28&29
Episode 28 & 29📲
***
بسم الله الر رŘمن الر Řىم
Da sunan Allah Mai rahma Mai Jin Kai
______yaushe zamu tafi Abuja Kinga yau meeting sauran kwana uku kuma zuwa yanzu nasan kowa ya hallara suke kira na suna gaya mun gasunan duk sun zo"
"Kina da gajen haƙuri auta inda kin kwantar da kinji! Yanzu sai kije ki haɗa kayan naki flight ɗin mu 8oclock pm zai tashi yau"
"Yeeeees bara naje na haÉ—a kaya dan idan na tafi ba dawowan yau ba dan naji ihsan tace anan zatayi hutu! Kinga daga nan sai nayi mata wayau ta biyo ni mu dawo nan idan yaso sai a nima mata transfer ta dawo nan da service É—inta Koh?"
"Cikin dariya tace kin ko yi mata wayau Allah ya shirya ku"itama dariya tayi tace "su fa basu cika zuwa nan ba sai in mune muka je chan ai gara nayi ta masu wayau suyi ta zuwa"
"Auta kenan Allah ƙara wayau to amma ni dai banga wayau nan ba" tashi tayi tana zumbura baki wai ance mata batada wayau,ganin haka ne sai Ummi tace "zauna kiji albishir" ba musu kuwa ta zauna tana jiran taji
"Ummi ina jii"
"Mi kike ci na baka na zuba? Daman Hajiya Mama zata dawo nan da zama ita dasu Hafsah" wani tsalle ta daka tana jin daÉ—i tace habawa shagali ummi kice ba zama grandma zata dawo nan! Toh Ummi yaushe zasu dawo kuma wa zai je dauko su?"
"Sai mun dawo daga Abuja shi yasa ana gama meeting washegari gari zamu dawo koda yake kince ke a chan zaki zauna Koh?"
"Da sauri tace wane niiii ai na fasa tini kowa ya zauna a gidan su" cikin É—an dariya tace "oo se yanzu kikasan haka Koh?" Tashi tayi ta nufa upstairs tana ba haka take nufi bah....
________fitowar su daga office kenan suna jiran Umar ya zo dan yace shi zai maida su,wanda a yanzu soyayya mai karfi ya ƙullu a tsakanin sa da Ruqqy,wanda a shekaran jiya iyaye suka zo gaisuwa zuwan da zasu ƙara yi na saka rana ne, "Mallama nkfa na gaji da tsayuwa fah?" Cewar eely tana hararan ta "wai ko dai na juya na goya ki ne?" Dukan wasa ta kai mata tana ɗan guntun murmushi, kaucewa Ruqqy tayi tana "a'a wallahi karki ragen sadaki ehem"
Itama É—in cikin wasa tace "yar is kawaii" "ke kuma na gaba da is bah"
Harara ta kai mata tana dauke kai da kuma É—an motsa lips É—inta alamar akwai abin faÉ—i saidai bakin ya kasa furtawa,É—an wannan maganar da tayi har ya saukar mata da ciwon kai,
"Ooo Allah alhamdulillah mungode maka ya Allah da kayi mu masu magana" tsaf eely tasan da ita Ruqqy keyi amma sai ta hita batun ta
Meenal dake ta kallon su tun ɗazu sai taji sun burge ta sosai shi yasa ta tsaya ta rinƙa kallan su ba tare da sun sani bah gefe ɗaya kuma tana mamakin wannan lamarin, ƙaraso inda suke tayi tana sauke glass ɗinta da yi musu sallama, sister ku shigo na rage muku hanya naga wajen shiru babu abin hawa, da yake Ruqqy ta kan haɗu da ita idan suka fito salla shi yasa ta ɗan waye ta, daukar wayar ta tayi kiran iphone wanda AS ya siya musu,numbern Umar ta kira tace mishi su sun wuce sun jira shi amma shiru,haƙuri ya bata sannan yace suje zaije gida su haɗu amsawa tayi da ok tana yanke wayar, eely muje Kinga idan muka tsaya anan ba abin hawa zamu samu ba Kinga yamma tayi, ba tare da ta kalle ta ba tace "sai nazo" babu yadda batayi da ita ba amma fir taƙi hawa dole ta bawa meenal haƙuri ta wuce wanda ita ma bata ji dadin hakan bah.
"Aiko kowa yaji a jikin ta Allah kuma yasa karmu samu abin hawan inga karshen iyayi" ƙin tanka mata tayi ta cigaba da tafiya kaman bazata taka ƙasa ba. Hadari ne sosai a garin wanda ya taso lokaci ɗaya machines dasu mota sai gudu suke basu son ruwan ya taɓa su. Kinga abinda kika ja mana Koh dan Allah da ace mun bita ai da ba haka bah" "na riƙe ki?"
"Ai da na wuce nan zaki gane cewa kin riƙe ni" taɓe baki tayi tana ɗauke kai,sunyi tafiya ba mai nisa ba suka ji horn daga bayan su,babu wanda ya juya a cikin su, motan ƙara matsawa kusa da su yayi ana ƙara danna musu horn nan ɗin ma babu wacce ta duba, ji tayi ance "Ruqayyah" nan kam Ruqqy ce kawai ta juya dan bata gane muryan ko waye bah, koda ta juyo da driver tayi arba da gani shi yayi kiran nata,eely kuwa bata tsaya ba ta cigaba da tafiyanta tana jin daɗin weather ɗin
Kafin Ruqqy ta samu daman cewa komi AS ya sauke glass ɗin gefen shi ba tare da ya ɗago ba yace "shiga muje" " yaya ba Ni ɗaya bace ni da Elham ne" b tare da wasa a fuska ba ya ƙara faɗin "shiga" wannan karan kam ba musu ta buɗe front sit ta shiga ba da son rai ba dan bazata so ta wuce ta bar ta ita ɗaya ba ga magrib ya kawo kai, tana shiga kuwa driver yaja motar suka bar wajen.
Duk da eely bata juya ba tasan Ruqqy ta shiga motar Ba tare da damuwa ba ta cigaba da tafiya ga hanyan shiru babu abin hawa ko ɗaya da ke gittawa sai motocin da suke wucewa da gudu kaman zasu tashi sama, wani mota ne yazo ya wuce ta gaban ta da gudu a hankali kuma taga motan nayin reverse yana yowa baya, "DEJART" tsam tayi tsaye nan gun da take,shi kuma na motan yana ganin haka sai ya fito cikin sauri ya ƙaraso inda take da murmushi a face ɗinsa, "tabb rai kanga rai daman" cikin ɗan murmushi da gani ta saba da wannan ɗin tace "taya za'ayi su gani kuwa" "barnan kin rai na ni da yawa"itama cikin haɗin fuska tace toh"ni yaushe na raina ka?"dariya yayi haɗi da faɗin halin ki na nan ya kwana dubu, sai alkahiri sir"ta ƙare maganan da son danne dariyan ta "saniya ce ba sir ba" haɗi dayin kwafa, "nidai shiga muje kuma sai kin gaya mun yadda akayi kika bar gari babu notice ba irin niman da banyi Miki bah ga wayar ki kashe baya shiga mufeeda ma na kira layinta shima kashe"
"Wannan bayanin haka sir"
"Ki raba ni dace mun sir tun kafin a jimu! Kinga eely kizo ki shiga muje Kinga garin nan da hadari kuma idan ruwan nan ya kufce ba tsanewan yanzu ba" ba musu kuwa suka isa wajen motan miƙa mata key yayi yace ita zata tuƙa yayi missing ɗin tuƙin ta, "ba wani wayau dai zakayi min" "haba dai mutuniya kema kinsan ba wannan ki dan tausaya min hannu na ne suka gaji"
"Toh Allah ya ƙara sauƙi idan da gaske ne" ta ƙare maganar da karban key dake hannu shi "karya nake shikenan eely! Badai kin raina ni ba?" "Sharri!Ni yaushe akayi haka"
"Ban sani ba" cikin taɓe baki kaman ba eely mara son surutu ba tace duk hanyan da ka sani su bace ma" pointing ɗinta yayi da hannu ita ma ganin haka tayi yadda yayi har haɗa baki suke inda eely tace tare da kai shikuma yace tare da ke lokaci ɗaya kuma suka kwashe da dariya.
Har zata bude mazaunin driver yace "mallama wait wait" tun kafin yayi magana dan ta tuna yadda sukeyi sai taje ta gefen shi ta buɗe mishi ya shiga sannan ta kulle ita ma zagawa tayi ta ta buɗe ta shiga sannan ta kulle daman haka sukeyi inhar dai zasu shiga mota ɗaya, ɗaya ke budewa ɗaya idan an kai wajen da zasu sai wanda ya bude da farko shi za'a budewa, kaman yanzu idan sun isa shi zai budewa eely ƙofa
Driving take slowly kaman bata son yi sai firan su suke sha da gani sun shaƙu da juna "eely ban tambaye ki ba?" "Inajin ka"
"Wai ina mallam É—an ladi ne?" Harara ta sakar mishi tana faÉ—in "kamanta dai mallam É—an gambo dai"
"Daga tambaya sai masifa Allah ya baki haƙuri to!amma ni dai nasan masoyin ki ne" "Allah ya kiyaye" daidai tanayin parking a ƙofan gidansu, kallan shi, zuwa yanzu ta gaji da surutu ba tare da tayi mishi magana ba ta dai yi mishi alama da ido alaman sun kawo,da yake yasan halin kayanshi ya buɗe kofa ya fita amma bai kulle ba, zagawa yayi gefen ta ya buɗe mata kofan ta fito ta koma side ɗin da ya fito kaman wasu yara suna haɗa baki but slowly sukace 123 suna kaiwa 3 suka buga kofan a tare suna dariya, "na riga ki", "ka dai riga kanka amma nidai nasan nine 1st" "rinto toh na ci girma na bar miki"
"Kaide ka sani muje nidai kafin in barka nan" "ai nasan ƙaramin aikin ki ne"jerawa sukai a tare suka shiga cikin gidan, tun daga kofa ya fara kiran "goggo! Goggo" amma a hankali wanda ba lailai goggon taji bah.bayan sun shigo ne ta shinfiɗa masa tabarma zama yayi yana ya gaji ruwa ta kawo mishi pure water masu sauƙin sanyi ɗauka yayi ya sha sannan ya dubata "ina goggo nikam?" "Baka da baki?"
"Da suƙi kam akwai shi! Goggo! Goggo" daga cikin ɗaki goggo tace na'am wake biɗa ta tana fitowa daga ɗakin, a bakin ƙofa ta tsaya sagade tana kallan shi kafin chan tace "Mubarak idanun ka kenan da kyar fa na iya gane ka"ta ƙare maganar da son zolayansa cewa yayi "goggo kiyi shiru kar yarinyan nan ta raina ni" taɓe baki tayi tana shigewa ɗaki tace "idan kun gama ku kira ni"
AS kuwa yana ƙofan gida tun daga zuwan su har rigengen da sukai duk akan idon shi, dauke kai yayi haɗi da faɗin ko ina ruwan shi tada motar yayi ya bar anguwan zuwa gidan Ummi nan ɗin kam ya jima sosai sai da yayi Sallar isha'i ya kama hanya komawa gidan shi.
__________bayan idar da Sallar isha'i suna zaune bayan sun kammala cin abinci wannan karan hadda Ruqqy tazo da ita ake ta fira wanda har lokacin mbk bai wuce ba yana nan, kiran umman shi yayi through video call tambayan shi tayi ina ya tsaya har Yanzu bai dawo bah kuma ga yana yin gari da hadari cikin ɗan dariya yace Anty autan ki ce ta riƙe ni "wacce auta na kuma?"
"Ooh ashe ban shafa miki bah,albishirin ki?"
"Goro fara ƙal"
"Ok tom Anty rufe ido sai nace ki buÉ—e sannan"
"Nifa iyayi ne bani so tam" ta ƙare maganar da rufe ido,ya fito eely yayi dake ta jinsu tunda suka fara waya tana jin so da kewar matan na taso mata sanadin haɗuwar su da mbk Ammie ɗinta da Anty maman mbk suka ƙulla abota, tashi tayi tana ƙarasowa inda yake zaune ta kai daga gefen shi. Juyo da fuskar wayar yayi zuwa gare ta ita kuma ta sunkuyar da kai tana jin kwalla na mata kai koma a cikin idanun, ji tayi mbk nace wa "Anty ki buɗe idon slowly" kamar yadda yace kuwa a hankali ta rinƙa buɗe idon har ta gama buɗe su a kan eely da kanta ke duƙe,tabbas duk da ta dukar da kanta ƙasa hakan ba zai hana ta gane wace anan ba, dan soyayyar da take yiwa eelham ko yarinya ta ce ita sai haka, so take ta tabbatar shi yasa ta ambaci sunan ta "Elham baby" na'am Anty ta amsa muryan ta na rawa sosai alamun tana gab da fara kuka, a ruɗe mbk ya fara tambayanta da "Bestie lafiya kuwa mi yasa kike kuka wani abu aka Miki?" Cikin murmushi yaƙe ta ɗago ta dube shi tace "qlau fah" zuba mata ido yayi ba dan ya yarda ba dan yasan eely sosai, "daughter mi akayi Miki?" Cikin fake smile ta amsa mata da Lafiyan ta qlau kawai kewan ta tayi ne, ai gani daughter,yasu goggo da Aminiya fatan duk kuna lafiya kwana ki munata niman wayoyin ku Amma duk a kashe munje har chan Minna moƙatan ku suka ce kun tashi kun koma Kaduna, itama gidan Aminiya ma haka wai sun tashi ga wayoyin duk basa shiga, miƙawa Aminiya mu gaisa kwana da yawa" cikin dauriya tace muna lafiya qlau, ga goggo ta ƙare maganar muryan ta yana rawa sosai mika wa goggo wayar tayi ta shige ɗaki da hanzari dan bata son suga hawayen idanun ta,karɓa goggo tayi itama cikin rawan muryan da ya saka Ruqqy da mbk shiga wani hali, cikin dauriya dai ta daure suka gaisa bayan sun gama gaisawa tace "goggo Aminiya fa idan bata nan a bani numbern da zan same ta" anty a lokacin ba abinda take son ji sai muryan Ammie,dan duk cikin su tafi jin kewar ta.
"Hmmm zulaiha kenan ai aminiyar ki saidai muyi ta musu addu'a dan sun riga mu tafiya" bata samu daman ƙarasa zancen nata ba taji kuka na zuwar mata kaman yanzu ne abin ya faru, mbk kuwa salati ya sake kamar yadda Anty tayi yace "goggo kina nufin Ammien mu ta rasu?" Gaɗa mishi kai tayi dan bakin ta bazai iya furta komi anan bah, shina mbk bai san sanda hawaye Masu zafi suka rinƙa gangara a fuskar shi bah,ji sukai cikin kuka sosai aunty tace kuyi min kwatancen gidan gani nan zuwa da Alhaji. Ruqqy dai an barta a duhu dan ita sam bata san labarin su bah, ita ta dauɗi wayan ta gayawa Anty sunan anguwan da kuma kwatancen gidan, bayan ta yanke wayar ne ta shiga bawa su goggo baki Saida suka ɗan lafa da kukan nasu ne sannan ta shiga ɗaki wajen eely saidai ƙofan rufe yake da key, "eelham dan Allah ki buɗe" shiru taji wato ba alamar budewa nan ta hau yi mata magiya akan ta buɗe amma taƙi, sallamar su aunty da isowan su kenan ita da Alhaji sai ɗiyar su Jawaher ya katse mata bugun ƙofan da take yiwa eely.
tabarma ta shifiɗa musu tana gaishe su wanda bappa kawai ya amsa aunty sam hankalin ta bai jikin ta, gaisar da goggo bappa yayi yana ƙara yi mata ta'aziyya,gaɗa kai kawai take haka dai ya samu ya lalashe su dukan su, "banga daughter bah tana ina?" mbk da sai yanzu ya farga babu eely a wajen yayi saurin miƙewa yana tambayan Ruqqy ko ina take, ɗaki ta nuna mishi knocking yayi mata a ƙofa sau biyu a na ukun ne ta buɗe, ba tare da ya kalle ta ba yace "fito su Anty sunzo" ba musu kuwa ta fito tana ƙarasawa wajen su gaida bappa tayi sannan ta faɗa jikin Anty tana sauke ajiyar zuciya shafa bayan ta tahau yi tana lallashin ta, bayan waje ya natsa ne bappa ya tambayi goggo "taya suka dawo nan babu labari? Sannan ina baba?" Bata ce masa komi ba sai kallan Ruqqy tayi tace "jeki ki kirawo min Abban ku da umman ku kema ki dawo" amsa mata tayi da Toh tana daukan hijab ɗinta tayi waje cikin kankanin lokaci sai gata dasu,umma sun shigo bayan sun gama gaisuwa ne sai goggo tayi gyaran murya wanda hakan shi ya ƙara natsar da wajen duk da dama ba surutu suke ba, "saminu ka tambaye ni ya akayi muka dawo nan ko?" Ta ƙare maganar da sigan tambaya "na'am haka ne goggo" toh Masha Allah duk zakuji hadda ku ma" tayi maganar tana kallan su umma da Abba,share fuskanta tayi tas ya zama babu ɗigon hawaye ko ɗaya ganin haka eely ma ta goge hawayen nata tass tana tuna alwashin da tayi wa kanta na kuka ba nata bane bah.
Goggo duk kallan su tayi kafin ta kwashe komi ta gaya musu tun daga kan auren da sukai wa eely har zuwa sakin da mijin yayi mata cikin bainar jama'a, koran da Abba yayi musu da kuma yadda ya nuna su twince ba yaran shi bane da rasuwan su Ammie da tashin su daga gidan da suke har zuwa dawowan su nan. Baka jin komi sai na shesheƙan kukan su umma, Anty,jawaher, Ruqqy,da mbk dan ya kasa daurewa,bappa da Abba ne kawai basuyi kuka ba sai goggo da eely baki su bappa suka rinƙa bawa matan su da ƴaƴan nasu, "goggo kuyi hakuri bisa jin mu da kukayi shiru duk bamu san abinda yake faruwa ba kenan dan Allah goggo ina son kiyi mana alfarma mu wanke laifin mu kuzo mu koma chan gidana da zama dan Allah goggo karkice a'a dan Allah" da ɗan murmushi a fuskar ta tace "a'a saminu nan ɗin ma da muke zaune ya isa dan uwan ka Kabir gashi nan yana kokari damu, Ni dai bani da bakin gode muku sai dai nace Allah yayi muku albarka daku da zuri'an ku baki ɗaya" da Amin suka amsa dukan su suna jin kaunar ta a rai, "goggo amma za'a rinƙa aramana Elham Koh?" Cewar Anty ganin goggo dai ba binsu zatayi bah, "gaku ga tanan Ni nawa ido"da sauri kuwa Anty tace "ku shirya mu tafi" ɗaki Ruqqy da eelham suka shiga suka haɗa kaya shima ba mai yawa ba sannan suka fito tsakar gidan da kayan su cikin ɗan madaidaicin bag, cikin zuciyar eelham kuwa tinani take taya zata bar goggo ta kwana ita ɗaya a gidan nan, samun waje tayi tayi zaune haɗi da faɗin ta fasa zuwa tambayan ta dalili sukai inda take gaya musu bazata bar goggo ita ɗaya a gida bah, cikin dariya bappa yace "gidan Abban ku zata kwana kafin a samo mai kula da ita" jin haka ne sai ta shiga ta haɗawa goggo kaya ta fito dashi,duk waje suka nufa inda suka je sukai wa goggo rakiya har gidan mai anguwa, sannan suka dawo suka shiga mota eely dai na tare da mbk ta ɗan ware tunda gashi sai tsokalan juna suke
Horn bappa yayi inda da sauri gate man ya taso ya buɗe yana miƙa musu gaisuwa haka suka ƙarasa zuwa parking lot fitowa sukai gaba dayan su sukai cikin parlon, parlon ya ƙawatu sosai da kayan alatu na zamani ga kujeru nan wanda daka kalle su zaka gane ba ƙaramin Naira yayi kuka bah, "jawaher dauki kayansu ki kaisu ɗakin ku kuje ku kwanta ku huta dare yayi sai in Allah ya Kaimu kuma"ba musu duk suka miƙe suna sallamar iyayen nasu suka shige ɗakin jawaher.
eely kuwa Saida sukai sallama da Bestien nata sannan ta wuce É—aki tana dariya tsokalan da yayi mata,su Anty suma sun shige É—akin nasu ganin haka ne shima mbk ya fice zuwa nashi part É—in dake a wajen part É—in su Anty.
Bayan sunyi wanka sunzo kwanciya suka fara raba hali an rasa wanda zai kwanta a tsakiya,gajiya sukai sannan sanan jawaher ta kwanta a tsakiyan tana "gobe Ruqqy ke zaki kwanta jibi eely" "zamu gani toh" cewar Ruqqy, da yake duk a gajiye suke suna kwanciya kuwa sai bacci ya dauke su
Jirgin su Ummi ya sauka tun tuni inda aka zo aka dauke su zuwa family house ɗinsu dake nan abuja. Sosai ta samu tarbar daga wajen kanne da yayunta da kuma ya'yan ta, tunda suka sauka meenal ta shige cikin yan uwanta suna firan yaushe gamo. Hayaniyar da suka damu kakar tasu dashi ne yasa ta kora su suje suyi bacci dare tayi nisa, da yake suna jin baccin firan ne kawai ya dauke musu hankali aikuwa suna kwantawa sai bacci...............✍🏻