21
by @gureenjoh
"Ma'u don Allah ki buɗe baki ki ci kin ji?"
Jiddah ta faɗa cikin muryar rarrashi don Ma'u yini guda kenan babu abin da ta yarda ta ci kullum lamarin kara ta'azzara yake, bata san me ya same ta ba amma ko a hirar da ta tsinkayi masu tsaron nasu suna yi ta ji suna magana akan rashin ƙarfin kwakwalwa shi yasa trauma din yayi hitting ɗinta Sossai kuma muddin ba kudi aka kashe a kanta kuma aka haɗa da kwararrun ma'aikatan jinya ba kwakwalwarta na shutting kanshi down a je a je za ta iya faɗuwa ta mutu.
Dukda hankalin jidda a tsanani tashe yake bata daina addu'a da rokon Allah ya hana kalmansu tabbata ba, tun da suka gano lagonta sai suka kashe mata baki, ya zamana bata iya yi musu musu sam, iyakaci saƙo take kaiwa wanda a wani sashe na zuciyarta tana jin har hakan ma bai dace ba kila amfani ake da miyagun kwayoyi ana lalata al'umma, ta tabbatar babu wani abu da za'a fitar daga gidan da kyakyawar nufi don dukkansu mugaye ne, dukkansu babu mai imani ciki.
Kuka kawai jiddah ta shiga yi a wurin cikin rashin makama, ganin irin kukan da take yi yas a Ma'un miƙa hannu ta riƙe nata sai ta dago da sauri, ruwan ta bata ta karɓa ta sha ta shiga bata abinci sai ta ga tana ci, hawaye ke zubarwa jiddah har Asm'aun ta gama cin abincin bata yi ko loma guda ba kuma nasu ne su biyun.
J da yake hakimce cikin kujera yana ɗan juyawa a hankali sanye da wasu bakaƙen kaya ya dauke kai ya kalli shadow
"Wannan kayan idan ta kara sati bata da amfani a yi da ita kudu a tabbatar ta yi nesa da nan a zubar ta bi ruwa"
"An gama J na fahimta"
Ya miƙe ya fice yana duba lokaci, Wayanshi ya zaro ya zubawa sakon kai ido na seconds kan yayi wani murmushi.
"Yaro yaro ne! Yaro bai san wuta ba sai ya taka!"
Mota aka buɗe mishi ya shiga suka fice daga arear gabadaya.
****
Shehi ya zama busy kwarai a kwanakin da suka biyo baya, zai iya cewa ma bai taɓa cin karo da kwanaki irin wannan ba ya haɗa stress mai yawa hakan ya sa Sam bashi da wani lokaci, tuni ya manta da wata Na'imatu da ya je ya gani yayin da a gafe su Ammiey ke ta hidimarsu har kuma lokacin Abbiey basu yanke hukunci ba.
Shi kam gabadaya damuwarshi sunan Ammar ya wanku, Abba ya rage fushin da yake yi ba wai suna ganin laifin Abba bane don yana fushi a'a abu da dole kowani uba zai ji babu daaɗi abin da idan ya tambaya za'a bashi to me na zamba? Shi kuma Ammar ganin ɗan uwanshi ya shiga lamarin Sossai sai ya ja baya ya bar mishi.
A ɓangaren wa'azi sai ya ƙara zafi ya zamana kullum maganan shi kan azzaluman 'yan siyasa da yadda za mu farka mu tsayawa kawunanmu, barazanarshi ga azzaluman sai ya ƙaru shi zai yi ya kwana lafiya amma da zaran ya fita duniya su kuma babu bacci.
Yau yana zaune a office dinshi cikin BUK yana duba wasu takardu ya ji an yi knocking.
Ya amsa sai aka tura kofar aka shigo, bai ɗago ba sai da ya ji shiru kan ya ɗago sai idanunshi suka faɗa kanta yadda ya tsare ta da su sai ta rasa natsuwa, bakinta ya shiga rawa ta rasa me za ta ce.
Cikin rashin sanayya yace
"How may I help you?"
Wani dummmmmm kanta yayi, yana nufin bai gane ta ba ne ko yaya? Rawa muryarta ya fara dukda maganan da take so ta yi da kyar tace
"Na'ima ce"
"Na'ima?"
Ya maimaita sunan trying really hard to be polite.
Sai ta juya da sauri ta fice wani irin kunya mai yawa na rufeta, a lokaci ɗaya hawaye ya shiga zubo mata ashe haukanta take, ashe tana nan tana baza hauka bata sani ba ya mance da ita ma, zuciyarta ya shiga ƙuna tun daga ranar da aka ɗarsa mata shi bayan dogon crushing bata samu isashen bacci ba ta zaci ko a waya zai ƙirata amma shiru, ta yi tunanin to kila ya sake zuwa nan ma shiru ta kasa hak'uri da kyar ta yi gaining courage na zuwa ashe rabon tayi kwanan baƙin ciki ne ya kaita.
Shi kam aikin shi ya cigaba da yi yana taɓe baki mata sun sha zuwa mishi haka don sai da ya shata layi mai girman gaske ya buga misali na ban mamaki da wata kan ya shawo matsalar zirga-zirgan su na ba gaira ba dalili da sunan gaisuwa ko wata kyauta(Gift).
Sai da ya gama ya miƙe ya bar makarantar yau ma shi kaɗai ne don haka da kanshi yake driving har Company, office ya wuce yana duba inda suka kwana ganin jiya-e-yau ya sa ranshi matukar ɓaci.
"Meyasa Hisham? Meyasa?"
"Ranka ya dade...."
Hannu ya ɗaga mishi sai ya miƙe tsaye
"A da ina zaton cewa matsala ake samu na ƙirge har kudin su ke ɓacewa amma a yanzu yadda ake tempering aikina ya tabbatar min da cewa da gaske sama da faɗi ake yi da kudaden nan. Ban san amfanin kiran kanku Audit ba muddin za'a samu wani yana lalata duk ayyukanku daga ciki"
Hisham yace
"Ka yi hak'uri Ranka ya dade"
"Ba zan yi hak'uri ba Hisham!"
Ba da tsawa ko ihu yayi maganan ba sai dai abin da ke zuciyarshi ne ya faɗa, ba zai yi hak'uri ba idan ya kawar da ido akan abin aikinshi ya cuta tunda yana da albashi already, ko ba don albashi ba companyn Abbiey kam ai na zuri'arsu ne gabadaya tunda don su aka yi kuma ake kan yi.
"Na dakatar da kowa a cikinku zan yi bincike mai tsauri duk wanda na kama da cin amana dole zai bar ma'aikatan ba ɗaga kafa, abun kunya ne a gare mu a ce daga wannan team ɗin ne zance ke fita har muke ba wa azzalumai daman ɓuya.... Ka isar musu da sakon nan you can leave"
Kwarjini da kuma yadda ya Kamen ne bai taɓa gani ba hakan ya sa dole bai iya sake furta komai ba ya fice, shima Miƙewa yayi ya fice gabadaya daga companyn saboda ɓacin rai.
Gida ya koma bayan yayi parking ya fito yana amsa call a dab kofan sashenshi ya gamu da Imam suka karasa tare don haka a parlorn ƙasan ya zauna Imam na tsaye har ya kamallah kan Imam yayi mishi barka da dawowa.
"Ga wannan an ce in baka ne har makaranta aka kawo"
Karɓar envelope din yayi ya buɗe ya fitar da farar papern ya karanta, sai ya ɗan yi tsaki... Ya miƙa wa Imam
"Ka ƙirasu ka tabbatar musu matukar ɗauke dauken hotuna da kuma videos zai kawo su ba ma buƙata"
Imam ya ɗan yi tsaii daga fah gomnati ne suke offering taimakawa Islamiyyarsa ta Al-Noor da kuma makarantar maza ta Auladul-Noor sai kuma masallacin shi Al-Noor Mosque, suna so duk abin da babu su zuba saboda jin Daaɗin ibada amma yana ba da umurnin ban da hotuna?
Kallonshi Shehi yayi sai ya ce
"Ka daina mamaki Imam, a sanina da 'Yan siyasa suna so ne kawai su yi campaign da hakan, ko ma su yi amfani da wannan daman wurin bata sunana tunda sun san da su azzaluman gomnatin nake faɗa, idan aka ga sun yaɗa ɗan wani abu kalilan da za su zuba ne wa gobensu ba don ni ba cewa za'a yi ina ƙin su amma ina karbar abin su da jin daaɗi su al'umma me zai hana su karɓa su kuma zaɓe su?"
Ya miƙe tsaye
"Gobe zan tafi Abuja kuma zan yi akallah sati biyu so za su zo bana nan make sure kun yi abin da ya dace dukda ma zan kira Sheikh Mukhtar"
"Toh in Shaa Allahu"
Imam ya amsa a lokacin Shehi ya gama haurawa Saman.
Wanka yayi saboda wani irin gajiya da yake ji, a tsaitsaye ya haɗa loggage dinsa don tafiya ce ta abin da ya shafi musulunci dole kuma ya kasance yana nan ɗin don har cikin gidan aka kawo mishi kati akan gagarumin taron.
Kaman yadda yake son jallabiya ya kuma saba da su fiye da kowani kaya farar jallabiya ce jikinsa ya saka Ghutra a kansa don idan bai saka ba ji yake kaman ba komai yake tafiya abu ne da ya riga ya saba for many years, Kasa ya sauka ya nufi wurin Maamah yana shiga ya samu tana duba wasu turarukan wuta.
Bayan sun gaisa tace
"Yauwa da ma yanzu nake zancenka a raina ga Turarukan wuta masu kamshi da na yi placing order an kawo daga Bauchi na sanka da turarukan wuta na tabbatar za ka ji daaɗinsu kwarai don ba dai daaɗi ba"
Tayi maganar tana miƙa mishi Sandal chips na bakhoor by seemah, dukda bai saba sayan turarukan wutan ma anan ba daga Saudia yake zuwa da abin shi jin wannan sai da ya sake kallon sticker ɗin yana tabbatarwa a Nigeria aka haɗa wannan ɗin, Sossai ya san turarukan wuta kuma ya yaba da kamshin wannan Sossai da Sossai. Miƙewa Maamah tayi ta je don ta kawo masa abinci ya ɗauki dayan dake cikin kyakyawar paper bag ɗin ya buɗe yana ɗan kai wa hancinshi ya shaki kamshin kadan ya duba sunan Hawii. Lallai ya samu plug da zai yi holding on to a Nigeria.
(Domin samun wannan turarukan wutan masu Daaɗin kamshi ku tuntuɓi bakhoor by seemah a wannan layi (***) babu kalar khumrah, misk ko Turaren da ba za ku samu ba tasted and trusted)
Bayan ya gama cin abincin yake sanar da ita tafiyanshi Abuja gobe da yammaci, addu'a tayi masa ya ɗauki paper bag ɗin yayi mata godiya kan ya fice, kyauta mai matukar muhimmanci da aka bashi a kwanakin kenan.
Sashen Daddah yaje ya gaishe ta da jiki ta ma samu sauki don tana taka ƙafar lafiya lau suka gaisa da Goggoninsa kan ya nufi wurin Ammiey ƙarshe ya sanar mata batun tafiyar bayan sun gama tattaunawa har zai miƙe tace
"Batun yarinyar nan Na'imatu kana kuwa ƙiranta a waya?"
Sai da gabansa ya ɗan faɗi da kyar ma ya tuna sai kuma fuskarta ta fara mishi gizo kaman ita ce ta zo dazu ya maimaita sunan a ransa da wanda ta faɗa tabbas ita ce, baki ya ɗan taɓe kaɗan bai ce komai ba.
Shirun shi ya tabbatarwa Ammiey da baya kira ɗin.
"Ka yi kokari ko baka je ba ka ƙirata a waya"
Ya amsa da
"In Shaa Allah"
Kan ya miƙe ya fice daga sashen, sashenshi ya koma dukda masallaci zai fita sai da ya ƙona turarukan nan duka yana jin natsuwa da kamshinsu har ransa, daga nan ya ɗan saka wasu oils a hannu da bayan kunnensa kan ya ɗora Jubba baka da gold ya fice daga sashen zuwa Islamiyyarsa don supervising kan lokacin sallah ya shiga.
*****
"Sohana na tura miki ticket dinki ta waya sai ki shirya gobe ki wuce Abuja"
Tana kishingide ne a parlorn Idanunta na kan TV da ake haska wani American film na faɗa, a hankali ta miƙe da kyau tana kallonsa
"Abuja? Me zan yi a Abuja kuma?"
"Akwai sakon da nake so ki kai min ne"
Yayi maganar ba tare da ya bata fuskar wata tambaya ba amma Diva ce bata yi shirun ba sai da ta tambaya
"Haka kawai rana tsaka? Anya Baba baka tunanin akwai abin da ya kamata in sani? I'm not a Lil child anymore Idan Abu da ya danganci natsuwa da kwanciyar hankalinmu ne you have to say it out Don mu shirya masa...."
Ya katseta
"Har yanzu ke yarinya ce Sohana, har yanzu da saura. Bana son musu ki yi abin da na ce!"
Fuskarta ta hade tamau ba don shi din ba ne wallahi ba za ta je ba, Sam bata yarda da shi ba dukda dama a irin lokutan nan na siyasa ba natsuwa ya cika samu ba saboda lokaci ne na tashin tashina, zub da jini, rigimgimu iri iri bai cika so ma tana nan ba amma ai zaɓen da saura.
Haka ta miƙe ta shige dakinta ranta a hade ya bi bayanta da kallo sai ya ɗan dafe Goshi.
Tana kwance Shaly ta shigo ita da Zubash su suka haɗa mata kaya don ta faɗa musu, sun jima a dakin kan suka tarkata suka bar gidan gabadaya.
****
A daren ranar Shehi ya zauna da su Abbiey ya sanar musu batun tafiyar sai Abba yake cewa
"Yauwa batun wannan yarinya kana ga hankalinka ya kwanta da ita za mu iya zuwa nemar maka aurenta? Ina tambayarka saboda mu fita hakkinka kar mu yi abu daga baya ka ga ba mu kyauta ba, muddin baka sonta za mu san yadda za mu yi da iyayenka mata su bar maganan"
Shi sai lokacin ya tuna Ammiey ta ce ya samu layinta.
"Abba ba ni da zaɓi duk abin da kuka yanke daidai ne"
Numfashi suka sauke amma basu ce komai ba, sai Uncle Ishaq ne yace
"Irshad ba'a aure babu soyayya fah, auren wannan zamani da soyayyar ma bai ɗore ba bare haɗi idan baka so kar ya zo ya zamana dayanku na cutuwa"
Ya girgiza kai
"Uncle duk shawarar da kuka yanke ya yi, Ammar ya binciketa bata da wani matsala dama kuma akan ilimi, kyau da nasaba addini ya yarda a nemi aure"
Daga nan ya sanar da su tafiyarsa gobe don ba lallai ma suna nan ba zai wuce, bayan sun gama mishi fatan alkhairi ya fice daga parlorn ya bar su suna cigaba da tattaunawa.
A parlorn ƙasa ya samu Ammar, ya zauna yana janyo system dinshi dake wurin ya kunna sai ya ɗan kalli fuskar Ammar yana yatsina fuska kaman ba zai yi magana ba sai ya ce
"Ammar! Layin yarinyar nan za ka samar min"
"wace yarinya kenan?"
Ammar ya tambaya yana ajiye Wayanshi sai da ya kusa Seconds goma kan ya ce
"Na'imah"
Murmushi Ammar ya saki
"Ka ce Amaryarka, amma don rashin kirki ni ne ma zan samar maka? Ni nake neman aurenta ne?"
Tsaki kaɗan Shehi yayi
"Ka san ba don Ammiey ta matsa ba duk wannan abu ba za'a kai shi da ni ba don bana son bata lokaci da raba hankali akan abin da ya kamata, ka samo min layin ta kan Ammiey ta ƙara ritsa ni in rasa amsar bata pls"
"Toh an gama Al sheikh"
Anan suka cigaba da hira sama sama Shehi na aiki har Mufida ta kawo musu abinci, anan suka ci sai chan dare Ammar ya fice daga shashen shi kuma sheikh ya haura sama, al'adarsa na bacci duk ya gama kan ya kwanta yana lumshe idanu.
Washegari bai yi wani nisa da gidan ba sai da ya tabbatar ya gama komai da ya kamata, la'asar lisss Ammar ya kai shi Airport.
Luggage dinshi babu wani yawa don haka shi yake turawa don zai shiga da shi cikin jirgin.
Farin thobe ne jikinsa da wani golden Jubba, Ghutra dinshi fari ne sol sai baƙin Agal daga sama takalmarsa bakake ne hannunshi ɗaya na tura Luggage din ɗaya na riƙe da alkyabba ɗin yana tafiya cikin natsuwa har ya gama duk abin da zai yi ya zauna wurin jiran flight, VIP section ne don haka kujeru ne masu kyau da tsari maroon colour zagaye da wurin, Ac na aiki haka kamshin Airfreshner a cike da wurin.
Tasbihi yake yi da yatsun hannunsa dayan hannun na riƙe da waya yana dannawa ya shiga jin sautin takalmi na shiga kunnenshi don sauti ne na takalmi mai tsini da ya haɗu da tiles sai yake ba da ƙarar marar Daaɗin saurare a wurinshi bai ɗaga kai ba Sam.
Ita kuwa kujerar da yayi mata ta samu ta zauna bayan ta tura milk color traveling bag ɗinta da ta ɗora mishi kit din Saman hannun gefenta kaɗan kafa ɗaya ta ɗora kan ɗaya tana cigaba da cin chewing gum yana ba da sauti fuskarta na kan waya.
Tsakin da bai san ya fita ba ya ɗan yi rashin manners din yayi yawa, ga kamshi da take bazawa tamkar namiji da alama bata da masaniyar ubangiji ya haramta irin wannan kamshi ga mace, saka Turare har ya cike wuri ga mace ba ado ba ne illa kwasarwa kai zunubi saboda duk namijin da ya Shaka har ya burge shi tamkar yayi zina ne da macen alhakin kuma baya kan kowa sai kanta.
Waya aka ƙirashi ya amsa yana ɗago fuskarsa Kasancewar suna saitin juna sai idanunsa suka sauka kan fuskarta, sallamar da yayi ita kuma muryar ya sa ta ɗago ta kalli wurin sai karab suka haɗa idanu...