INUWAR DUTSE.......

Episode 1

by @rabearhwakili

*_๐Ÿ—ป๐™„๐™‰๐™๐™’๐˜ผ๐™ ๐˜ฟ๐™๐™๐™Ž๐™€...๐Ÿ—ป_*




 *_Rabi'a wakili_*



*_ุจูุณู’ู…ู ุงู„ู„ู‘ูŽู‡ู ุงู„ุฑู‘ูŽุญู’ู…ูŽูฐู†ู ุงู„ุฑู‘ูŽุญููŠู…_*



   *_Book 1_*

*_Episode 1_*



_______________________



     Kowane ษ—an adam yana ratsa sararin duniya ne ษ—auke da wani tsari na daban wanda Allah Ya tsara mana a rayuwa. Wannan tafiyar ba ta da wata fuska ta zahiri, kuma ba ta da siffa ko launi da za a iya kallo da idanu muddin mutum yana raye, sai dai nauyinta da zafinta suna sauka ne kai tsaye a kan zukatan da ke ษ—auke da ita. Akwai lokutan da walwala da daษ—i ke bayyana a fili tamkar farin wata, akwai kuma lokutan ฦ™alubale masu ษ—aci da ke girgiza jiki da firgita tunani, har ya kai ga mutum ya ringa gani a ransa tamkar dukan kofofin mafita da hanyoyin samun sauฦ™i sun riga sun datse, an bar shi shi kaษ—ai tsakanin tsananin fargaba da fita tsammani. To sai dai, a daidai lokacin da hasken rayuwa ya dusashe, sa'ad da dukan kewayen mutum ya turnu da baฦ™ar inuwa ta tsananin rudani, makami mafi ฦ™arfi da ke share fagen samun mafita shi ne natsuwa ta dindindin gami da jajircewa ta gaskiya. Kowa ya sani, Zaman jiran dadi, sai mai babban bargo.Haka kuma, duniyar nan ta zama tamkar igiyar ruwa, tana juyawa da kowa yadda ta ga dama, ba ta taษ“a tsayawa a guri guda ba. Saboda haka, ikon tsayawa tsayin daka a lokacin da wannan igiyar ruwan ke kwasar mutum zuwa ga gaษ“ar da bai sani ba, wani babban matsayi ne da kwarjini na daban wanda ba kowa ke iya kaiwa gare shi ba. Mutumin da ya siffatu da wannan juriya, ya riga ya buwayi dukan wata barazana da kowace irin maฦ™arkashiya da ke tunkaro shi daga kowane sashe na rayuwa. Jajircewa kuwa ita ce danyen ฦ™arfin da ke tursasa wa mutum ci gaba da takawa, tana tilasta wa ฦ™afafunsa ci gaba da takawa a ฦ™asa ko da gangar jikinsa ta gaza ษ—aukar nauyin kanta saboda tsananin gajiya da wahala. A cikin tsarin tafiyar duniya, fuskantar matsaloli ko kaษ—aitawa a cikin damuwa ba ฦ™asฦ™anci ba ne, kuma ba yana nufin an ฦ™are ba ne; wata koyoce ta musamman, wani darasi ne mai tsada da ke gina mutum, yake ฦ™ara masa kaifin basira domin ya shirya shi da dukan dambarar da zai fuskanta a gobe. Wannan rayuwar ba ta taba tafiya daidai da burinmu ko yadda muke tsara ta a cikin zukatanmu ba. Idan igiyar ruwan ฦ™addara ta taso da ฦ™arfi, tana juyawa ne kawai a kan sahihin tsarin da Mahalicci Ya riga Ya ฦ™addamar tun kafin halittar komai, domin a ฦ™arshe kowa ya gane cewa matsalolin da ke zuwa ba su da manufar ruguza mu ko share mu daga doron ฦ™asa, illa gyara mu da za su yi, su fito da ainihin juriya da ฦ™arfin da ke ษ“oye a cikinmu. Duk wanda ya fahimci wannan ma'ana ta sirri, ba ya fargabar tsayawar al'amura, kuma ba ya tsoron shiga cikin sabon rikici ko wata turkaturka ta rayuwa, domin ya san cewa tafiyar duniya ba ta taba kayar da wanda ya iya dakatawa ya bar wa Allah ikonsa ba. Haka kuma, mutumin da ya karษ“i dukan abin da ya zo masa da zuciya ษ—aya gami da gamsuwa ta ciki, ya sanya juriya a matsayin garkuwarsa ta yaฦ™i, sannan ya dogara ga ALLAH, lallai ne zai riski nasarar da aka riga aka rubuta masa, zai kuma taka da ฦ™afafunsa a kan daukakar da aka yi masa alkawari ko da dukan hanyoyin da za su kai shi gurin a halin yanzu sun Lulluษ“e da baฦ™ar inuwa ta duhu mai ban tsoro. Domin a ฦ™arshe, rayuwa gaba ษ—ayanta, arziฦ™i, matsaloli, da daukaka, duka suna naษ—e ne a cikin babban shirin nan na ฦ™addara, wata doguwar hanya ce da kowa ke bi yana takawa daki-daki cikin duhun dare, ba tare da ya san wace irin dambarawa ko jarrabawa ce ke jifansa a gaba ba, sai dai kawai amincewa da juriya da kuma dogara ga ALLAH, shi ne hasken da ke haska masa kowane taku.

 

________________

     Kano state Nigeria.

       Yammace saฦ™aliyan ana gab da magrib, wani mutum na hango, bai cika kiษ“a ba, Sauri yake ta zubawa kamar wanda zai tashi sama, babbar rigar da ke jikin shi wacce ta sha ruwa sai tashi da sauka yake, kamar wanda zaiyi tsuntsuwa ya fire sama, tafiya yake  baya ko kallo inda yake saka ฦ™afa, kamar yadda baisan inda yake takawa ba, haka zuciyar shi ta kasance tana chan wani wajen daban. Burin shi kawai ya koma gida, ko ya samu sarari na daga abinda ya taru yai masa yawa. 

     Tun da ya doso farkon layin anguwar ake binsa da kallo, kallon da ke mishi inkiya da gagarumin matsala, eh kam dole ya ambaci haka da matsala mana, dan babu rana na ALLAH da zata zo ta wuce  bai samun irin waษ—an nan idanun a kansa ba, wanda ba yau farau ba, yana kuma da babban tabbacin ba ฦ™arshe bah kenan, matuฦ™ar yan kokawan gidan sa suna nan, ai shikenan.

     A maimakon yanayin sa ya chanza, amma ina babu alamun haka tattare da shi, inda sabo ya saba, dai dai da kwayar zarra hakan bai taษ“a ci masa tuwo a kwarya ba, idan sun kashe kansu maฦ™abarta har yau har gobe kai har wani shekara bata cika ba, toh akan mi zai na dinga wahalar da rayuwar sa a kansu, su bar sa da abinda yake damun sa mana. 

     "Mmmtwwwsss" ya ja doguwar tsuka dai dai ฦ™ofar wani ษ—an matsakaicin gida da hayaniya ke tashi daga ciki babu  ฦ™yaukyautawa, wanda sautinsa yake tashi  ana ji har ฦ™ofar gida da maฦ™ota. 

     Shiga ciki yayi, Inda ya  tarar da su a hargitse, sai faman yaษ“awa junansu   magana da son maida martani a zafafe cikin fusata dan a kular da abokin faษ—an. Hakan ba sabon abu ba ne cikin rayuwar gidan ba, domin ga wanda bai san su ba sai ya yi tunanin sun haษ—a tsatson ฦดan dambe ko kuma maguzawa, ta yanda ba sa raina ruwan shuka, kamar jira suke yi a ce kule suce as. 

       ฦŠauke kai ya yi tare da jan doguwar tsaki da nufin barin wajen. Babu shiri babu tsammani ya ji sauฦ™an bokiti a bisa goshinsa, take ya cije leษ“en sa tare da dafe goshinsa da tafukan hannayensa saboda  azabar zafin da ya ziyarci har cikin ฦ™oฦ™on kansa, nan take malolo makure sa a wuya.

        Shiru ya mamaye wajen tamkar an yi ruwa an ษ—auke, duk wannan hayaniyar ta gushe tamkar yadda ruwa da sabulu suke gusar da ษ—auda. Ba komai ya haddasa hakan bah illa ganin kwaษ“ar da suka kwaษ“a, watsar da makaman yaฦ™in da suka yi niyyar tadawa suka yi yayin da kowa ya sha jinin jikinsa.

 Da sauri ya ciro hannun sa akan goshin dan tabbatar wa shin da gaske ษ—in sun raunata sa? Cikin sa'a ba ciwo ba kuma jini, a ษ“oye ya sauke ajiyar zuciya da hamdala ganin ba su zudda masa da jini a banza da wofi ba, dan ba yi da hanyar kuษ—in magani balle a ษ“allo masa wata jinyar.

        ฦ˜ara ษ—aure fuskarsa ya yi waje guda tamkar magribar ษ—inya, ya na cin  magani haษ—i da bin su da kallon ษ—aya bayan ษ—aya, Ji ya yi wani sabuwan baฦ™in ciki ya ฦ™ara shigewa kai tsaye har cikin ฦ™asan zuciyarsa, dan takaicin ganin yadda suka nuna  rashin damuwa sai ma kallon da suke bin sa dashi kamar da shi za su ci gaba da dambarwan, nan take malolon sake linkuwa fiye da wanda yake ciki, a yanzu hakan kuwa ya taimaka wajen ฦ™ara tunzira shi, ga takaicin su da takaicin ya dawo bai samu abin da ya fita nema ba, abin sai ya haษ—u ya haษ—e masa goma da ashirin. Hakan ya ฦ™ara taimakawa wajen tafasar da zuciyar dake kwance cikin ฦ™irjinsa.

    A fusace ya soma cewa  "Uban wa ya halbo ni? Wallahi idan kuma ba haka Allah sai na lahira yafi ku jin daษ—i, a waje mutum bai huta ba, a ce cikin gidansa ma ba zai huta ba? Duk kun ฦ™arar da ni dan masifarku kamar wanda Maye ya yi wa ajiya. Na ce uban waye ya halbo Ni?" Ya ฦ™are maganar yana mazurai cikin maษ—aukakin ษ“acin ran da ya bayyana har a cikin kalmominsa.

        Duk tsam sukayi suna binsa da kallo, kamar sunga wani sabuwar halitta, ko wani majigi. ko ma ace kamar waษ—an da basu gane yaren da yake yi ba ma bare su fahimci inda ya dosa. 

    manyan mata ne su uku da yan mata uku, chan ฦ™arshen gidan wata matashiya ce zaune a ฦ™ofan madafa sai dai ta juya musu baya, duk wannan masifar da suke ko ษ—agowa ta kalli halin da suke ciki batayi ba, bare ta ce wani abu, idan ba ka lura ba, ba za kace akwai mutum a wajen ba, dan gaba ษ—aya yanayin matashiyar ya nuna bata ma san halin da suke ciki ba. "Ooh ga ษ—an iska na magana ai dole ku maida ni tataccen haihuwar ฦ™asar gada! Dan....."

    Cikin sauri mama ta tare shi jin zai fara  sakin ashariya tace "haba mana mallam kasan dai mutum ษ—aya zaiyi wannan aiki ba wai duk mutanen da suke a wajen nan ba koh? bare kuma kazo kana wa mutane kwakwazo, da son tarawa mutane jama'a cikin gida?, Kai ma kasan ba aikin kowa bane sai ta yar gaban goshin ka, dan haka ka juye a kanta ba wai waษ—an da basu san hawa da sauka ba".

    Wata muguwar kallo ya wurga mata wanda yake cike da takaici da ษ“acin rai mai tsanani, ba mama da yake watsa wa kallon ba har su Umma duk sun sha jinin jikin su suka tsime waje ษ—aya, sanin kansu ne kwaruru ba sa'an wake bane, banda ALLAH yasa gwiwa ta faษ—i ฦ™as wanwar da wane mutum naji mutuwa, Inda a lokacin da yake amsa sunan sa ne, da wata magana ake ba wannan ba, a fagen rashin mutunci baya ya basa ba gaba bah, duk wani nau'ikan rashin mutunci da suke fama dashi a ฦ™arฦ™ashin ฦ™afar sa suke, dan kuwa kam sai sun jira sa. 

    "Nace uban waye ta hal ban? Wan nan itace ta ฦ™arshe ba zan kuma magana ba, amma zan yanke hukunci ga wanda yayi bai faษ—a ba, dan nasan ko wace, walau yayi ma mutum daษ—i ko akasin haka". Ya faษ—a a tsawace har jijiyoyin wuyansa suna tashi. 

    Binsu da kallo ya shiga yi kafin ya gyada kai yana ฦ™ara tabbatar da cewa eh kam lailai ya cika ษ—an iska haihuwar ฦ™asar gada, yo to inba ษ—an iska ba waye zai ta ษ“aษ“atu a rasa mai tanka mai? Nan da nan ransa ya ฦ™ara ษ“aci, fiye da wanda ya shigo dashi gidan, Fiye da wanda suka ฦ™ara masa.  

      "wa.." da sauri umma ta katse shi dan tasan shi tasan halin shi sai dai ma su ba wasu labari, dan ba mutunci ne dashi ba, yanzu yana iya mata duk abinda ya ga dama gaban kishiyoyi, "kayi haฦ™uri mallam nice! hakan ta faru cikin rashin...

    "Isassa, shafaffa da mai, hamshaฦ™iya, wallahi ALLAH ni nasani, tunani na bai  tafi a banza ba dan nasan kaf gidan nan kece zaki aikata min haka, san nan tsabaragen rainin da kikayi min ina tambaya sai kallo na kike da fiฦ™iฦ™in idanun ki  Kamar kinga mahaukaci sabon kamu" 

     Nifa ba da gangan na jefe ka ba, bare ka taso ni gaba da maganganu kamar wacce ta burma maka wuฦ™a a ciki, alhalin ษ—an bokiti ne fah ya same ka a ka, naga kuma bai kumbura ko zub da jini bah! Ka daiyi haฦ™uri Mallam ba kai nayi niyyan halba ba sai matar ka zuhura, amma Wallahi ko yanzu ษ—in ma ba sha tayi ba, ALLAH sai nayi abinda nayi niyya".

      Nan fa ta shammaci kowa ta wurga wa Inna lariya, cikin Sa'a kuwa ya sauka kan goshin ta, dake lariyar ฦ™arfe ce Kuma ta ษ—an ษ“alle hakan ya bada daman kartan mama a goshi kaษ—an.

    "Kan bala'in nan......har ni zaki zubda wa jini? Lailai Rashida kin ษ—ebo abinda yafi ฦ™arfin ki, ya kuma fi ฦ™arfin dangin ki". Tana kaiwa nan tahau dube duben abinda zata maida raddi itama. 

     "Ke awaaa....? Tsaf  umma ta haษ—iye Maganar da tayi niyyar furtawa, sakamakon ganin mama ta dunfaro ta wuฦ™a kai tsaye. 

       tabbass ta tsure jinin jikin ta duk sun dawo kan kumba, sai dai gefe na zuciyar ta tana gaya mata kar ta gudu, idan ta gudu ai sai mama taga lagwan ta. 

      ฦ˜ara gyara tsaiwa tayi tana jiran tazo ษ—in taga iya gudun ruwan ta. Saidai kafin mama ta ฦ™araso gare ta Samha da Hanifah sun riฦ™e ta kam wanda hakan yaja mata dakatawar dole. 

    "Ku sake Ni, wallahi ni ko ita cikin gidan nan, har ni zata zubda wa jini?" 

    "Ke Hanifah ku sake ta! Ke kuma idan kin fasa chaka mata wukar baki haihu ba, na bar muku fili, ku cigaba amma a bakin auren ku, ni Muhammad na gama magana". 

     Shiru ya mamaye ilahirin gidan kaman anyi ruwa an ษ—auke, wanda har Abba ya bar wajen basu samun zarafin cewa uffan bah. 

    Shi kuwa yana gama faษ—in haka ya bar su nan tsaye ba tare da ya dube ko wanne su ba.

     ษ—aukar buta yayi ya nufi hanyar makewayi. Anan ya lura da ita, daman duk ษ—insu bai jituwa da ita dan bata bashi abinda yake so, wato kuษ—i!, shikuma mutum ne da idan kana bashi to fah zakuyi mutumci rana ษ—aya ka tsallake bakai haka ba, shikenan ka shiga sahun waษ—an da basu da amfani, shi yasa yaran duk basa basa wani girma, duk kuwa da cewa shi ya haife su. bayan su suna da yayu guda uku da suke a gidan ma'auri "sannu da zuwa Abba! Ina yini?" Ta miฦ™a masa gaisuwa cikin girmamawa,. ko kallo bata ishe shi ba, Ya shige banษ—aki, sai da ya fito san nan ya dube ta yace "gwara ki chanza mugun halin nan naki ki waye ki zama kamar sauran ฦดan uwanki,ba wai ki zauna kina jiran sai an miki ba! bani zaki taimaka ba sai kanki, shawara nike baki dan ki amfani kanki da ษ—an ki" yana ฦ™are faษ—in haka ya bar wajen. 

     Har Abba yayi alwalla yazo zai fita a gidan Basu samu zarafin cewa komai ba, dan maganar da yayi ya zame masu kamar gubar da ke ฦ™ona jinin jikin ya hana Mutum moruwa haka suka kasance a tsai a nan kaman wasu mutum mutumi. 

    "masifar da kuke nima ya tsaya kanku! idan ku ka jiwa juna ciwo biyar na baza tayi kuka ba, idan kun so ku kashe kanku". Cewar Abba da ke shirin fita daga gidan. 

     Ganin fitar sa yasa duk suka watsar da makaman yaฦ™in su Kamar basu ne suka so tada wata babbar husuma a cikin gidan ba.

      Sai dai ba'a hana ษ—an sabo da abu, nan fa suka koma kan wannan matashiyar dake a ฦ™arshen gidan dan duk maganar da Abba ya yaษ“a mata a kunnin su, nan fa suka shiga sukar ta da aibanta mata yaro, Kamar sun manta da ฦ™addara tana kan kowa.

      bata ษ—ago ba bare ta nuna tasan sunayi, sai cigaba da kaษ—a miya da tayi. Wannan halin nata na nuna rashin damuwa na ษ“aฦ™anta musu zuciya, shi yasa basu cika bi ta kanta ba sai ta yaron ta wanda gaba ษ—aya bata ragi, tanan ne kuma mutum zai gane tana da baki da tsiwa. Sai dai duk da irin soyayyar da take wa Maher hakan bai hana ta tsayu tsayin daka wajen ba shi ingantacciyar tarbiyya da uwa ta gari take baiwa yaranta ba.

     "Su inna an daiyi sallah, san nan dan Allah ku barta ta huta, ai ba kanta farau ba kuma ba ฦ™arau ba! ฦ™addara ai tana kan kowa Haba mana" cewar Samha, ษ—aya daga cikin yan matan nan uku. 

      Doguwar tsuka umma taja haษ—i da faษ—in "Kece bakin ta, ita bata iya magana ba ne? Toh ahir ษ—inki! Kar ki kuma ana mata magana kina sa baki,nasha kwaษ“an ki bakya ji! Amma..." Ta ฦ™are maganar da jijjiga kai.

       "Sa'a ki ka ci  bakya a kusa dani da na buge maki baki gobe baza ki kuma ana ma wata magana ki saka baki bah" Cewar Mama..........โœ๐Ÿป


Toh jama'a wannan karan ina muka kawo kan mu ne haka?๐Ÿค”



***


Shere fisabilillah

***