💦BARIKI TAFI GIDA 💦

Chapter4️⃣

by @aishayakubuahmad811

💦BARIKI TAFI GIDA 💦




writer✍️
Aisha Yakubu Ahmad 






join my whatapp group via thus link : ***















Bismillahir rahmanir raheem 











Pages4️⃣









Kwance take tayi rubda ciki ta zubawa bango ido 
, ƙarasawa budurwar tayi ta taba wacca take 
kwance , juyowa wacca aka taɓa tayi , dara-

daran idanun ta kawai na kalla, naga suna 
tsananin kama da matashiyar nudurwar da ta 
shigo ɗakin da kuma Ashnahh , da hannu ta fara 
mata magana alamun ina “ Addah ash “ da 
hannu wacca akayi wa mavan da hannu ta fara 
nuna mata hanya , kuka ta fara tana mata 
magana da maganar kurame , hakan ya 
tabbatar mun kurmace. Bata bari ta ƙarasa mata 
bayani bah kawai ta saka kai ta fice zuwa inda ta 
samu Ummiey, magana ta fara cikin fusata da ke 
nuna zallar ɓacin rai da tsiwa da take tattare da 
ita , kana ganinta kasan gwana ce eajen iya 
tsiwa da fitsara , “ se da nace miki Ummiey 
matuƙar kika bari mijin ki ya kori yar uwata nima 
se na bar miki gidan nnan “, “ kunyi tunanin 
ƙarya nake koh , to wallahi nima gidan xan bari 
“, bata rufe baki ba murya daga sama taji ancre “

 Allah ya raka taki gona ki je kemq na barwa 
duniya “ ba wabi bane illa wanna tsohon da ya 
kori Ashnaah , wato mahaifinsu , magana ya 
cigaba “ Aida idan kema kika ƙara ko minti biyu 
a gidann se na kusan halakaki da duka “ be rife 
baki ba tayi karab tace “ Allah ma gode maka da  
ka fitar da ni da wannan gida na mijin umma , 
kuma kamar yadda ka faɗa zan bar mska gidan 
ka , amma ka sani se ka yi na damar korata da 
kuma ya Ashanah a gidan nnan “ , daga haka ta 
shige ɗaki ta ciga haɗa kayanta , fitowa tayi 
turus ta tsaya ganin Ummiey tsugunne a gaban 
baba tana kuka tana cewa ya mata rai , ƙafa 
yasa ya shureta  ta faɗi a wajen yayi wajen yana 

zage- zage , ƙarasawa tayi wajen Ummiey , 
dafata tayi ta shi ga magana cikin sanyi da karye 
war murya kamar ba ita ta gama yiwa mahaifinta 
tsiwa ba , wanda taje kira da mijin ummma , ji 
tayi an dafata ta baya ita , budurwace wacca 
aƙalla zatayi shekaru ashirin da biyu a duniya , 
tanan hawaye itama , ta fara mata magana ta 
kurame , “ tana mata alamu da karta tafi ita ta 
barta , kamar yadda  Ashnaah ta tafi ta barta “, 
bata san lokacin da ta fashe da wani kuka me 
taɓa zuciya ba , rungume juna sukayi suka 
cigaba da kuka tare , se da sukai mai isar su 
sannan Aida da banbare ɗayar tare da furta” 
Ashfahh kiyj haƙuri amma kinsan mijin umma 
baya magana biyu , tana magan tana gwada 
mata da hannuwanta yadda zata gane , kuka 
kawai wacca aka kira da Ashfah take yi . 



Juyawa Aida tayi tana ƙoƙarin barin gidan da 
gudu Ashfahh ta rungume ta ta baya ta mata 
alamu da hannu na zanyi missing dinki , itama 
tana hawaye tayi mata alamu na itama zatayi 
missing dinta , saka kai tayi ta fita a gidan ta bar 
umma da Ashfahh suna zubar da hawaye 
…..,………………..🥹



wannan kennan 





ku biyo ni domin jin yadda zata kasance 💧


Daga alƙalamin✍️
Aisha Yakubu Ahmad