💦BARIKI TAFI GIDA 💦

Chapter 5️⃣

by @aishayakubuahmad811

💦BARIKI TAFI GIDA💦



writer✍️
Aisha Yakubu Ahmad 





join my whatapp group via this link : ***












💦Ending of free pages💧









Bismillahir rahmanir raheem












Page5️⃣















Wata mota ce ta shigo harabar asibitin , wani 
matashin baƙin saurayi ne ya sakko daga motar 
aƙalla ze yi shekaru 28 zuwa da tara , sanye 
yake da blue jeans da black t-shirt,  sanye yake 
da wata ɓakar p- cap , black beauty ne, 
kyakyawa ne sosai , yana ƙananun idanu wanda

 suka amshi fuskar sa sosai, cikin asibitin ya 
dosa , a ƙofar shiga reception ya tsaya , yana 
ƙoƙarin kiran Abid , se ya hango shi zaune ya 

 lumshe idanunsa , cikin sassarfa ya ƙarasa 
wajen shi . 


Zaune yake ya lula duniyar tunani , saukar 
hannu yaji a kafaɗar shi wanda hakan ya sanya 
shi sakin ajiyar zuciya tare da juyawa dan ganin

 waye , haɗa ido yayi da Musaddiq , murmushi 
musaddiq ya sakar masa , haɗi da tambayarsa , 
lafiyar sa , kamar mara son magana haka ya 
shaida masa , abunda ya faru , waje ya samu ya 
xauna , ba jima wa se ga nurse ta ƙaraso wajen 
Aabid tace “ sir jaririyar na cin ƙoshin lafiya , se 
dai tana ɓukatar abinci , kuma the mother is 

unconcious ko za’a iya siyo madara ta yara se a 
bata kafin maman tata ta farfaɗo.


Miƙewa yayi ya isa wajen Musaddiq magana 
sukai sannan ya saka kai ya fice haraban 
asibitin,mota ya shiga ya fice daga asibitin 
………………💧





ASHNAHH POV………………..



Kwance take akan gadon asibiti , a hankali ta 
fara buɗe idanun ta da sukai mata nauyi , nurse 
ta gani a kanta , addu’a take a ranta , allah ya 
sa, jaririyar nan ta mutu , dan bata san ina zata 
nufa da yarinyar bahh , muryar nurse din ce ta 
dawo da ita daga tunanin da taje “ baiwar allah 
kin samu hatsari ne , kyma wanda ya kaɗe ki 
shine ya kawo ki asibitu , yau kwanan ki huɗu , 
shi yake kula da ciyar wa yarki da take chan 
gadon “ , ta faɗi tare da nuna mata gadon yar 
tata, fitsari tace tana ji haka ya bata damar shiga 
banɗaki, taji sayƙi sosai , bata jin komai a 
jikinta,alwala ta dauro sannan ta fito tana ƙoƙarin 
sako kanta ɗakin , shima a dai- dai lokacin ya 
shigo , yana sanye da white jean da blue shirt , 
haɗa ido suka yi , saurin sauke kanta ƙasa tayi , 
ta shiga takowa a hankali , dakin ta ƙaraso , ta 
zauna , gaida shi tayi , tsaya yayi yana kallonta , 
jin shiru ita kuma ya sa ta ɗago kanta , 
idanuwansu ne ya sarƙe ana juna , gaban ta ne 
ya faɗi ras, da sauri ta dauke idonta a kansa ta 
sake ƙasa da kai , samun kansa yayi da 
murmushi sanan ya amsa ta da lpy, kujera ya ja 
ya zauna , gyaran murya yayi ya fara magana “ 
baiwar allah bansan sunan ki ba , na daɗe ina 
fatan allah ya tashi ka faɗun ki ko dan ki faɗa 
gidan ku , sannan na maida ke “ yana fara 
magana hawaye suka fara wanke mata fuska , 
cikin muryar kuka tace “ bani da kowa , bawan 
allah na gode , allah ya saka da alkhairi , amma 
zaka iya tafiya tunda har na tashi”  , kuka take 
sosaai, shiru ne ya ratsa tsakanin su , miƙewa 
yayi yace kiyi sallah za muyi magana , be jira 

cewarta ba ya saka kai ya fice  a 

ɗakin………………💧







ku biyo ni domin jin yadda zata kasance

free pages sun ƙare 💧



Daga alƙalamin✍️
Aisha Yakubu Ahmad