💦BARIKI TAFI GIDA 💦

Chapter 3️⃣

by @aishayakubuahmad811

💦BARIKI TAFI GIDA💦

writer✍️
Aisha Yakub Ahmad 







join my whatapp grouo via this link : ***













Bismillahir rahmanir raheem 








page 3️⃣








Tafiya take tana hasaso abubuwa da yawa da 
suka faru a rayuwarta , tana tuna yadda

 mahaifinta ya ke da son kuɗi , yadda baya

 girmama mahaifiyar ta , yadda yake wulaƙanta

 su , yadda yake dukan mahaifiyarta , kuka ta 
sak i , se da tayi me isar ta sannan ta goge

 hawaye , ta cigaba da tafiya , tun tana tafiya da 

kuzari har ta soma gajiya , haka ta ci gaba da 

tafiya , tana taku ɗai ɗai , dai dai san da zata 

tsallaka titi , wata mota ta taho da gudu , ba ta 

lura ba , se ƙarar horn taji a kanta wanda hakan 

ya gigita ta kawai a afka gaban motar , hakam 

ya bashi damar kaɗe ta.

Cikin sauri ya sakko daga motar lakacin mutane 
sun fara taruwa yayin da jaririyar nan take ta 
tsala kuka , kukan tane ya ankarar dashi har ya 
ga yarinyar,a hankali ya dauki uwar ya saka a 
mota sanna wani mutumi ya miƙo masa jaririyar. 
Wani private hospital ya nufa dasu , a nutse ya 
fito ya wuce ciki , tare da wasu nurses ya dawo ,

 cikin sauri suka nufa ciki da ita taimakon 
gaggawa suka fara bata , shi kuma yana riƙe da 
jaririyar , nufar wata nurse yayi ya miƙa mata 
jaririyar , wuce wa nurse din tayi da ita , yayin da 
shi kuma ya koma reception yana zaune. 

Waya yake dannan wa da bisani kuma se ya 
kara wayar a kunne ; “ musaddiq “ naji ya furta 
ina hospital kazo yanzu ka same ni , ban san me 
aka ce daga ɗayan ɓangaren ba , gani nayi ya sauke wayar……………….💧






HAJ ATIKA POV … ……………..




“ ai se naga bayan sa kamar yadda na kori uwar

 su ta barmin gida da wannan me idon magen , 
shima haka ze bar gidan nan “ shiru tayi banji 

ma aka ce daga ɗayan ɓangaren bah , sake 

cewa tayi “ ai ɗazu ina sane na saka aka yi faten

 wake da safe saboda nasan ko yunwa zata 

kashe shi baze ci bah, magana aka sake yi a 

ɗayan bangaren , kwashe wa da dariya tayi tace 

“ shi ya isa ya faɗa wa mahaifinsa abun da nake 

masa ai soko ne kina ganin sa “ dariya ta sake 

saki sannan tace “ indai wannan ne na miki 

alƙawari Nimrah bata da mijin da ya wuce Aabid 

in dai ina raye” sun daɗe sun tattauna sharrika  

iri-iri sannan sukai wa juna sallama daga baya 
………………..💧




wannan kenan 





“ Ummiey ina addah Ash ta ke “ wata yarinya ta 

fada wacca bazata wuce shekaru sha biyar bah, 

duba na kai ga wacca aka kira Ummiey, 

mahaifiyar Ashnahh ce , duba na sake kawai 

kan yarinyar , tsananin kamar da suke yi da 

Ashnahh ne ya saka na sake duban ta a karo na 

biyu , kyakyawa ce dan har ta so tafi Ashnahh

 kyau , tana da dan tsayi , saɓanin Ashnahh, 

kuma wannan tafi Ashnah garin jiki , kuma 

wanna fara ce sol ,  shiru Wacca ta kira da 

Ummiey tayi mata , itama bata sake ce mata 

komai ba kawai ta wuce ɗaki dan duba Ashnahh

 , wata mace na hango a chan ƙuryar ɗakin …………………💧

ku biyo ni domin jin yadda zata kasance 



Daga alƙalamin✍️
Aisha Yakubu Ahmad