TAZARAR SO

Page 1

by @nafsalkz

TAZARAR SO 
          By
Nafisa S Adam
(Nafsal KZ)

KARAMCI WRITERS ASSOCIATION
(Karamci Tushen mu'amula ta gari)
 

 
 Page 1

"Atika Atika Atika"  malam Tasi'u ya shigo gidan yana faman kira ba tare da ya yi sallama ba.  
"Na'am Malam, wannan kiran ai yayi yawa sai ka bani tsoro, kamar wani zararre". Atika da ta fito daga ɗakinta ta faɗa tana gyara ɗaurin  zanenta.
"Wato Atika ni kike kira da zararre ko, to wallahi sai dai ki nemo mai hankali ya je ya nemo muku abinda zaku ci a gidan nan" Malam Tasi'u yayi maganar cike da ɓacin rai
"Wayyo Malam kayi haƙuri, suɓutar baki ne, ai bamu da wanda ya fika".
Malam Tasi'u na harhaɗe rai ya miƙawa Atika ledar dake hannunsa yace "Ga shinkafa nan rabin kwano ce da Ƙyar ma na samota dan haka kowa yaci ya batse da ruwa".
Ledar Atika ta kalla tace "To wannan ai ko ni da yarana ba zai ishe mu ba balle na haɗa da waccan yar balaja'un matar ta ka". Atika tayi maganar tana jujjuya ledar 
"Ni dai iya abinda na iya samowa kenan a yau, dan haka a ganganɗa ayi dubara sai kuma zuwa gobe".
Atika cikin kwantar wa tace "Kaima Malam baka jin shawara da sai na ce ka haƙura ka saki yarinyar can ko ka rage wa kanka nauyi"
"Zaki iya biya na duk kuɗaɗen da na kashe a kanta? sai muyi lissafi ko yanzu kika biya sai na kaɗata tayi gaba"
Taɓe baki Atika tayi tace "shikenan sai ka zauna ka cigaba da asara dan na san tabbas dakon wahala kake ga kuɗin abinci ga na magani ga babu biyan buƙata, yarinyar nan ko rantsuwa nayi babu kaffara tana da layar zana da sihiri a tare da ita, ba zaka taɓa samun biyan buƙata a tattare da ita ba".
"To an fad'a miki ni ɗin a zaune nake, nima da kike gani neman magani nake ido rufe kuma na tabbatar wata rana zan dace"
Sake taɓe baki Atika tayi tace " Kana bani mamaki duk wari da ƙarnin rauni da gidan nan keyi a dalilin yarinyar nan neman kusan ci kake da ita, aiko sai dai ka mutu kana fafutuka".
Malam Tasi'u bai sake tanka mata ba ya fice  daga gidan.Murhu Atika ta haɗa ta dafa shinkafar ta sa musu manja da yaji suka ci ita da ƴaƴanta duk wannan abin da ake Dijah najinsu daga ɗakinta, idan da sabo ta saba domin ta daɗe da daina kuka akan jarrabawar da ta samu rayuwarta.
Ana kiran sallar maghrib Sakina tayi sallama ɗauke da cooler a hannunta da kuma waya a ɗayan hannun.

Atika dake zaune tsakar gida tare da yaranta tace "Ke zo nan", ba musu Sakina ta ƙarasa gaban Atika.
Cike da gadara Atika tace "Ba an hana ki shigowa gidan nan da waya ba, ko dan kin ga na ƙyale ki kina shigowa".
"Ki haƙuri aunty Atika insha Allah ba zan sake ba"
 "Bani wayar idan kin fito zaki tafi kin amsa, jiki a sanyaye Sakina ta miƙawa Atika wayar sanan ta shiga ɗakin Dijah.
A zaune ta tarar da Dijah ta kafawa 
Ƙafarta Idanu ta zabga tagumi.
Ƙarasawa gaban Dijah Sakinah tayi tace "Aunty Dijah dan Allah ki haƙuri yau ban samu damar zuwa da wuri na taimaka miki ba, gidan kawu ƙanin Mama naje ya sama min aiki a wani gidan saida abinci, suna biyan albashi mai kyau amma gaskiya ana cin lokaci a wajen, ko mun gama aikin wai sai lokaci yacika sannan zamu bar wajen, amma ni na kai musu ƙorafi akan ba zan wuce ƙarfe biyu ba, na faɗa musu  su rage kuɗin aikina zan riƙa tafiya idan na kammala aikina, idan kuma ba zaiyu ba to zan haƙura da aikin su nemi wani".
Hawaye ne ya zubo daga idanun Dijah "Sakina ban san kalar ƙaunar da kike min ba domin ko wani jinin nawa ba lallai bane ya min abinda kike min nagode kema Allah ya faranta miki".
Murmushi Sakina tayi tace "Idan kina kukan nan Aunty dariya kike bani kamar wata jaririya, yanzu dai bari na taimaka miki kiyi sallolin ki, ga abinci na taho miki dashi".
Bayan Dijah ta idar da Sallah Sakina ta bata abinci sannan tace "Bari naje kyamis ɗin surajo na kira shi, yau sati ɗaya kenan ba ai dressing ba naga da kin motsa ƙafar ruwa take kuma da alama tana hana ki bacci".
"Aa Sakina a dai haƙura, kar ma ki fara tunkarar Malam da wannan batun ranki zai iya ɓaci".
"Aunty Dijah kar ki damu yau mama ta bani dubu ashirin na ajje mata kuma sai azumi zatayi amfani da su, su zan ara, ana biyana a wajen aiki sai na maida mata kar ma ki min magana dan ba zan saurare ki ba, af na manta ban sanar dake ba Faisal ya siya min waya, na zo miki da ita dan ki koyamin yanda ake hawa yanar gizo amma Aunty Atika ta kwace".Fuskar Dijah ɗauke da murmushi tace "Na miki murna gaskiya Faisal da gaske yake son wannan ƙanwar kuma Aminiyar tawa, ki ce mishi mun shirya tsaf domin ba shi auren ki".
Dariya Sakina tayi mai cike da kunya hakan yasa tayi saurin ficewa daga ɗakin.
Murmushi Dijah tayi sannan ta ɗauki flask ɗin abincin ta fara ci.
Dijah na gama cin abincin Sakina tare da surajo me chemist suka shigo d'akin, bayan ya mata ya jiki ya fara duba ƙafar, Dijah ta sha azaba amma tayi juriya domin babu wanda yaji muryarta".
Gumin dake fuskar surajo ya goge, magunguna ya bata sannan yace "A gaskiya Dijah lokaci yayi da za a kaiki asibiti, ke da idanunki kinga yawan ruwan da na fitar a wannan ƙafar taki idan har ba  so kike ki rasa ƙafar nan  gabaɗaya ba shekara kusan ta uku  kenan fa, ai ƙafar ma ta miki adalci da yawa". "Nagode sosai surajo insha Allah idan Malam ya shigo zan roƙe shi idan ina da rabo sai ya amince ya kaini Asibitin"
Cike da tausayi Surajo yace "Allah ya kawo miki mafita Dijah".
Fita yayi Sakina ta bi bayan shi ta sallame shi duk da iya kuɗin magani kawai ya amsa, godiya tayi masa sannan ta dawo ɗakin ta fara gyarawa, bayan ta gama tayi wa Dijah shimfiɗa  sai da ta tabbatar ta taimaka mata ta shiga net sannan tayi mata Sallama ta fito ta amshi wayarta ta nufi gidansu.

      _____________
 Zaune yake akan yalwattacen gadonsa yayin da ya jingina jikinsa da allon gadon, tsananin ƙarfin sanyin dake ɗakin, mutum zai zata snow ne yake sauka a cikin ɗakin.
Buɗe ƙofar akai aka shigo hakan yasa Abdallah ɗago da kansa ya zubawa ƙofar idanu duk da yasan mutum ɗaya ne zai iya shigo masa ɗaki kai tsaye.
Fitilun d'akin Salim ya kunna sannan ya ɗauki remote ya rage ƙarfin Ac.
Akan sofa "Haba Diamond wannan sanyin ai sai ka cutar da lafiyarka, ni dai na rage dan ba zan iya ba, idan na tafi ka ƙara".
Duk wannan maganganun da Salim keyi bai sa Abdallah ya tanka masa ba.
Tashi Salim yayi ya sauka downstairs na gidan da niyyar zuwa kitchen ya haɗo coffee 
Cike da mamaki yake kallon mutanen dake cikin parlon ƙasa a ranshi yana tunanin yanzu fa ya shigo ya wuce bai ga kowa ba to yaushe suka shigo
Ƙarasa wa yayi gabansu ya gaida su sannan ya wuce kitchen, coffee ya haɗa ya dawo sannan ya ce "Baffa kuyi haƙuri bamu san da zuwan ku ba, da mun haɗa muku tarba ta musamman, amma yanzu zanyi muku order breakfast".Cikin halin ko in kula Baffa yace "Idan ka shiga ciki ka sanar da abokin naka muna nan muna jiransa".
"Insha Allah Baffa yanzu zai sakko ya sameku".
Cikin sauri sauri Salim yake hawa stairs ɗin har tsallake wasu yake, yana buɗe d'akin ya ajje coffee cup ɗin akan center table yace "You're in trouble mr man, your second Dad has arrived".
Haɗe fuska Abdallah yayi ya kwanta tare da jan blanket.
Waya Salim ya ɗauka ya yi order breakfast sannan ya Kalli yanda Abdallah ya shige cikin blanket gabadaya. "Please Diamond kaje kayi attending ɗinsu idan ba so kake su biyoka har nan ba".
Sake haɗe rai yayi sannan ya sauko daga kan gadon cikin tafiyarsa ta ƙasaita ya nufi bathroom.
Sai da ya kammala shirinsa tsaf sannan ya fito.
Cikin taku ɗai ɗai yake sauka daga stairs ɗin gabaɗaya hankalinsu ya koma kansa domin dining area direct yake kallon stairs ɗin.
Ɗaya daga cikin kujerun parlorn ya zauna yana danna wayar dake hannunsa yana jira su gama breakfast.
Cikin nutsuwa ya bisu one by one ya gaida Bayan ya gaidasu sun amsa Baffa Adam yace "Audullahi ni zakayi wa ƙarya kace min wai zaka zo Nigeria, kasa nayi ta jiranka amma shiru, to na sa ubanka ya biya mana kuɗin jirgi ni da Alhaji Iro abokina, kuma ga mu mun zo mu ƙure ƙaryar taka".
Ɓuya Salim yayi a bayan kujera yana dariya domin ya san ba abinda Diamond ya tsana irin a ɓata masa suna.
Da kyar Abdallah ya daure zuciyarsa yace "Baffa next week nake sa ran zuwa Nigeria, ban yi ma ƙarya ba, ayyuka ne suka riƙe ni anan ".
"Allah na tuba mene aikin da zai riƙe ka a wasan buga ƙwallo, ko ka samu aikin yi ne a nan?"
Maganar Baffa ta mugun ɓatawa Abdallah zuciya, kenan mutumin nan yana nufin bai san darajar zama star a duniyar wasanni ba" Abdallah ya faɗa  a ransa" A fili kuma ya sake maimaita zan shigo Nigeria next week Baffa".
Washe Baki Baffa yayi yana fara'a yace "Yanzu naji batu, kana zuwa insha Allah za ayi baiko a saka rana".
Rai a ɓace Abdallah  yace "Ba wannan zai kawo ni ba".
Salim yayi saurin cewa "Dama Baffa contract ya amsa zai bugawa Nigeria wasan Ƙwallon ƙafa na duniya da ake yi duk shekara, wannan karon a Nigeria za'a buga, kuma Abdallah yayi niyyar bawa ƙasarsa gudummawa a wannan shekarar".
"To ai na zata saura wata uku wasan dan naji da kunnena a wani shiri na gidan rediyo".
Salim dake ta faman murza yatsun hannunsa kamar wanda hadda ta ɓacewa ya sake cewa "Eh Baffa haka ne saura wata uku amma dole zai je ya amshi takardun yarjejeniya ya cike kuma naji yace so yake yayi training ɗin a Nigeria". 
"To Alhamdulillah zamu koma mu jira zuwan ka sai ayi baiko a tsayar da ranar biki, Kana gama wasan sai ayi ka dawo nan tare da matarka".
Shiru na ɗan lokaci ya ratsa parlon, can Baffa yayi gyaran murya yace
"Yauwa idan ka tashi tafiya Nigeria ka biya can ƙasar labanon ɗin ka sanar da Mahaifiyarka da danginta idan akwai masu ra'ayin zuwa sai su sanar damu mu tanadi masauki".
Duk wannan surutan da suke Abdallah yayi shiru kamar ma ba dashi suke ba.
Kwanansu uku suka tattara suka koma Nigeria bayan Salim yayi musu alƙawarin kawo Abdallah gida.

Dijah na zaune a inda take cikin ɗakinta kamar kullum tana karanta littafin "A cikin ido" da Sakina ta samo mata domin rage wa kanta zaman damuwar da ya sameta, wayar Sakina ce tayi kuwwa dan haka Dijah ta ajje littafin ta ƙwalawa Sakina kira
Tsame hannu Sakina tayi daga cikin ruwan wankin ta goge  sannan ta ƙarasa ɗakin Dijah
Ganin wayarta na ringing ya tabbatar mata da wannan ne dalilin kiran  Dijah.
wayar ta ɗauka ta ɗaga kiran sannan ta samu waje ta zauna".
Sam Dijah bata jin mai suke faɗa amma dai taji Sakina tana cewa "A gaskiya a yanzu Aunty Dijah nake wa wanki sai dai ka zo bayan maghrib ko a haƙura sai gobe.
Dijah na ƙoƙarin yi mata magana ta ga ta miƙe cike da shauƙi tace "Dan Allah, kana nufin favourite ɗinka Diamond zai shigo Kano a yau, a gaskiya naji daɗin hakan Allah yasa ka samu damar ganinsa, ai yau na yafe maka zuwa zance,
tana gama magana da Faisal ta juyo cike da murna don sanar da Dijah sai ta lura Dijah tayi  zurfi a tunani.
Littafin dake hannun Dijah Sakina ta zare wanda hakan ya dawo da  ita daga tunanin da ta tafi.
Aunty Dijah lafiya kike irin wannan zurfin tunanin ko akwai abinda ke damun ki bayan wanda na sani.Murmushi Dijah tayi "aa kawai dai gani nayi yau kin sake har da waya a gidan nan"
Dariya Sakina tayi tace "Ai naji daɗi sosai da yau Aunty Atika ta fita unguwa dama kar ta dawo".
Da sauri Dijah ta katse Sakina da cewa "Ai ba zamuyi wannan fatan ba sakina nan gidan tane kuma ni na tarar da ita, mu bar wannan maganar"
"Yauwa naji kamar ke da Faisal kuna maganar Abdallah zai shigo garin Kano ko? Dijah ta kawo maganar dan ta kauda waccan hirar, Ba ta jira amsar Sakina ba ta sake cewa kenan wannan shekarar Ƙasarmu tayi nasarar sayen ɗan kwallo mafi tsada".
Cike da mamaki Sakina ta samu waje ta zauna tare da faɗin "Dama Aunty kin san Diamond?, kice kema 'yar gani kashe nin ball ce, aiko idan Faisal ya sani zai ta bada update ina sanar miki"
"Naso ball sosai a zamanin da, amma banda yanzu".
Yanzun ma Aunty dan baki da lafiya ne ga rashin kwanciyar hankali irin na gidan nan" Sakina tayi maganar cike da damuwa a muryarta.
Malam Tasi'u da ya shigo gidan ya wuce banɗaki ba tareda sanin su ba ya gama uzirinsa ya fito daga banɗakin yaji Sakina na faɗin ga rashin kwanciyar hankali a gidan Butar ya ajje ya ɗaga labulen ɗakin Dijah yace "Sannu masu kwanciyar hankali, to ko yau da safen nan ma sai da aka raba faɗa tsakanin tsohuwarki da abokiyar zamanta, ni wallahi ba dan ba mai iya aikin da kike na kula da Dije da tuni na miki iyaka da gidana don na fuskanci ke munafuka ce kuma zaki iya raba aure, ki kiyaye ni na faɗa miki" 
Haka Malam sule ya saki labulen yana cigaba da bambamin faɗansa
Hawaye suka ciko a idanun Dijah "Dan Allah Sakina kiyi haƙuri kada ki fushi".
"Kar ki damu Aunty Dijah ina nan tare da ke duk runtsi".  
Hawayen da suka zubo mata ta goge tare da sakin ajiyar zuciya.

Comment and share
Nafsalkz