26&27
Episode 26&27📲
***
Jumma'at Kareem to all Muslim ummah🕋📿 may Almighty Allah accept our silent prayers🤲
بسم الله الر رŘمن الر Řىم
Da sunan Allah Mai rahma Mai Jin Kai
Satin su mubeena 1 kenan a America wanda ita har cikin rai bataso su kai haka ba saidai zugin da ƙawayenta keyi mata yasa ta mance da batun dawowa kodan taga yadda yaƴan nata suke amma deep down tana jin kewan su fiye da tunani. Yau de tunda ta tashi take marmarin Nigeria aiko bata biɗa shawaran kowa cikin ƙawayen nata ba sai shamsiya inda take gaya mata tana son ta koma Nigeria hakanan, gashi tunda suka zo kota kira AS bai ɗauka "banda abin ki mubee taya ma za'ai ya dauka bayan kin fito ba tare da izinin shi ba! Yanzu ba fata nake miƙi ba idan wani abun ya same ki ko kuwa kika mutu mi zaki cewa Allah? Wallahi ya kamata ki dawo daga rakiyar su zee, nidai shawara nake baki idan kin ɗauka daidai ne in akasin haka shima daidai, wallahi ki aje mugun huɗuban dasu zee ke yi miki ki koma ga Allah ki riƙe mijinki da ƴaƴan ki! Yanzu yadda kikeyi inda ace mijin ki mai niman mata ne mi kike tunani?" Hmmmm ta sauke ajiyar zuciya wani zuciyar na ƙokarin karban maganar shamsiya saidai hakan ya kasa yiwa "Ni dai ba wannan ba yaushe zamu tafi" "daman ai ke ba gaskiya kike so bah sai mu shirya gobe mu tafi shawara karki sake ki faɗawa su zee ehem" ita da kanta tasan idan ta faɗawa su zee tofa ita da gida sai baba ya gani amma sai ta amsa mata da "toh mama" duk dariya sukai, shirya kayansu sukai suka saka cikin waldrop dake a ɗakin dan kar sauran ƙawayensu suyi tunanin wani abin.
sosai take son Shamsiya saboda idan tana ƙokarin kaucewa ita ke taro ta idan anyi Sa'a bata yi nisa bah,nan dai suka zauna suna ta fira wanda a ciki shamsiya ke dan bata shawarwari wanda zata bille shima cikin hikima take yinshi. Shamsiya dai ka barta da halinta amma tsaf tasan abu mai kyau da akasin haka, haka dai ta cigaba da bata shawarwari cikin hikima wanda a lokaci da ka kalle su zaka gane ƙawance ne na tsakani da Allah ba kaman su zee dake mata hassada bah...
_____________tunda AS yake zuwa bai taɓa zuwa ya haɗuwa da eely a waje ba dan kullum tana cikin ɗaki lunƙume, ko a wajen aiki bai taɓa ganin ta ba, haka kuma bai taɓa jin muryan ta ba gashi yanzu satin su Anwar daya da kwana biyar sun shaƙu da eely sosai kallan uwa suke mata, hakan da suke gwada mata bai hana ta nuna musu darajan mahaifiyar da ta haife su ba,kullum ƙara chusa musu kaunar mahaifiyar su take,a yanzu kam su kan barta ta tafi aiki haka idan ta dauko Anwar shima yana barinta ta koma sun ƙara wayau bata kuma barin shi yana fita waje, saboda gudun haka ta siyar mishi Kayan wasa.
Yau ta kasance weekend wuraren magrib zaune suke a tsakar gida su duka harda umma wanda zuwan ta kenan ba jimawa,eely kwance take ta daura kanta a kan ƙafafun umma tana game da wayar goggo, Anwar kuwa yana a ta gefe yana buga ball,su goggo da umma sai fira suke inda Ruqayyah take wasa da Anam ta kan ɗan saka baki a firar tasu. "eely ki shirya muje gidan su Anty Maryam mu karɓo tsara ban mu tun kafin ta gama rabar dashi kin dai san halinta"
"Da zata wuce na wa kika bata"
"Iyeee lailai ma aiko saidai kar tayi tsaraban! Ai idan batayi dan Allah ba zatayi na dole dan tana hana Ni zan jido ne na bar gidan"
"Sata" amsar da eely ta bata kenan wanda hakan ya tunzura Ruqqy tace dillaliyar ce Ni karshen sata" ɗan guntun murmushi tayi tana ɗan tabe baki haɗi da faɗin "kayan mu dai ɗaci ne dasu eh......ai bata ƙarkare magana ba Ruqqy ta taso a harzuƙe tayi kanta ganin haka ne yasa eely miƙewa da sauri ta faɗa ɗaki hadda su banko kofa, bugbuga ƙofa Ruqqy ta rinƙa yi tana ta kumfan baki su umma kuwa dake sun san halin su kana shiga tsakani zasu watsa maka ƙasa a ido shi yasa suka hita batun su, gajiya tayi da buga ƙofan ta dawo ta zauna, daga cikin ɗaki kuwa jin da tayi Ruqqy ta daina buga ƙofan ne sai ta leƙo ta window tace "dan Allah dillaliya ɗan miƙo min wayar umma" ta ƙare maganar cikin rashin son magana. banza tayi da ita sai Anwar ne ya ƙaraso wajen da kayan kwallon sa a jiki "umma waya in kai wa umm na" ba musu kuwa tace "karɓi maza miƙa mata" yana nufan ƙofan ɗakin sai ga sallamar AS bashi izinin shigowa akayi sannan ya ƙaraso har duƙe ya kai yana gaisar dasu umma inda suka amsa masa da kulawa da tambayan shi iyali nan ɗin ma ya amsa da Alhamdulillah, Ruqqy ma ta gaisar dashi shima ya amsa da kulawa yana kai zaune kan tabarman da ta shimfiɗa masa. Ruqayya "tashi ki miƙo masa furar sa a ɗaki" "Toh goggo" dakin goggo ta shiga ta dauko masa furan cikin kofin silver ajewa tayi a gaban sa, cikin jin daɗi dan yanason fura sosai yayi mata godiya.
"Umm ki buɗe kofa nine ba anty bace" cewar Anwar da yake ta faman bugun ƙofa dan da farko baiyi magana ba sai yanzu yayi ita kuma bata buɗe ba tana tunanin ko Ruqqy ce, "boy kai ne" "Yes umm open the door"
Abin mamaki wai Anwar yana ganin shi amma ya nuna kaman bai san shi ba, hankalin shi gaba ɗaya yana kan umm ɗinsa,burin shi ta buɗe masa ya samu ya miƙa mata wayar. Shi yasa AS ya kafe wajen da ido yana fatan yaga wannan umm ɗinsa,tunanin shi katsewa yayi ganin an buɗe kofan ɗakin saidai baiga kowa ba, Anwar kuwa yana shiga ta rufe kofan da key yadda yake, Ruqqy kuwa cikin ɗan ɗaga murya yadda zata ji tace "mutun ga tsoro ga tsokalan faɗa ai yau saidai karki fito daga ɗakin" oho eely yi tayi kaman bata jita ba ta share, "umm ga waya na karɓo wurin umma" ya ƙare maganan da miƙa mata wayar karba tayi tana shi mishi albarka,kiran sallar magrib ɗinda akeyi ne yasa ta canza masa kaya zuwa jallabiya na yara da niyan idan ta idar da salla tayi mishi wanka tunda bai samu tayi mishi na yamma ba, wa ya boy muje ayi alwalla muyi salla "noo yau da papa zani masallaci yazo" "ok jeka Allah ya tsare" Saida ya buɗe kofan har ya fita sannan ya amsa da "Amin bye" ganin fitowar shi ne yasa AS nufan ƙofa wanda ya riga da yayi alwalla,Saidai da sauri Anwar ya dawo kaman yayi mantuwa a bakin ƙofan ɗakin ya tsaya yana "umm mi zan dawo miki da tsaraba?" Cikin dariya tace "komi ma inaso boy" bai bata ansa ba ya fice inda ya samu papan sa a inda ya barshi yana jiran shi, duk Maganar da Anwar ya faɗa a kunnin sa, kama hannun shi yayi suka fice zuwa Masallaci, bayan an idar da salla ne suka fito "Papa" kyalesa yayi kaman bai ji kiran nashi yake ba, "papa" "mene"
Babu ko kunya tuna bai gaisar dashi ba sai cewa yayi "papa ka kaini nayiwa umm tsaraban masallaci" yi yayi kaman ba dashi yake ba "papa pls" "muje" mota suka nufa shiga duk sukayi sannan ya bawa mota wuta suka bar arean,kayan su maƙulashe ya dinga jidar mata shi kuwa AS binsa kawai yake saida ya gama daukan abinda zai ɗauka ya juyo yana papa na gama gani yayi duk babu kayan arziƙi a ciki sai na kwaɗayi shi kuma haka kawai yaji yana buƙatan siyan mata wani abu kodan kula mishi da yara da take, jan hannun Anwar yayi suka nufa wajen Saida wayoyi ya dauka iphone 11 guda biyu sai bangaren tulare ma Saida ya zaɓo kamshin da yayi masa,wajen biyan kuɗi suka ƙarasa inda akayi masa calculating ya fidda ATM ya biya nan suka fito da ledoji,
Koda suka isa anguwan su goggo isha'i sukaji ana kira sai basu shiga ba sai da sukai sallar sannan suka shiga gidan sallama dauke a bakin AS Anwar kuwa umm ɗinsa ya hau kira wai tazo ga tsaraban masallaci, da yake duk suna tsakar gida saidai wannan karan umma ta koma gida goggo da Ruqqy ce sai eely da fitowar ta kenan, amsa masa tayi da "na'am boy mu ga" da sauri kuwa ya iso gareta yana zazzage ledar daukar wayar goggo tayi ta kunna haske dan basu da light mi zata gani kuwa kayan su chocolate ne gasu nan kala kala, kallan shi tayi face ɗinta ba wasa tace "wa ya siyar maka duk wannan" ta ƙare maganar da nuna su chocolate ɗin, "papa ne ya kaini shine na siya miki" "awwwn that's my boy Allah yayi maka albarka but don't try it next time here?" "Bazan kuma ba" "yawwa gud boy" "yaya barka da dare" cewar Ruqqy amsawa yayi shima a daƙile, ita eelham sai yanzu taji muryan shi daman takan ji muryan nasa saidai bata taɓa ganin shi ba, ba tare da ta ɗago ta kalleshi ba tace "ina wuni" daman tunda suka shigo idon shi ke akanta, jin tana gaisar dashi ne sai ya dauke kai cikin basarwa yana amsawa da "lafiya" gefen zuciyarsa yana mamakin ta wai itace umm ɗin su Anwar. Ya kice tunanin yayi a rai kafin yace "Ruqayyah gashi" tashi tayi ta saka hannu biyu ta ƙarɓa duk da baiyi mata bayani bah hakan ya nuna nata ne godiya sosai tayi mishi kamar tasan abinda yake ciki,tashi eelham tayi dauke da Anam da tayi bacci tini ta shige ɗaki bata cewa komi bah, da kallon gefen ido ya bita yana mamakin ta,shigan ta ba jima shima yace zai wuce yana sallaman goggo,Saida ya fita sannan Ruqqy ta buɗe ledar da ya bata,farin ciki sosai tashiga yi da ganin abin arzikin da ya kawo masu nuna ma goggo tayi haɗi da faɗin goggo duba kiga yaya ya siyar mana wayar zamani ga kuma tularen nida eelham"
"Masha Allah kun gode kwarai da gaske Allah ya ƙara buɗi Ahmad dai baya gajiya Allah ya saka nasa da mafificin alkhairi" "Amin ya Allah! eelham fito ga fa abin arziƙi da zafin ta ya sauka"cikin nutsuwar ta ta fito daga ɗakin "lafiya zaki cikawa mutane kunni" "dole fah in cika abin arziki ne ya same mu! Yaya Ahmad ya siyan mana waya ni ɗaya ke ɗaya ga kuma tualare" kwarai da gaske tayi murna da haka amma a zahiri sai ta taɓe baki irin ba'a burge ta bah. mi wani kika tsayawa mutane a kai kina wani ya mutsa baki kaman Kinga kashi,ganin goggo zata fara wanan faɗan nata ne sai ta kai zaune tana kallon wayar miƙa mata Ruqayyah tayi wai ta zaɓi ɗaya ai dan ita aka siyo,dan mƙararren harara ta watsa mata sannan ta ɗauke kai "kema dai Ruqayyah Allah ya ƙara banda abin ki inace ke ya miƙawa wayar, banji yace keda wata can daban bah" cikin fara'an ta tace "goggo haka yake nufi! Kinga ai bazai siyo waya biyu dan mutum ɗaya ba" "wannan kuma ku kuka sani ɗauki wanda ranki yake so ki zaɓa ki darje" "Yanzu kuwa goggo" nan ta zaɓa wanda take so shima bawai ta tsaya ƙare musu kallo bane, miƙawa eely tayi tana cewa "ga naki Allah yasa a kashe lafiya" ƙin karɓa tayi tana faɗi "ba buƙata ko nace inada buƙatar waya ne?"
"Toh nidai ba Ni nasiya wayar ba dan haka bani zaki faɗawa ba,kijira wanda ya siya idan yazo saiki gaya masa baki buƙata"
"Ai kuwa dai kin bata amsa dai-dai da ita" cewar goggo,jin suna son suyi mata chaaa a kai yasa ta miƙe ta shige ɗaki ganin haka ne Anwar ya bita suka shige ciki dan su kwanta su hutawa rayuwar su....
Ba daɗewa da shigar ta goggo suka suka miƙe suka nufi ɗaki (asuba tagari)....
___________daga wajen goggo gidan Ummi ya nufa knocking yayi a ƙofan parlon yana tsaye ba jimawa aka buɗe ƙofan wacce ta buɗe ƙofan ne ta leƙo dan ganin waye, ido huɗu tayi da ƴaƴan ta cikin sake murmushi tace yaya "ina wuni" "lafiya" ya amsa a daƙile dan shi ba ma'abocin son magana bane, jayewa tayi nan ya samu daman shiga ciki inda ya tadda Ummi a zaune ga mubeena a gefen ta, "Ummi ina wuni?" "Lafiya qlau,ya aikin?" "Alhamdulillah"
"Daman ai yanzu nake shirin nayi kiran ka" gyara zama yayi yana mai cewa "gani Ummi" ba wasa sam a fuskarta tace "mi yasa da mubeena tayi tafiya idan ta kira ka baka ɗauka?" Lallai kam wato har mubeena tana da bakin kawo ƙaran shi wurin mahaifiyar shi, cewa yayi "Ummi hakan bazata ƙara faruwa bah insha Allah" "tambayar ka nayi mi yasa take ta ƙira ka amma kaƙi ka ɗauka?" Shiru yayi baice komi bah, ganin haka ne sai Ummi tace "mi ya haɗa ku kikace?" Tayi maganar tana kallon mubeena, ita kuwa babu ko kunya ta ƙara maimaitawa "wai akan tayi tafiya bada izinin shi bah shiyasa yake fushi da ita amma wallahi ummi nayi nadama" faɗi yake lailai ma mubee wato tasan tayi laifi ta kuma san bata da gaskiya shine ta wuto nan gashi babu ko kunya ta faɗi abinda tayi,shi dai abinda yasa yake ƙara sonta kenan,bata iya karya ba koda ita take da laifi Indai magana ya tashi ta kan faɗi gaskiyar abinda ya faru yanzu ɗin ma shiyasa yaji zuciyarsa tayi sanyi,jin kuma tayi nadama inda ace batayi ba bazata buɗe baki tace tayi bah, "tunda ta gane laifin ta har tasan tayi kuskure kayi haƙuri komi ya wuce". "amsawa yayi da insha Allahu komi ya wuce" cikin sauri mubee tace "ina son a dawo mun da yara zuwa gobe dan Allah Ummi ki saka baki dan zai iya cewa sai ya hora ni! kuma ni ba zan gane gidan ba" "Toh Ahmad ka daiji idan Allah ya Kaimu sai aje a dauko su" cikin rashin damuwa ya amsa da "Allah ya Kaimu" 'ku tashi kuje dare na daɗa yi" miƙewa sukai suna sallamanta, buɗe mata front sit yayi sannan ya zaga ya buɗe ya shiga yana ta da motar suka bar gidan,da yake da anguwan su dana Ummi ba wani nisa ne dashi bah, a ƙofan gate ɗinsu ya danna horn mai gadi yazo ya bude da sauri Saida ya tsaya suka gaisa da gate man, sannan suka shige ciki da mota, parking yayi, ya fito ya buɗewa mubeena kofa suka nufa cikin gidan key ya ciro ya buɗe kofan falon, dan ya bawa masu aikin gidan hutu amma mata, shiga sukai yana kunna wuta ko ina yayi tar da haske ba tare da yayi mata magana ba ya riƙo hannun ta suka hau sama zuwa ɗakin baccin su...
_____a zabure ta tashi bakin ta da addu'a Kallan su Anwar tayi ganin dai duk suna a gefen ta yasa ta sauke ƙatuwar ajiyar zuciya tana kuma ƙara recalling mafarkin da tayi, gani tayi AS ya zo zai tafi dasu Anwar jin haka da tayi ne sai ta fito a zabure daga ɗakin tana dan Allah karka tafi dasu ina sonsu,dan Allah, har zubewa kasa tayi tana roƙan shi amma ina kama hannun Anwar yayi ga Anam a kafaɗan shi haka yasa kafa ya bar gidan ko tausaya mata baiyi bah, mtwsss tsaki tayi tuna mafarki ne ba gaske bah, addu'a tayi tana kara komawa bacci,
Jin ana buga ƙofa shi ya tasar da ita daga baccin da ya kwashe ta ji tayi gaban ta ya faɗi innalillahi kawai ta shiga nanatawa kafin ta miƙe cikin sanyi ta buɗe kofan,ganin goggo ne sai taji ta ɗan samu natsuwa harda su sauke ajiyar zuciya, "lokacin sallah yayi kiyi maza kizo kiyi alwalla kar lokaci ya ƙure, yau duk mun makara"
GaÉ—a mata kai kawai tayi dan bata jin zata iya magana. Fitowa tayi ta dauki buta ban É—aki ta fara shiga sannan da fito ta daura alwalla ta koma É—aki
Yau bata da karfin fita yin aiki shiyasa ta zauna a nan inda tayi salla, goggo kuwa bata leƙota ba ta dauka ko ta koma bacci ne shiyasa ta kyale ta, tana nan zaune a ɗaki tayi zugum har rana ta fara fitowa jin muryan goggo tayi tana "yau Khadijah lafiyan ta kuwa zata tayin bacci har yanzu goma ake biɗa fah, Ruqayyah zo ki dubota" tashi Ruqayyah tayi ta shiga dakin ganin ta tayi zaune a kan sallaya ganin haka ne yasa ta koma bata ce mata komi ba dan ita ta dauka wani abin take dake ta bawa ƙofan baya, "goggo karatu take bata idar bah" "oo to Allah ya taimaka" da Amin ta amsa
Elham ba ita ta fito ba sai wuraren sha biyu shima dan goggo ta matsa mata ne, daman goggo tini ta É—auki su Anwar tayi musu wanka dan ganin maman nasu sai a hankali, bucket ta dauka taje bakin rijiya ta É—iba ruwa ta nufi ban É—aki dan yin wanka, koda ta fito sama sama ta shafa mai dan garin yau akwai zafi, da niyan ta ta fito tsakar gidan amma ta fasa ta koma tayi zaune kan katifa,
AS da mubeena ne suka shigo gidan goggo ta barma ta shinfiÉ—a musu tana yi musu sannu da zuwa ruwa ta kawo musu pure water, ba musu kuwa AS ya dauka yasha, mubeena kuwa ko kallo, bayan sun gaisa AS yake faÉ—a mata sunzo É—aukan su Anwar ne.
Elham da take cikin ɗaki saida taji gaban ya faɗi kardai mafarkin da tayi shi zai faru "ya Allah kasa ba haka bane" can waje kuwa saida goggo taji wani iri dan duk sun saba da yaran sosai saidai babu yadda suka iya masu ƴaƴa suna bukatar abunsu, "Allah sarki zamu sha kewa kuwa bara na dauko su dan Anwar yayi bacci saidai Anam idanun ta biyu, ɗaki ta shiga ta dauko Anwar,miƙawa AS shi tayi a hankali dan kar ya tashi, komawa tayi ta dauko Anam dake ta wasan ta na yara tana haɗo musu da kayansu,koda ta fito mubeena ce ta karɓi Anam,AS kuwa godiya yayi mata sosai yana aje mata rafan yan dubu dubu guda uku, da sauri goggo ta katse shi da faɗin "Ahmad ɗauka tun muna sheda juna" dan Allah goggo karkice a'a" na riga da na faɗa ba zan dauka bah" "goggo albarka muke nima" jin haka ne sai ta ɗauki rafa ɗaya ta cire dubu daya a ciki ta aje masa sauran a gaban shi tana Allah yayi albarka na gode kwarai da gaske, babu yadda baiyi da ita ba akan ta karba amma ta nuna wannan ɗin ma ya isa,babu yadda ya iya haka ya dauki kuɗin sannan ya miƙe, ganin haka ne itama mubeena ta tashi sallamar goggo sukai suna ficewa daga gidan.
Idanun eely sun kaɗe sunyi jawur kaman rushe kuka take son tayi saidai ina hakan yaƙi ya faru dan ta riga da tayi hannun riga da wannan hawayen a lokacin, jin wani zafin sa na taso mata tayi dole taji zafin sa taya za'ayi jiya yana gidan amma ya kasa gaya musu zai ɗauki su Anwar sai da rana tsakan nan, inda ta dauki albashi ta cire su kenan daga babin rayuwar ta zata manta tayi rayuwa dasu tunda tasan ba ƙara haɗuwa zasuyi ba, tace koda ta ga su Anwar ɗin zata dauke su kaman da, nan ta rinƙa lallashin kanta har ta ɗan fara sauko wa, lokaci ɗaya kuma kewar su mufeeda ya tasar mata tabbas tana son su dan sun dauke ta a matsayin yar uwar su ta jini,cikin wani hawayen da bata san da zuwan su taji yana zubo mata a fuska dan tuna rayuwar da sukai tare su shida cikin so da kaunan juna, bawai ta manta dasu bane cikin babin rayuwar ta ba a'a kullum Allah keda kullum da begen ƙara haɗuwar su take,da ace tana da numbern su da ta biɗe su sai dai yan zu bata da numbern su dan wayar Tata a chan gidan su ta barshi, share hawayen tayi tana ƙara jaddada wa kanta kuka ba nata bane zata ci gaba da maida komi ba komi ba insha Allah.Tashi tayi tana zaran hijab dan so take ta je ta gaida umma
Goggo ma dai ta shiga kewar su Anwar amma sai ta danne dan kar taƙarawa eelham damuwa, saidai mi lokacin da eely ta shigo sallamanta akan zata gidan umma sai taga fuskar nan kamar yadda yake a kullum mamaki tayi dan batayi tunanin haka bah,ita duk a nata tunanin eelhan zata sakawa kanta damuwa sai taga akasin haka, katse mata tunani tayi da faɗin "na tafi gidan umma" a dawo lafiya tayi mata ita kuma tana ficewa daga gidan...
__________zanga-zanga Anwar ya hauyi da ya tashi yaga ba gidan goggo yake ba kuma gashi baiga umm É—insa ba,aifa nan ya hau kuka hadda birgima wai sai an maida shi gurin umm É—insa hadda su ihu,saida mubeena ta dauko cable charge tace zata dake shi sannan aka samu salama dan ita ta É—auka ko goggo yake kira umm, AS da yake zaune yana jin su bai ce musu komi ba daman yasan idan Anwar ya tashi akwai daru, a nan da yake kwance wani sabon bacci ya kwashe shi
A takaice dai Saida Anwar yayi sati ɗaya yana kiran a kai shi wurin umm dinsa kafin yazo ya haƙura ganin ba kai shi za'ayi bah.
Elham ma dai kewar Anwar na nan daram babu abinda ya rage daga ciki saidai ta kan danne sosai, a tsakanin ne taje school ɗinsu Anwar ta gayawa antyn shi zata daina zuwa daukan shi.............✍🏻