1
ABUJA NIGERIA*.
~ASOKORO~
Wata kyakkyawar matashiyar yarinya ce wacce a kallo ɗaya za a tantance irin baiwar da Allah ya yi mata na tarin kyau da tsarin halitta, ta haɗa komai na macen da ta samu cikakken gata kuma shalelen iyayenta. Cikin shigar kayan motsa jiki ta ke guntun riga da wando masu faɗi wanda ya ke nuna alamun kaya ne da a ka tanada dan yin exersice. Ga sumanta da ta ɗaure shi da rebom yana reto a gadon bayan ta saboda aikin juya jikinta da ta ke yi cikin sauri-sauri, duk da ta haɗa gumi ba ta tsaya ba sai da ta ji ta gaji sosai kana ta dakata ta janyo wani ƙaramin farin towel ta shiga goge saman wuyanta da fuskarta Kafin ta ɗauko gorar ruwa ta kafa bakin ta shanye ruwan ciki tas sannan ta yarda gorar ta saki towel ɗin da ke saman kafaɗarta ya yi ƙasa.
Wani juye ta yi tamkar babyn roba tare da sarƙe hannayenta a ƙirjinta tana barin ɗakin games ɗin cikin sassarfa, kai tsaye katafaren ɗakin da ya ke mallakinta ta nufa wanda yaji kayan alatu da more rayuwa a ciki da a ka kashe maƙudan kuɗi duk dan a ƙawata bafin cikinta, ƙamshin sanyayyen turaren wuta da ya gauraya da sanyin AC ya mamaye cikin faffaɗan ɗakin.
Kan royal bed ɗinta ta zube tana mayar da numfashi tare da lumshe idanunta kana ta buɗe su, sai kuma kamar wacce aka tsikara ta sauko daga gadon ta faɗa toilet ta sakar ma kanta ruwa. Manyan idanunta da suke ɗauke da kalan blue ta shiga warewa a hankali ruwa na cigaba da shiga cikin su, gashin kanta kuwa yana kwanciya yala-yala akan kyakkyawar farar fuskarta. Duk inda a ke neman mace me aji da kuma kyau idan a ka zo kan ta an gama.
Furzar da ruwan da ke shigar mata baki ta yi tana mai maida gashin kanta da ya rufe rabin fuskar ta baya, a hankali ta soma gudanar da wanka tana mai bin sassan jikinta a sannu, bayan ta gama wankan ta ja bathrobe ta sanya, sannan ta ɗauki towel ta tsane sumar kanta, bayan ta gama ta fito ta nufi wajen madubin ɗakin ta ja stool ta zauna, Sannan ta soma busar da gashin ta da haire dryer. Mayukan gashi masu ƙamshi ta shafa kana ta haɗa ta yi parking na shi a tsakiya yayinda ta bar jelar gashin ke rito a gadon bayan ta.
Hoda da man laɓɓe kawai ta shafa sai kwalli da ta saka a ƙurmin ido wanda ya ƙara fito da kyawun su tare da girman halittar su.
Ƙarar ringing ɗin wayarta da ke kan gado ne ya jawo hankalinta wajan, wani ƙayatattan murmushi da ya bayyana dimples ɗinta ta saki yayin da ta ɗaga wayar da faɗin.
"Assalamu' alaikum Daddy, amincin Allah ya tabbata a gareka. Fatan ka tashi lafiya?" Ta ɗayan ɓangaren a ka amsa da:
"Albarka ya tabbata ga ƴata da iyalan ta, fatan Nazli din Abba ta tashi cikin ƙoshin lafiya?" "Alhamdulillah Daddy, barka da warhaka Dadyn Nazli. Ina Mommy da Aunty Neesah?" Ƙyataccen Murmushi Daddy ya yi yana cewa. "Mun tashi Lafiya Alhamdulillah, Mommyn ki ma gata nan ku gaisa." Ya faɗa tare da miƙe ma Mommy da ke serving ɗinsa, hannu ta sa ta kaɓi wayar suka gaisa kana ta miƙa ma Aunty Neesah ma suka gaisa kafin daga bisani suka yi sallama da Alƙawarin za su haɗu a school.
Murmushin da baya rabuwa da fuskar ta a koda yaushe ta sake ta na jin soyayyar iyayen ta da kuma ƴar uwar ta na ratsa dukkan bargon jinin jikinta, a rayuwa ba ta haɗa familyn ta da komai, she just love them so much, irin wanda ba a iya misaltashi. Ta na kuma fatan Allah ya bar su tare cikin aminci da soyayyar juna. Ganin lokaci yana tafiya gashi yau suna da lectures ƙarfi 10:00 kuma yanzu har 9 saura ya sa ta buɗe closet ta fito da wando jean da farar riga mai gutun hannu ta sa kana ta ɗaura abaya after dress a kai, ta isa gaban madubi ta tsaya ta yi rolling ɗin mayafin abayar, ta fesa turare tare da ɗaukar jakarta da kuma wayarta cikin farin ciki da takun kasaita ta bar ɗakin.
zaune Zaid ya ke a parlour kan kujera mai ɗaukan mutum biyu, hankalinsa kacokam yana kan wayarsa kuma da alama abu mai muhimmanci ya ke dubawa. Dogo ne fari mai matsakaicin kyawu da ba za'a saka shi cikin layin munana ba, sanye ya ke cikin wani tsaɗaɗan black suit da ya amshi jikinsa. Ƙamshin turaren ta ne ya fara yi masa iso wanda ya tabbatar da Nazli ɗinsa ce. Ɗago kai ya yi ya na mai bin ta da wani sihirtaccen kallo.
"Good morning love." cewar Nazli ta na sakin lallausar murmushin da ya bayyana wushiryar da ke tsakanin haƙoran ta na sama, Zaidu ya lumshe ido ya buɗe ya na mai cewa. "Morning beauty, fatan kin tashi cikin ƙoshin lafiya?" ya ƙare maganar tare da miƙewa ya riƙo hannunta suka nufi dining. "Lafiya Alhamdulillah." Nazli ta faɗa a hankali daidai lokacin da ya ja mata kujara ta zauna ya ja ta kusa da ita ya zauna, da kanta ta yi serving na sa kafin ta yi wa kanta.
Lokaci zuwa lokaci ta ke cire kai ta na satan kallonsa, ganin yadda ya ke cin abincin sa cikin nutsuwa da kwanciyar hankali ba ƙaramin burge ta ya yi ba. Bakin ta cike da magana amma ba ta san ta ina za ta fara ba, ido kawai ta zubawa masa ta na jin son sa na ƙara mamaye zuciyarta. Ajiyar zuciya ta sauke ta shiga tunanin ta ina za ta fara warware saƙar da zuciyarta ke yi mata, hakan ya sa zuciyarta ta ke bugawa da sauri numfashinta ya na fita da ɗumi, ta na burin yau ta fallasa masa sirrin da ke cikin zuciyarta wanda ta dinga ɓoye wa na tsayin lokaci, ta san zai yi matuƙar farin ciki idan ya ji kalaman da za su fito daga bakin ta saboda abu ne da ya daɗe ya ke burin ji daga gareta, shi ya sa ma ta shiga dokin furta masa kalmar da zai gyara makomar aurensu har ba ta son abin da zai zo ya gibta a samu akasi.
Auren ta da Zaid bana soyayya ba ne auren haɗi ne, ko ta ce a wurin ta ne ba soyayya ba amma Zaid tun rana ta farko da ya yi tozali da ita ya ji ya kamu da son ta wato love at first sight,bai yi ƙasa a guiwa ba ya tunkare ta da baton amma ta nuna masa ita ba ta ra'ayin aure yanzu balle soyayya, amma duk da hakan bai yi ƙasa a guiwa ya cigaba da gwada sa'ar sa akan ya ji ya gani zai cigaba da tuntuɓar ta dan ba ya jin zai iya haƙuri da ita. Ganin ya yi ta ƙoƙarin shawo kanta amma hakan bai samu ba sai ya tukari mahaifiyarsa da batun inda ita kuma ta samu Mommy da maganar, da ya ke Mommy da mahaifiyar sa aminan juna ne hakan ya sa Mommy yin farin ciki da wannan batun domin alaƙar su za ta yi ƙarfi daga aminai su koma sirkan juna an zama ɗaya kenan.
koda Mommy ta samu Nazli da wannan maganar ta nuna rashin amincewar ta domin ita a lokacin ba ta shirya yin aure ba dan karantun ta shi ne a gaba da komai, amma ganin rashin jin daɗin hakan a fuskar Mommy ya sa ta amince ba don ta so ba sai dan farantawa Mommy. Dan Mommy uwa ce a gare ta da za ta iya salwantar da komai na ta dan ganin ta faranta mata kamar yadda ta tabbata Mommy na iya yin fiye da hakan ma a kanta, sannan masu iya magana na cewa abun da babba ya hanga yaro ko ya hau tsani ba zai gani ba, kuma ta yarda da hakan dan tana tsaka da ganin zahirin hakan.
Wata shida kenan da auren su kuma har zuwa wannan lokacin babu abin da ya dangaci auratayyah da ya taɓa shiga tsakanin su, domin tun a daren ranar da a ka ɗaura aurensu ta sanar da shi cewa ta aure shi ne ba don komai ba sai dan farantawa iyayen ta dan haka kar ya tsammaci komai a wajan, sannan ta buƙaci su bi komai a sannu har zuwa lokacin da ta ji za ta iya mallaka masa zuciyarta da kuma gangar jikinta. Hakan ne ya sa ta buƙaci damar sanin juna kafin ta ɗauki mataki na gaba, duk da Zaid bai ji daɗin hakan ba amma sai ya bata lokacin da ta buƙata. Haka suka cigaba da rayuwa a cikin gida ba tare da sun raba ɗakin ɗaya ba, soyayya da kulawar da Zaid ke nuna mata ya narkar da zuciyarta garesa. Kuma ta ji tana son su kai auren su zuwa mataki na gaba, kusan sati ɗaya kenan ta ke faɗa da zuciyarta a kan ta sanar da shi su wuce gurin amma ta gagara.
Gyaran murya da ya yi ne ya jawo hanaklinta gareshi. "Me ki ke tunani ne haka?" cikin inda inda ta ce. "B..ba..babu komai." "Kin tabbata?" Kai ta gyaɗa masa alamaun eh, kallon plate ɗin gabanta ya yi ya ce. "Then why are you not eating?" "Zan ci." "Good." Ya furta tare da maida hankalinsa ga na sa abincin. Ka sa haƙuri ta yi ta ce. "Zaid, can we talk please?" Cikin kulawa ya ce"Yeah me ya faru?" Wasa ta fara yi da yatsun hannunta tana taraddadin ta ina za ta fara, har ta buɗe baki za ta yi magana amma sai ringing ɗin wayarsa ya katse mata hanzari.
"Sorry baby zamu yi magana anjima in na dawo." Ya furta bayan ya ɗaga wayarsa, kai kawai ta iya kaɗa masa ta na gani har ya bar parlour. Zazzafar ajiyar zuciya ta sauke tana mai fatan samun ƙwarin guiwar faɗa masa anjuma, sai ta maida hankali ta kan breakfast ɗinta.
Sallamar da a ka yi ne ya ja hankalinta ga wacce ta yi sallamar ta shigo palourn, matashiyar budurwa ce da ba za ta haura 18 ba. Sanye ta ke cikin doguwar riga da hijabin da ya kai mata guiwa. A hanaklin ta taka har wurin da Nazli ta ke ta rusuna ta gashe ta. "Aunty ina kwana?" "Lafiya Nadia kin tashi lafiya?" "Lafiya Aunty." Ta masa tare da tsayawa wuri ɗaya ta soma wasa da bakin hijabin ta, lura da hakan ne ya sa Nazli ta ce. "Akwai abin da ki ke buƙata ne Nadiya?" "Eh Aunty, idan ki ka bani izini ina son na je gida na duba Mama da ƙanina." Ta faɗa cikin taraɗaɗin amsar da za ta samu a wajan uwar gijiyar ta, duk da ta san da wuya ta hana ta zuwa gida duba mahaifiyar ta. "Uhmm yaushe kenan ki ke son zuwa?" Murmushin jin daɗi ta saki tare da cewa. "Da wai gobe na ke son zuwa." kurɓan tea ta yi tare da faɗin. "To Allah ya kai mu goben."
"Na gode sosai Aunty, Allah ya saka da alkhairi, ina alfahari na kasancewata a ƙarƙashin ki domin ke mutumiyar kirki ce, komai na zama ke ce sanadi. Ina fatan nima wata rana na zama kamar ki a rayuwa, shi ya sa na ke ƙoƙarin koyi da ke, Allah ya bani ikon faranta miki Aunty." Sanyayyen murmushi Nazli ta saki tare da kaɗa kai kawai sai ta ce. "Nadiya ina son ki san duk abin da na miki ko na yi wa ƴan uwanki domin Allah na yi shi, dan haka ba na son ki ji a ranki kamar ina bin ki wani abu ko ki yi tunanin za ki biya ni." Sai ta ja fasali tana mai fuskarta ta da kyau kana ta ɗaura da. "Domin idan kin yi hakan ba zan ji daɗi ba, ina ganin ki ne tamkar ƴar ƙanwata. Ko aikin nan ma ke ki ka dage sai kin yi amma ni karatu na ke son ki yi, ina son ki yi karatu mai zurfi ta yadda za ki iya taimakon mahaifiyar ki da kuma ƙaninki ba tare da kin nemi taimakon kowa ba. Rayuwa babu tabbas yau mu ne gobe ba mu ba, ba lallai ba ne mu kasance tare har abada ba. Ina son ko da a bayan rai na ki zama abin kwatance ki zama wani abu a rayuwa."
Shesheƙar kukan da Nadiya ke yi ne ya sa ta dakata da maganar ta zuba mata ido na ɗan ɗakika kafin ta sake murmushi da cewa. "To me ye na kuka Nadiya?" "To ba ke ce ki ke iƙirarin mutuwa ba, dan Allah ki dai na faɗan haka ba na jin daɗi Aunty Nazli."
"Hmm Nadiya kenan, to ai ko babu mutuwa akwai yanayin rayuwa, komai zai iya faruwa a ko wani lokaci. Ni dai fatana za ki kasance mai riƙon amana da gaskiya a ko wani yanaye da ki ka tsinci kanki." Dum gaban Nadiya ya faɗi jin ƙarshen maganganun ta.
"Yanzu dai ba wannan ba, na yi magana da principal ɗin makarantar an gama komai da komai in sha Allah daga next week za ki fara zuwa makaranta, sun ce za su a je ki a SS 1 duba da you are drop out sai ki maida hankali sosai a kan abin da ya kai ki. Bana son wasa Nadiya."
"In sha Allah zan yi iya ƙoƙari na Aunty, ba zan baki kunya ba." Ta furta a sanyaye dan gaba ɗaya jikinta ya yi sanyi."
"Yauwa hakan na ke son ji daga gare ki, Allah ya dafa miki." Ta faɗa tare da miƙewa ta na duban agogon hannunta da ya nuna 9:20, a hankali ta furta. "God, na yi latti." Jakarta da mukullin motar ta ɗauka kana ta dubi Nadiya da ta soma tattara dining ta ce. "Bye na Nadiya sai na dawo." Daga nan ba ta jira mai za ta ce ba ta fita cikin sassarfa.
Tana fita compound ɗin gidan ta faɗa a motar ta ƙirar BMW mai gadi ya wangale mata gate ta fice, cike da ƙwarewa ta ke sarrafa sitiyarin motar har ta isa makaranta. Bayan ta samu wuri ta yi parking ta fito, tsaye ta yi gaban mirror motar tana gyara rolling ɗin mayafinta ta ji an ƙira sunan ta.
"Nazli!!"
Waiwayowa ta yi cikin sakin fuska da da fara'ar da ba ta rabo da fuskarta ta ce. "Aunty Neesah."
Daidai lokacin da Neesah ke ƙarasowa. "Sai yanzu ki ka shigo kenan?" Halan ba ku da lectures da wuri?"
"Ehh sai goma mu ke da lectures yau." "Lokaci ma ya yi ai dan ƙarfe goma saura ƴan mintuna." Cewar Neesah tana duba agogon tsintsiyar hannunta, ɗan kaɗa kai ta yi sannan ta maida idanunta kan Nazli da ta buɗe motar ta fito da jakarta da takaddun ta. "Okay sis bye sai kin fito kar na riƙe ki." "Okay bye." Daga nan ta juya har ta soma taku Neesah ta sake tsaida ita. "Uhmm...ji mana!."
"Yes, lafiya?"
"Ina jiran ki idan kin fito mu wuce gidan ki tare".
"Okay ba damuwa ,bari na yi sauri kin san lecturers ɗin department ɗin mu basu wasa da latti".