....
Fatali ta yi da lamarinsa ta yi waje, sai da ta je Falon ta zauna sannan su Maa-ma suka iso.
Shiru ne ya ratsa tsakani kafin Maama ta ce ''Ni fa sai daga baya nake tuna labarin da kuka ba ni ranar da kuka fita Garden sai abun yake ba ni dariya" Hibba ta kalli Maama ta kawar da kai saboda ganin irin murmushin da take yi wanda ya fi kuka ciwo, wai kuma a hakan ƙoƙari take ta kawar musu da damuwa, "Maama zan tafi, na samu kiran waya ya fi a ƙirga saboda jirana da ake yi" Hibba ta faɗa tare da tashi tana gyara riƙon ƴar jakarta.
"Kar ki tafi yanzu gaskiya , ki bari sai ɗan anjima" "Me zan yi a nan Maa?! kawai mu zauna kamar korarrun karnuka ɗin shi ne kar in tafi?" "Eh ni na faɗa, duk da can ya zama dole to nan ma ya kama ki ne" "Ni fa ba ni da wata alaƙa da gidan nan, kuma in sha Allahu ba zan ƙara zuwa ba"
"Ba na son rashin hankali Hibba!, gidan Iyayena ne fa kike yiwa wannan furcin!" "Maama ba haka ba ne, gidan wasu dai da suka gina gidan suka ba wa Iyayen, nan bai yi kama da gidan iyaye ba, inda za ka zo ana cewa ka zo gayyar soɗi, inda ake korarka wai shi ne gidan Iyaye??!" "Zan faska miki mari fa!, na gaji da jin surutan banzan nan naki, ko ki so, ko ki ƙi gidan iyayena ne, hasali ma Mahaifiyata a Gidan nan take rayuwa, haka Mahaifina ya rayu a Gidan nan kafin Allah ya karɓi ransa, kuma na ce miki dole ki zauna!"
Ɗora hannu ta yi a ka tana zagaye wajen cikin sauri ta kai minti biyu tana kai mari ta kai gwauro sannan ta tsaya ta ce "Maa-ma ki taimaka ki yafe min ki bar ni na tafi don Allah! ba don na gaji ba kawai don ana buƙatar ganina a wani wurin, Maa duk a yau za mu gabatar da Sabon Project na aikinmu fa!".
"Gaggawar me kike haka?, ki yi haƙuri ki bi abin da Maa-ma take so ! " wata baƙuwar murya ta ji a cikin kunnenta, ta juyo da sauri don ganin kowaye, Shugaban ƴan sa ido ta gani tsaye a bayanta ya ƙureta da idanunsa da suke matuƙar yi mata Barazanar da babu dalili, "Please!" ya ƙara faɗe yana sake wararo mata idanu, ƙasa ta yi da kai ciki disashshiyar murya ta ce "Okay".
Ya ɗan murmusa kafin ya koma gefe ya zauna ya harɗe ƙafa ya zaro Waya ya fara danne-danne.
Hibba kuwa zagayen ta cigaba da yi tana yi tana duba Agogo.
Maa-ma ta ɗan kalli Hamdan ta ce "Na daɗe ban ganka ba Hamdan!, ina ga ko Zuwana na ƙarshe taron nan ban ganka ba saboda....." kasa ƙarasa maganar ta yi saboda tuno yadda ta koma gida cikin Mawuyacin hali saboda cin mutunci da tozarcin da ta fuskanta a ranar.
Lumshe ido Hamdan ya yi ya nisa kafin ya buɗe su akan Hibba yana cewa "Maa-ma ni ɗin ne Ja'iri ne, ba na son zumunci, na fi mayar da hankali kan Kasuwanci, shi ne ya fi burgeni fiye da Komai, shi ya sa Taron ma ban fiya zuwa ba, yau ɗin ma ina ga rabon katari ne, don kuwa ni ma dai kamar ita! ina da meeting yau!" ya ƙarasa maganar yana nuni da Hibba tare da ƙara zuba mata na Mujiya, ya rasa me yasa ya kasa gajiya da kallonta , a zahiri ba ɗabi'arsa ba ce yawan kallon Mutum amma yau a karon farko ya kasa janye idanunsa daga kan Hibba.
Maa ce ta katse masa tunanin da cewa "Ah lallai kam Ja,iri ne!, to Allah ya taimaka ya bada sa'a, ai dama kyaun Ɗa ya Gaji Mahaifi, indai kuwa ka gaji Abbanka ai ba za kai sanya wajen Kasuwanci ba!" Ya jinjina kai gami da cewa "Haka ne Mommu Amina! ina da jajircewa sosai akai da yake ra'ayina ne, sauran abubuwan da ba ra'ayina ba kuma fa ina da wuyar sha'ani a kai, kin ga ni ba na son Haɗa Kasuwanci da Daddy, amma Daddy da Ammy sun fi son haka, kuma gaskiya ina da ɗan wuyar sha'ani akan hakan!" "Ai sun san zaka tsaya tsayin daka akai shi ya sa suke ta zawarcenka, don haka ka dage ka yi abin da zai faranta musu ka ji?, in ka haɗa biyu ai duk za ka iya tun da kana da ƙwazo da jajircewa!" "Haka ne! ina yin ƙoƙari sosai, kuma zan ƙara ninka ƙoƙarin in sha Allah" .
Hajiya Karima ce ta ƙaraso wajen fuskarta ba yabo ba fallasa ta ce "Hamdan kana nan kana hira da Mamanka? ina ga rabon da ta ganka tun ba ka iya ɗaura Zariyar wando ba ko?!" Dariya suka yi duk amma banda Khalil da Hibba.
Hajiya Karima ta ce "Ki yi haƙuri fa Amina!, komai lokaci ne kin ji?, koda a haka Allah ya tsarawa bawa rayuwarsa to fa dole wataran komai zai canja tun da ba Duniya ce madawwama ba, ki yi haƙuri kin ji!, duk da na san da bakya haƙuri da yanzu idan aka ce ina danginki ma ba za ki nuna mu ba, Yaran dai su ne abun rarrashi yanzu!" Maa-ma ta murmusa ta ce "Ba komai fa, dama haka ne ai, duk ba mu yi fushi ba ma!" Kafin Hajiya Karima ta ce wani abu Hibba ta katse su da cewa "Ni fa na tafi Maa, yanzu ma kin ga Ismail ne yake kirana!" Kafin ta rufe baki Hamdan ya tashi ya samfe daga wajen, Maa-ma ta bita da addu,a, Khalil ma tashi ya yi zai bi bayanta Maa-ma ta hana.
Tana fitowa daga falon ta yi tozali da Hamdan, "Ko in raka ki ne?" ya jefo mata tambaya, ganin mukullin Mota a hannunsa ya sa ta ce "A É—ansahu na zo kuma a shi zan koma, a shi nake zuwa duk inda zan je!" ya saki baki yana kallonta.
Kafin yayi wani motsi ta fice....
A wajen Get ta gamu da wanda ta fara gani tun kafin ta shigo, yanzu ma kallonta kawai yake yi ko ƙifta ido ba ya yi tamkar wani saƙago...
Hibba ta zumɓuri baki ta yi gaba da sauri don kuwa ya fi mata kama da Mashayin Giya ga kallon da yake mata irin na ƙwalama,,, kar ta je yana jin haushinta ya sauke gajiyarsa akan ta.
Maa-ma ba wani daɗewa ta ƙara yi ba ta tashi ta koma gidanta dan kuwa har yara Ƴaƴanta idan sun zo wucewa kallon matsiyaciya suke mata su wuce, wasu ma har da aje mata magana don kuwa sun ga iyayensu suna yi...
Hamdan.... har ya gama zamansa ya bar musu Gidan bai nutsu da kowa ba don Hibba ta gama ficewa da hankalinsa.......
Aunty Indo