INUWAR DUTSE.......

Episode 3

by @rabearhwakili

🗻INUWAR DUTSE....🗻


_Rabi'a wakili_

 

Ep 03


Bismillahi Rahmanir Rahim.

★...

       ♡♡♡ ♡♡♡


         


_____________________


ꨄꨄꨄ



        Aysha da dake a É—aki har bacci ya fara É—aukar ta, kamar daga sama taji kukan maher, ba shiri ta miÆ™e zaune tunanin ko dan ta sa a rai ne shi yasa take jiyo kukan sa, sai dai ta tabbata ba mafarki bane jin har ta farka tana jin kukan sa, ga muryan su Abba da uncle Isma'il tana ji, har ta tashi zata fita sai kuma ta fasa, baza ta iya zuwa wajen su da sunan zata É—auki maher ba, tana da kawaici sosai a kansa duk kuwa da irin son da take masa,fasawa tayi ta koma ta zauna, tana dai ta jin su har dai maher yayi shiru a san nan ne ta ji wucewar uncle Isma'il. 

      Yana fita Abba ya É—aura da faÉ—in, "toh sai ku wuce kuje ku kwanta koh?, banda bin kwaf mi na fitowa bayan uwar da ta haife shi ma tana ji amma taÆ™i fitowa sai ku yan niman suna". Babu wacce tace uffan ta koma É—akin ta, ganin wucewar su yasa ya shiga kwala kiran Aysha kamar ba dare bah. Kafin ta fito, sai ga shigowar Hanifah ita da samha, a É—age suka É—aga masa hannu har zasu shige ciki a kausashe,?ya daka masu tsawa da ya haifar masu da tsayuwar dole, da matsanancin mamaki fiye da tunani sam basu yi tunanin haka daga gare sa ba, yaushe rabon da Abba ya É—aga musu murya, yaushe rabon Abba ya yi musu haka a matsayin uba? Sun manta tun kafin sukai haka amma yau shi yake daka musu tsawa a matsayin muryan uba, ba su kaÉ—ai bah har Aysha dake a baya sai da mamakin haka ya daskarar da ita. 

      Jiki a sanyaye haÉ—i da tsoron da ya yi musu shigar É—aya, suka juyo gare sa, sai dai abinda ya daure masu kai fuskar nan tashi na nan a sake ba wata damuwa, sauke ajiyar zuciya sukai ba su kaÉ—ai ba har su umma da suke hange ta window, "icce kuka gani da zaku zo ku wuce sa?" Yayi maganar kamar  yadda ya saba a kullum, "san nan nawa kuka samo?" Ba tare da sun amsa masa ba suka buÉ—e jaka zasu fiddo da abinda suka samo, nan kam murmushi mai faÉ—i da yalwa ya cika masa fuska, har ya tara hannu zai karÉ“a umma ta riga shi, ta amshe duka tana binsa da kallon banza da kallon mutum mara amfani. 

       "Wlh Mallam bazan baka kudin nan ba, baka san ci da shan mu ba, sai dai mu mu nema mu baka? Toh ba zan bayar ba,?cefane za'a yi dashi idan Allah ya kaimu, kai ma ka amfana, amma ba zan baka ko biyar ba ka kaima gidan chacha da baka taÉ“a cin moriyar shi ba yauwa, ka dai jira idan ka samu kuÉ—in kanka sai kaje kai tayi ba dai da kuÉ—in yaran mu....." Hauren da ya kai mata shi ya katse ta ba shiri, ganin ya dumfaro ta a zafafe ysa ta wurga É—akin ta, da Allah ya taimaka a buÉ—e ta barshi, tana shiga ta datse da key. Bubbuga Æ™ofar ya hau yi kamar zai Æ™alle Æ™ofar saboda tsananin bugu.

      "Dan Allah Abba ka daina dare ne fa, Mutane zasu shaida halin da muke ciki fah" cewar Samha. 

   a fusace Abba  ya furta "idan sun sani sai me akwai abinda basu sani bane daga cikin Rayuwar gidan nan bane? tunda kun maida kanku yan terere" ya Æ™are Maganar da buga kofar da Æ™afa da Æ™arfi, a dai dai nan maher da ke hannun sa ya tsaga ihu dan bugun ya firgita shi.

    ALLAH ya jarabce shi da son maher hakan yasa lokaci É—aya ba shiri ya natsu ya hau buga bayan sa alamun lallashi. Har sai da yayi shiru san nan ya cigaba da buga kofar da zuba duk tijarar daya ga dama. Itama daga ciki tana maida masa da martani. "Dan Allah Abba kayi haÆ™uri ga wannan in Sha Allah idan Allah ya kaimu sai na cika maka sauran" nutsuwa kuwa yayi tsaf, hannu har rawa yake wajen karÉ“an kuÉ—in, bata jira cewar shi ba ta tara hannu zata amshi maher ya hana, ganin haka yasa ta shige ciki daman Hanifah ta dade da shige tun kafin su fara tijarar su.

      Da murna sosai Abba ya chusa kuÉ—aÉ—en a aljihun rigar sa haÉ—i da kwala kiran sunan Aysha. Da sauri tasa hannu ta É—auke hawayen fuskarta na tausayin halin da suke ciki. Fitowa da ga inda take ta isa inda yake.

       Cikin sanyin murya kalau ta furta"Abba gani" "na ganki mana! Kin kuma kyauta, kin ma kanki, dan wulaÆ™anci kina jin yaron nan na kuka kuma kin san ke yake biÉ—a kin masa banza, dake baki damu dashi ba idan ma abin cutarwa ne sai dai ya cutar da shi kenan dan baki son sa? Kin san baki buÆ™atar shi mi yasa kika samo cikin sa?".

     Ita dai shiru bata ce komai ba, dan bata da abin faÉ—i, lamarin Abba ba'a iya masa, yanzu da ace ta fito sai ya shuka mata rashin mutumcin da kaf anguwar sai anji, gashi duk gudun da tayi bata tsira ba.

       Cigaba Abba yayi da faÉ—in "toh Ni Inason sa yafi min ke so dari da Æ™ari, dan baki da wani amfani gare ni". magana yake amma maher sai faman kiciniyar a sauke shi yake haÉ—i da É—aÉ—É—aga hannayen sa a dole yaga mahaifiyar sa. Cikin takaici Abba ya dungure masa kai, ba tare da ya kuma cewa komai ba, ya dungurar mata da shi ya shige É—akin sa.

     Yana jin sa a jikin Aysha ya lafe luff, haÉ—i da sauke ajiyar zuciya, shafa bayan sa tayi san nan ta shige É—akin ta dashi.

  Tana shiga ta kwantar dashi bisa gado har ya bare baki zai fara mata kuka fuska ba wasa tace "Allah ya baka Sa'a kamun kuka sai na maida kai inda ka fito, tunda kai baka san kara ba, baka da yarda kamar wanda za'a je a siyar" dariya ya kyalkyace dashi dake yaron akwai sa da wayau sosai. Kwanciya tayi itama a gadon tana lakace masa pointed noise da y gada a wajen ta, dariya ya kuma yi gefen kumatun sa na dama suna loÉ“awa, faÉ—awa yayi jikin ta. Yana son cigaba dayi mata rigima, "kayi! Zan wurgar da kai ne a wajen ummo ta cinye ka" É—if yayi babu wani jimawa bacci ya É—auke sa daman Bacci yake ji barin ma gashi yasha kuka. 

    Gyara masa kwanciya tayi ta shiga binsa da kallo, lokaci É—aya tausayin yaron na Æ™ara shigarta a rai, da tsoro mai tsanani, tasan nan gaba idan ya girma zai tambaye ta ina baban sa, bata fatan wannan ranar, gudun haka kuwa, matsayi biyu a zata taka a rayuwar sa, wato ta zame masa uwa da uba.

      Shafa sumar kansa data kwanta yayi luf tayi a hankali kafin ta zuba masa ido, sak da sak yake kama da ita har hasken fata ba abinda ya baro nata da bai É—auka ba, sauke ajiyar zuciya tayi haÉ—i da manna masa sumba a goshi tayi musu addu'ar bacci ta shafe masu jiki dashi.


LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_


*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*


ALƘAWARIN SARAUTA

Jidderh Galadima


SARƘAR DUHU

Oum Fadeel


ALEENAH ALEEM

Aid Walee


INUWAR DUTSE

Rabi'a wakili


₦500

Via

9119359211

Moniepoint

Rabi'at Sani Adamu

Sai katura shedar biyanka anan👇

***