83&84
{🌹 EELHAM🌹}
Rabe'arh wakili
82 & 83
بسم الله الر رØÙ…Ù† الر ØÙ‰Ù…
Alhamdulillah AS sun sauka Nigeria a airport din Kano koda ya fito ya iske driver dinsa yana jiran sa dan ya kira shi ya faɗa masa time ɗin da zai sauka shi yasa, gidan su goggo yace a wuce dashi koda suka isa gida part din shi ya wuce direct dan dare ta riga da tayi duk da farkon dare ne kuwa, part din na nan fes dan ummi ta kan sa masu aiki su gyara masa duk da baison masu aiki na shigar masa part, wanka yaje yayi ya shiga kitchen ya haɗa liptea ya fito falon, Saida ya kammala sannan ya maida cup ɗin ma'adanar ta bayan ya dauraye, ɗakin shi ya koma ya na kwanciya kuwa bacci yayi awon gaba dashi daman ga gajiyan tafiya.... Gidan shiru baka jin motsin komi sai na kukan tsuntsaye, eelham ce jikin window tana kallon gate ɗin gidan daga dakin inna dan har tayi bacci farkawa tayi, tana tsaye a nan taga gate man ya buɗe karamin kofan gate yana matsawa wanda ya shigo, a lokaci daya kirjin eelham ya buga dumm dumm dimmm dimmm,dafe kirjin tayi tana karanto duk addu'ar da tazo bakin ta, jikin ta ya hau ɓari dan ganin abinda idanun ta sukai mata gani ji tayi kanta ya kulle zargin shi nan da nan ya mamaye mata zuciya da tsanar sa, haka ta kasance ga Aziza da take tsaye wajen window itama dan an sanar mata da abin harin su zai shigo cikin gidan yau,amma tunanin ta bai taɓa hasaso mata wanan fuskar bah,shikuwa wannan mutumin daidai wajen window dakin inna ya tsaya yana kara waya a Kunni sakamakon kiran da akayi masa daga ɓangaren can, ba'a jira cewar ba aka ce "karka shiga da akwai matsala ka dawo yanzun nan". Kit aka katse kiran bai ko ƙara ko second ɗaya a wajen ba ya kama hanya da niyan barin gidan a kusan tare Azizaa da eelham suka bi bayan sa, amma saidai Azizaa ta riga eelham fita shi yasa basu haɗu da juna ba haka suka rinƙa bin bayan sa sunayi suna laɓe cikin ikon Allah sam bai lura da ana binsa ba burin shi kawai ya koma can wajen yan kungiyar su ya ji mike faruwa dan wannan kiran na gaggawa da gani ba daidai ba, Saida sukai tafiyan wajen hour 1 and half sannan suka ga ya shiga wani lungu, yana shiga itama Aziza ta shiga wanda eelham ta ɗauka ko tare suke duk da dai bata hango ko fuskar waye ba, Saida ta tabbatar sun shige sannan itama ta shiga tanayi ta na laɓewa, abinda basu sani ba fadil da hashem da umar suna biye dasu a baya saidai suma ɗin basu san ko su waye a nan ɗin ba, wajen shiru sai kukayen tsuntsaye da kwaɗi da suke a ruwa dan wajen ya kasance kamar daji ne duba da manyan itacuwa dake a wajen da kuma grasses da sukai wa wajen kawanya, can nisa da kofan shigowa haske ne na fitilar aci balbal ake hangowa, can wannan mutumin ya nufa suma ɗin haka suka rinƙa take masa baya cikin taimakon Ubangiji da rufun asirin sa, ai ƙame wa sukai bayan sun iso wajen Inda suka iske wata mata daure ta igiyoyi masu kauri ga jikin ta nan duk jini alamun dai ba karamin azaba aka gana mata ba, Saida wannan mutumin ya tsaya a post dinsa sannan cikin girmamawa yace "shugaba gani, naga kiran gaggawa ayayin da komi yake gab da kammaluwa" cikin ɗacin rai da kunan zuciya yace"wannan matar ita da yaron aikin ka sukayi kiran wata akan tafiyar ka cimma aikin mu, ganin da yayi ba haske yasa yayi kiran ka" wata tsana mafi tsanani yaji yana dirar sa akan wannan mata ba tare da tunanin komi ba ya ƙarasa gareta ya ca kuma wuyan ta ya shaƙe shaƙa bana wasa ba da kyar sauran members suka kwace ta wajen wannan mutumin faɗi yake "kin san shekara nawa nayi ina farautan wannan yarinya ko kinsan abubuwan da na tsallake dan sabida wannan yarin yan? Ko kin san buri na akan haka?" Ai komawa yayi ya rinƙa kai mata duka kamar an aiko shi da yake zuciya na kusa yake mata wannan dukan yasa dakyar aka banbare shi daga gareta ita kuwa sai maida numfashi na wahala take Wanda a yanzu da kyar yake fita,,, a harzuƙe ya nuna ta da yatsa manuniya yace " kenan a kwanakin da muka harar wa cikin su uku kece kika ɓata mana aiki? Ke ce ko ba ke bace?" Ya kare maganar a tsawace yana kokarin rikiɗa ya koma wani babba kwaro, eelham da take video recording nan da nan komi ya fara dawo mata na mafarkin da take yawan yi da wannan halittar, jikin ta rawa ya kama yi numfashin ta har yana yi kamar zai ɗauke hannu tasa ta danne bakin ta jin tana kokarin tona wa kanta asiri addu'oi ta fara jerowa cikin ikon Allah ta samu natsuwa, haka ta ke ga ɓangare Azizaa kadan ya rage ta fasa ihu sai dai taji anyi sauri an rufe mata baki, hadi da faɗin "ki nutsu" cikin yin ƙasa da murya, ba shiri da juyo da sauri ta kalle ta ba kowa bane face eelham, sauke ajiyar zuciya tayi da mamakin ganin ta anan amma bata ce komi ba duk suka maida hankali wajen abinda yake faruwa, cikin sauyin halittar nan ya isa gare ta yana buɗe katon bakin shi kamar kada, ganin haka da tayi ne yasa ta kama addu'a a sarari kowa naji, shi kuwa wannan mutumin da ya rikada duk da yana jin karfin addu'an a jikin shi haka bai sa ya daina nufo ta ba, cikin members dinsu kuwa babu wanda yayi gigin riƙo shi a wannan karan dan duk wanda yaje wajen yasan sauran Saida maman mutum ta haifi wani ba shi ba, ganin zata nakasa sa yasa ya hura wuta ya wurga mata, da yake Allah ba azzalumin bawan sa bane ba Allah ya taimake ta aka ɗauke ta daga wajen nan da nan kuwa wajen ya kama da wuta balbalbal, daga saman jet aka wurgo da Roop mai karfi shi wannan ya kama ya hau da wannan matar a kafaɗan shi har suka shiga cikin jet ɗin, shima wannan halittar tashi ya rinƙa yi sama yana kaɗa fifigen shi kadan ya rage ya cimmusu sai ya kasa ya fado ƙasa sabida karfin addu'a da wannan mata ta rinƙa yi, cikin wani tsananin a zaba ya juyo, sauran members kuwa nan kowa yayi ta kansa dan sun san idan ya riƙe mutum a halin nan da yake tsaff zai farkawa mutum ciki, aziza taga abinda yafi karfin ƙwaƙwalwar ta kuwa nan ta ƙamƙame eelham tana da ta sani bin shawaran da akace ta biyo shi, shikuwa wannan halittar jin da yayi zuciyar shi na kaishi ga wajen su eelham ne yasa ya tafi i zuwa wajen, Azizaa da eelham kuwa ƙafa mi naci ban baka ba ganin yana kusanto gun da suke, nan suka kwasa a sittin, gwaff Azizaa tayi karo da mutum wata razananniyar kara ta saki tana sumewa, cak hydar ya ɗauke ta aka wurgo da Roop ya dare zuwa cikin jet dan ganin wannan halittar ta kusanto su, eelham ma dai haka ta rinƙa gudu har ta fita daga cikin wannan wajen gudu take har ta iso titi wani ta hango rakube wajen wani icce da alamun shi ma dai taimako yake biɗa yana ganin ta kuwa shima ya hau binta a baya suka rinƙa gudu Saida sukayi nisa da wajen sosai sannan suka samu waje suka fake suna maida numfashi,.... Cikin dajin kuwa masu jet ɗin nan kuwa sai ɗauki ɗaɗ-ɗai suka rinƙa yi wa mugayen nan har Allah ya basu ikon kwasan su duka harda ogan su, wanda kwata kwata dibara ta kwace masa, haka dai yana ji yana gani ya mika wuya aka tafi dashi Saidai sun kasa da wannan mutumin haka dai aka barshi da saka ran shima zuwa gobe insha Allah zai shiga hannu haka dai suka bar cikin dajin nan cikin nasara batare da ko kwarzanen ciwo a jikin su ba,,,... Su eely suna zaune a nan sai ga mota tana danna musu horn har sun mike zasu kwasa a guje taji ance "daughter" a zabure ta maida duban ta zuwa ga Anne da take hakimce a back sit dan daga cikin motar sun kunna haske ta yadda na waje zai gan na ciki, buɗe ƙofan Anne tayi ta fito da murmushi dauke a fuska tana zuwa tayi hugging din eelham haɗi da shafa kanta, breaking hug din tayi ganin fa ba lokacin haka bane janta tayi zuwa cikin mota a back sit shikuma wannan namijin ya shiga front sit duk da dai Anne bata san shi ba za ta taimaka mishi ne kawai, direct gidan ta dake anan Abuja aka wuce da su duk da babu haske sosai a garin haka bai hana su gano kyawun gida na Anne ba,wani giet ne yazo ya buɗe musu gate suka shiga ciki,bayan yayi parking suka fito suna nufin cikin gida, a falo suka yada zango eelham kuwa kwanciya tayi tana jin jikin ta da cikin ta na dan yi mata ciwo, Anne da kanta ta shiga kitchen ta kawo musu ruwa masu saukin sanyi nan kuwa suka kwankwaɗe duka lafewa tayi a jikin Anne tana sauke ajiyar zuciya shima wannan guy ɗin da basu san shi ba kwanciya yayi kan cushion yana maida tashi ajiyar zuciya dan yau sun ga abinda basu taɓa gani ba haka kuma sun tirƙa gudu, ganin da Anne tayi ne kaman suna son suyi bacci yasa ta katse su tace su bari idan sukai subhi sai su kwanta gaba ɗaya dan lokaci ya kusa sauran yan mintina..