92&93
{🌹 EELHAM🌹}
Rabe'arh wakili
92 & 93
بسم الله الر رØÙ…Ù† الر ØÙ‰Ù…
Knocking kofa meenal tayi mata daga ciki eelham ta ce "waye?" "Wai kizo ga baƙuwa tana son ganin ki" tana gama faɗi bata jira cewar ta ba ta wuce, ita kuwa eely tinani ta shiga yi wata baƙuwa kuma da wannan daren, daurewa tayi ta mike tana ƙara bin su Anwar da addu'a saboda tsaro, a hankali ta karasa gefen Anne ta zauna cikin murya ƙasa ƙasa tace "Anne wa yake ne ma na?" Pointing zeenat tayi tace "gata nan" ita kam bata gane ko wace ba har zata yi magana kuma sai tayi shiru, zeena kuwa taso wa tayi har gaban eelham ta tsugunna ta kuma haɗe hannayen ta waje ɗaya alamar roƙo tace "dan Allah dan Annabi Muhammadu saw eelham kiyi haƙuri ki yafe min abinda nayi miki ba dan hali na ba dan Allah da Manzon sa" "mi kika yi mata da kike neman yafiyar ta?" Cewar Abbu, cikin na dama da kunya ta zaiyane musu cewa "ita ce ta zuba wa eelham magani a cikin cornflakes na zubda ciki ashe bata dashi sai dai yayi daidai da zuwan period ɗinta shine yasa haka yayi mata rushing shi kuma doctor din ya kasance doctor din mu ne to da yayi min wannan bayanin sai na saka ya juya abin ya koma yadda ya gaya muku, dan Allah ku yafe min
na tuba bazan kuma ƙara aikata makamancin haka ba, ba ma gare ta kawai ba dan Allah" ta ƙare maganar hawaye na zubar mata dan da gaske wannan karan tuban gaske tayi ba ta muzuru ba, ganin gaskiyar da sukai da ga kwayar idanun ta ne yasa basu tambayi dalilin ta nayin haka ba suka amsa mata da sun yafe mata bappi kuma da kanshi ya buƙaci da eelham ta yafe mata tunda ta gane kuren ta, ita ma ɗin ba'a ja da nisa ba tace ta yafe, Anne kuwa ɗaga waya tayi ta kira aunty Maleeka tace su taho da mazajen su da kuma sauran kannen ta, ba'a dauƙi wani lokaci mai tsawo ba sai ga sallama su aunty Maleeka sai aunty safna bayan ta kuma anty zahra daga bayan ta kuma mijinta ne dan su fadeel da hashem daman tunda suka miƙa Abba suka dawo babu jimawa, an dan yi gaishe gaishe inda eelham taƙi ta dago da kai dan ji take idanun wanda yake kallon ta sunyi mata kaifi da yawa haka yasa taki ta ɗago duk da taji muryan yan uwan ta wanda ta daɗe tana mararin ƙara son gani su, bayan waje ya natsa Anne ta dauko wata kyakkyawar box ta aza shi bisa table ɗin gaban su goggo tana kaiwa durƙushe a ƙasa Muryar ta na rawa saboda tuno ranar da baba ya bata amanar su, tace "goggo wannan gaba ki ɗaya dukiyar baban su ne wanda kafin Allah yayi masa rasuwa ya fito dasu yace in riƙe su amana munyi maganar da kwana biyu sai Allah yayi musu rasuwa" tana kaiwa nan ta saka hannu ta ciro wani takardun gida wanda aka ware su daban cikin wata file buɗewa tayi ta ciro su sannan ta miƙawa goggo tace "wannan yace idan Allah ya ƙaddara haɗuwar shi da abokin shi to wannan mallakin shi ne idan kuma ba ya nan yace na tayasa isar da haka" tana kaiwa nan ta aje tana share hawaye wanda eely ma kukan take cikin karamin sauti su anty Maleeka ma sai kwalla suke ta sharewa, wani kuma paper ta kara fidda wa tace "wannan kuma yace na Hajiya maman shi ne" sai anan Abbie da grandma suka gane inda zancen ta ya dosa jin abinda tace dan haka baba yake kiran grandma, muryar grandma na rawa tace "Hajiya Khadijah kardai ince wannan ɗin ce matar ɗa na" gaɗa kai kawai goggo ta iya yi mata dan sun fama mata wannan mikin da take ta dannewa, wani kuma ta ƙara fiddawa tace "wannan kuma yace mallakin Hajiya maman shi ne da na goggo kawai amma ya roki alfarman gidan ya zama family house ya zama ana gida ɗaya kuma gari ɗaya" wata kuma file ɗin ta ciro sai da ta share hawaye wannan karan sannan ta buɗi baki da kyar yace "wannan kuma yace ta Yar uwar shi Ammie ne, yace baida tamkar ya ita bayan iyayen sa" numfawa tayi kafin ta ci-gaba da faɗin yace "idan kin tashi miƙa musu Idan bani kice karsuyi kuka barin ma Ammie kice addu'ar ta kawai nake buƙata inasan kanwata sosai ina kuma alfahari da ita" they can't help it all but to cry, Anne, goggo, grandma, inna, eelham,su anty Maleeka da dama tuni suke kuka nan suka ƙara buɗe wata sabuwar babin kuka, Abbu, Abbie da Abba su suka basu baki har dai sukai shiru, na karshe ta ciro daga cikin file ɗin tace "wanga kuma yace a bawa Alhaji Muhammad dan ya kasance mutumin kirki ne" sauran takardun da suke ciki suna da yawa ba laifi inda aka duba aka ga gado ne da yake duk suna da ilimin akan rabon yasa suka raba aka ba goggo ta ta rabon amma taƙi ta amsa tace ta bar ma yaran sa, Anne ma ance ta karɓi tumulin takaba amma taƙi, haka dai aka rabawa yaran shi su uku inda ko waccen su ta fidda dukiya mai yawa, eelham kuma aka bata File ɗin da baba ya ba ma Ammie, amma tace a barshi wajen goggo,sai a nan su aunty Maleeka suka ga eelham nan fa suka tarbi junan su cikin kewa da so da kauna, bayan an dan wartsake ne duk da kowa yana da damuwar shi a zuciya ya dai boye ne kawai, Anne ce tace "Mallam fadeel da Mallam Hashim agaishe ku da kokari aikin ku yana kyau fah ko ma ince yayi kyau" wata kunya ce sukaji ta rufe su suka kasa cewa komi sai dariyar da suka sunkuyar da kai suke, grandma tace "ya zaki sakawa yan jikokina zafi dan Allah" cikin ɗan murmushi tace "Hajiya mama a dai bar kaza cikin gashinta" "a'a a dai faɗa muji" ai babu shiri suka dawo suna duban Anne suna yi mata sing alamun tayi hakuri, karab kuwa sai kan idon goggo, "ai Hajiya Khadijah ki hita batun waɗan nan mutanen ba'a shiga tsakanin su" "goggo a dai bar komi yadda yake" cewar aunty Maleeka Anne kuma ta karɓe da cewa "daman ai bakin ku ɗaya ya zama na banda daman inyi waya sai an kwafa an kai wa Radio masu jini..." Da sauri aunty safna ta taso ta rufe mata baki tana dariya tace "Anne we are Sorry kinji?" Su ma mazajen nasu haɗa hannu sukai suna bata haƙuri cikin marairaice fuska, mutanen falon kuwa duk da suna cikin damuwa amma wanna comedy tsakanin in-laws ya mantar da su nan kuwa suka hau yi musu dariya, kamar yadda suka saba goggo tace "ai fa sai mun ji abinda kuka kulla yau ehem! muna jira" "a dai nima sauƙi ban da zuuuu" sai kuma gaba ɗaya da yaya fadeel,yaya hashem, yaya muktar, aunty Maleeka,anty safna, aunty zahra, da kuma eelham wacce tayi maganar suka haɗa baki wajen faɗin "giiiiiiiiiiiiii" suka jashi da tsayi, ita kuwa pillow ta dauko ta wurga musu nan kowa ya yi ta kansa mutanen falon kuwa sai dariya suke ta faman yi musu dan sun burge kowa,Anne ma miƙewa tayi saɗap saɗap Saida ta kai kofa sannan ta dan leƙo tace "Hajiya goggo muma munyi nan sai da safe" "daman ai nasan bakin ku ɗaya duk zaku shiga hannu na ne" tuni Anne tayi gaba inda ta same su a waje sun shinfida carpet sai firan yaushe gamo suke, ganin Anne ta fito ne yasa suka bata wajen zaman dan ita Anne bata ɗaukan surikan ta a surikai a ƴaƴa take daukan su, ayi raha ayi dariya shi yasa wancan karan da suka kasa gane inda ta dosa ne yasa hankalin su tashi sosai sanadin fara binciken su kenan a kanta, a ciki kuwa wasun su sai dariya suke har yanzu dan gaskiya sun burge su kwarai da gaske, AS kam ya gaji dan haka ya shiga ɗakin da EElham ta fito inda ya samu su Anwar sai bacci suke shima gefen su ya kwanta bayan ya ɗauro alwallan bacci sai da yayi da gaske sannan bacci ya ɗibe shi, dan fuskar eelham yake ta masa gizo, suma ganin dare yaja ne yasa su grandma suka ce aje a kwanta hakanan nan kuwa kowa ya watse, a waje Ummi ta iske da irar firan da suka dasa, sakon su inna ta isar musu sannan Anne da umma da Ummi sai eelham suka wuce part ɗin Ummi da idan tazo anan take sauka, mazajen su aunty Maleeka kuma suka bi su yaya khaleel zuwa sashen su na samari aunty Maleeka ma dakin iyayen su suka kwana tunda ko wani part yana da space sosai haka dai kowa yayi Bacci,,, washegari kuwa iyayen suka fito suka haɗa break mai lafiya inda aka tafi can ɗakin taro aka jera break ɗin anan bayan an gyara shi, aunty inteesar da Anty zuwaira su suka yi sarving din iyayen su amma sauran kowa yayi sarving mijin shi haka kuwa akayi,Elham plate daya ta dauka spoon uku ta saka dai dai cikin su sannan ta aje a gefen su, ta kuma haɗa musu Golden morn a bowl ɗaya spoon uku wato ita da Anwar da Anam, nan suka fara Bama cikin su hakkin shi, sauran kuwa sai hidima suke da mazajen su, su grandma da su Ummi sunji daɗi abinda eelham tayi amma sai sukayi kamar basu gani, anty Hanan da kanta tayi sarving ɗinsa ta miƙa masa gabansa amma tana aje wa ya tashi ya bar ɗakin gaba ɗaya yana jin ɓacin rai...