NANNY(MAI RENO)

23

by @jamilaumarjanafty

*NANNY...!*
    _(Mai Reno..)

*Na*

*AISHA ALTO*
*JAMILA UMAR (Janafty)*

*HIJABS CORNER BY JANAFTY*

*Muna da Hijabai masu kyau da inganci, ɗinki cikin kwarewa da* *mabambanta design,  muna aikawa da kayanmu ko'ina a Nigeria, muna maraba da masu siyan ɗaya ko sari.*
****, tuntuɓa ta wannan lambar*
*KADUNA/ZARIA*

   *BABI NA ASHIRIN DA UKU*

Ranar da Innaro ta tafi Farida ta samu Mufeeda a cikin Ɗakinta tana bama Ayman Nono Domin shiyafi Airah rigima, Gefenta ta Zauna Tana Faɗin "Kina nan Ashe..? Ina Airah take ne..?

Mufeeda tace "Wlh Ayman ya tashi Da Rigima ni nagaji da Tsotsan nan nashi Momy.." Hararanta tayi kafin tace "Kin me..? Lallai Awo ki Yarinya don sai sun Shekara 2 zaki yayemin yara.." Shagwaɓe Fuska tayi tana Faɗin "Kai Momy.."

Bata bi ta kanta ba ta fara faɗin "Kinsan Abunda Nake so Dake..? Mufeeda ta girgiza kai Farida ta cigaba da Faɗin "Yau zaki karɓi girki ma'ana Yau kece keda Abban Basma.." Ido Mufeeda ta Zaro gabanta na Faɗuwa Kallonta Farida tayi tana Faɗin "Eh Sai ki Shirya, yanzu tashi zakiyi mu shiga Kichen tare muyi Dinner, kinga ya kamata ace mun gyara komai bai dace ace yana da mata har guda biyu ba amma ace kullum Sai dai Iya ta girka ta bashi yaci ba sai na yanke Shawaran Duk wacce keda miji Ranar toh zamu Shiga kichen tare mu taimakama juna ko ya kika gani..?

Mufeeda ta Sadda kai ƙasa Tana Faɗin "Duk Abunda kika yanke Dai-dai ne Momy.." Kafaɗarta ta Dafa tana Faɗin "A'a karki ce Haka kema fa matar gidan nan ce kina da Hakki kan komai.." Mufeeda batayi magana ba Farida ta cigaba da Faɗin "Iya zata shi ci gaba da taimaka mana wajen kula da Airah da dai Sauransu.." Kai Mufeeda ta gyaɗa tana Faɗin "Hakan yayi Momy.." Sun daɗe suna hira kafin Ayman ya gama shan Nono Farida ta ɗaukeshi su Fito Falo, Su miƙawa Iya wacce ke goye da Airah tayi barci an samu 'yar Rigima Naila an tafi islamiya, Farida ce ta miƙa ma Iya Ayman ta faɗa mata Shawaran da suka yanke taji Daɗi sosai, Ko babu komai yanzu Tahir zai Fara Ɗanɗanan daɗin Aure.

Farida da Mufeeda Haka suka Zage suka Shiga Sukayi girki mai rai da lafiya, Tuwon Shinkafa suka yi miyar Agushi saboda Tahir yana bala'in son Tuwo ga miyar taji man Shanu da naman rago zuƙu-zuƙu, Zobo suka haɗa suka sanyashi cikin Fridge, Dai-dai Dawowarsu Basma Daga Makaranta suka gama komai har gyara kichen ɗin Farida ta Fita ta bar Mufeeda na wanke wanke Abun da suka ɓata, Su kansu yaran sunyi matuƙar mamaki ganin Duka iyayen nasu acikin kichen suma sun Nuna murnansu suna tsalle Cewa yau zasu ci girkin Momy dana Aunty Mufeeda.

Farida ta matsama Mufeeda taje tayi wanka itama Sama ta Haura ta Shiga wankan, Bayan ta Fito tayi sallar Magriba ta Shirya cikin wani ubansun Leshi Riga da zani batayi kwalliya ba amma Tayi kyau sosai Tana Fesa Turare taji Ihun yaran suna Faɗin Daddy oyoyo Murmushi tayi tana Ƙoƙarin Ɓoye Abunda ke Taso mata acikin ƙasan Ranta ta Fito Tun daga saman Steps d'in yake kallonta yana Riƙe da Naila harta ƙaraso tana Faɗin "Sannu da zuwa Abban Basma.."

Murmushi ya sakar mata yana Faɗin "Yauwa Umm Airah ko..? 'yar Dariya tayi Briefcase ɗinsa ya Miƙa mata ta maƙale kafaɗa tana Faɗin "Yau bani keda kai ba Mufeeda ce.." Duk da acikin Ranshi yaji daɗi domin wajen Wata goma kenan yana Fatan sake komawa wannan ƙorama amma sai bai nuna ba yawani Ware ido yana Faɗin "Bangane ba..? Baki ta murguɗa mai tana Faɗin "Baka gane ba ko..? Zaka gane anjima.." Dariya yayi yana kallonta saboda yarda tayi magana su Basma kuwa Tuni sun Wuce ɗakunansu, Farida ce ta Ɗaga Murya tana Faɗin "Mufee...Wai me kikeyi ne Haka bakiji Shigowar Megidan naki bane...? Ta faɗa tana Murmushi.. 

Mufeeda Dake laɓe Tun Ɗazu ta kasa Fitowa saboda kunya ta Fito kanta Sunkuye tana Faɗin "Gani Momy sallah na idar..." Ajiyar Zuciya Tahir ya sauke yana kallonta ƙasa ƙasa Tana Sanye cikin Riga da Siket na wata atamfa wanda yasan Mufeeda abaya ba wanda zai ce itace yanzu domin Mufeeda yanzu haihuwa da Namiji Sun Buɗata tayi kiɓa kamar ba ita ba hips da nonuwa kuwa sun cika ko'ina, ƙarasowan tayi ta ranƙwafa tana faɗin "Sannu da zuwa Daddy." Amsawa yayi yana kallon Fuskarta ido cikin ido Farida Dataga Haka sai ta wuce kichen tana Faɗin "Ki bishi Sama ki Taimaka mai yayi wanka Mufee, kafin ku Fito na Shirya Tebur.." Ta faɗa tana Shigewa kichen da Sauri kamar zata faɗi Domin bazata iya jurar irin wannan kallon Sha'awan da Tahir ke bin Mufeeda dashi ba.

Ganin ta tsaya tana Wasa da Hannunta yasa kawai ya juya ya fara Haura step Naila kuma Tun ɗazu ta sauka Daga hannunsa tabi Basma Ɗakinta cikin Sanyi jiki tabi bayansa yana jin takunta ya mata banza Har Suka Shiga bedroom ɗinsa, ko kallonta baiyi ba ya ijiye Jakar Briecafe ɗinsa da wayarsa ya Buɗe Ƙofar Toilet ya Shiga Haushinsa Ɗaya da Mufeeda Yadda komai wai sai Farida tace mata tayi Zatayi alhalin yana da tabbacin Daga Iya har Innaro basu barta Haka ba.

Kuma yayi gaskiya domin Innaro ta mata nasihan ta kuma ta bata wasu Shawarwarin, ƙara zama da Miji, Harda gyaran Jego Haka Innaro ta Tiƙe ta ma Mufeeda, kayan lambun nan Duk matsa mata take tana Sha Tsarki da ruwan zafi mai bagaruwa, shan madara da Zuma, kuma kafin ta tafi ta tarasu ita da Farida ta sake musu nasihan Zama lafiya, Amma Duk mufeeda tayi biris tana jiran komai sai Farida tace tayi kana zata Da Haushin Abun ya gama wanka ya Ɗauro alwala ya Fito Kansa Ɗaure da karamin Towel yana goge kansa Jikinsa kuma sanye da wani baƙin dogon wando Tana nan tsaye inda ya barta yana ganin Haka yace "Kinga ki Tafi kawai Nagode.." faɗin haka da yayi yasa ta Ɗago kanta suka Haɗa ido saurin kauda kai tayi ganin Ƙirjinsa yana waje ga gashi Duk ya kwanta cikin kasala ta ƙarasa kusa dashi tana Faɗin "Kayi haƙuri Daddy..."

Kallonta yayi yana Faɗin "Baki man komai ba Mufeeda Abu Ɗaya nake so ki gane yadda nake Mijin Farida haka kema nake Mijinki.." Gyaɗa kai tayi kanta na ƙasa tace "Bazan ƙara ba.." Ta faɗa Muryanta na rawa ganin Haka yasa ya Riƙo kafaɗunta yana Faɗin "Meye Abun kuka..? Kinga Zauna na gama Shiryawa mu sauka tare.." Ya faɗa yana Zaunar da ita Kan gado shi kuma ya juya yana neman kayan da zai saka Wasu Riga da wando ya saka ƙirar Armani ya Taje kansa sai gashi ya fito kamar ɗan Saurayi dan Shekara Talatin da Biyar, Tana ta satar kallonsa bai nata magana ba, sai da ya gama kana ya Riƙo Hannunta ya miƙar da Ita yana Faɗin "Muje ko.."

Kasa kallonshi tayi ta sadda kanta ƙasa, har suka Fito Daga Bedroom Farida na Saman Dining bayan ta gama Shirya komai ita da Basma da Bassam da Naila da Iya, Hangosun da yayi yasa ya saki hannun Mufeeda saboda idanuwan yaran, Farida ko Sau Ɗaya ta kallesu bata ƙara ba Har suka ƙarasa Saukowa, Farida Jikinta na rawa Ta ja musu kujeru suka Zauna yana amsa gaisuwan iya Cikin Fara'a yace "Ina su Airah...? Farida Tace "Har sunyi  barci kasan su Da sunji Ruwan zafi Shikenan.." Bai ce komai ba Illah Basma Da tace "Daddy yau fa girkin Momy zamu ci dana Aunty Mufeeda." Baki Tahir ya washe yana Faɗin "Realy...? Lokaci Ɗaya yana kallon Farida Ita kuma tana kallon Mufeeda Suna Dariya hannu yasa bisa Ƙirji yana Faɗin "Uhm..Lalle Tahir ya zama Ɗan gata.."

Ya faɗa yana Murmushi Farin ciki ya Cika ranshi, ba wanda ya ƙara magana har Farida ta sallami kowa suka Fara cin abinci, Tahir kuwa ya Zuba santi kamar ba gobe har Farida na saka mai Waigi Ranar Haka Suka gama cin abinci Cikin Farin ciki wanda Suka Daɗe basuyi ba bayan sun koma suka koma Falo Suka Zauna suna Hira da 'ya'yansu Har su Airah suka tashi Iya ta kawo ma Mufeeda ta basu Nono bayan ta gama ne Tahir ya Ɗaukesu yana Musu Wasa Farida bata bari Hiran yayi tsawo ba tace kowa ya wuce ɗakinsa yayi wanka yayi sallah kafin ya kwanta Tun da yau basu Fita sallah ba...

Ita ta karɓi Su Airah tana Faɗin "Allah tashemu lafiya...Ango Asha Amarci lafiya.." Ta faɗa ta Wuce da Sauri Jikinta na Ɗan Rawa Sabida yadda wani Duhu ya mamaye mata Zuciya, Da kallo Suka Bita Tahir ne kaɗai ya amsa mata da Allah tashemu lafiya.

Miƙewa yayi bai tsaya wata magana ba ya Riƙo hannun Mufeeda ya miƙar da ita Tsaye kuma bai yarda sun Haɗa ido ba suka Nufi Bedroom ɗinshi, Ita kuwa Farida kan gadonta ta kwantar dasu Airah Itama ta Sulale tana Sakin kukan Data ke Danewa wani kishin Tahir ne ke taso mata, Sheɗan na Zugata amma tana ƙoƙarin yakiceshi Da ƙyar ta miƙe ta Faɗa Toilet tana Rangaji.

Suna Shiga Bedroom ɗin Tahir ya saketa yana Faɗin "Ki shiga ki ɗauro alwala.." Bata yi musu ba ta Shiga ya bita da kallo yana Murmushi bata jima ba ta Fito tana Faɗin "Daddy na Fito.." Kallonta yayi kai tsaye kafin yace "Sallah zamu yi.." Kai ta gyaɗa kafin tace "Bani da Hijabi anan Ɗakin.." Bai mata magana ba illah Ficewa Da yayi har Zuwa Ɗakinta ya Buɗe Wardrope ɗinta ya Ɗauko mata Hijabi da wata Arniyar Rigar barci ya kawo mata Duk Farida najin Fitarshi da Dawowarshi tana Zaune kan sallaya bayan ta idar da sallah Hawaye na Zuba daga cikin idanuwanta..

Miƙa mata yayi Haɗe da Rigar barcin yana Faɗin "In mun idar sai ki saka wannan rigar barcin.." Ido ta Waro Tana Faɗin "Kai Daddy.." hararanta yayi ya wuce bai mata magana da Sauri ta kama bakinta tana Faɗin "Bazan ƙara ba." Murmushi kawai ya saki shima ya Faɗa Toilet d'in Mufeeda daban take, Komai tayi cikin bada Haƙuri take, Alwala ya Ɗauro Shima ya Fito kafin yajasu sallar sai da sukayi sallar Isha'i kana yajasu Raka'a Huɗu bayan sun idar ya dinga kwaroro musu Addu'ar zaman lafiya Mufeeda na amsawa da Ameen.

Tashi yayi ya isa saman Side Drower d'in gadon ya Ɗauko Madaran Hollandia ya Tsiyaya cikin Kofi ya cikashi yazo gabanta ya Zauna ya miƙa mata ta saka hannu zata karɓa ya Girgiza mata kai yana nuna mata bakinta ganin yadda ya Haɗe Rai, yasa ta buɗe baki ya shiga bata sai da tasha fin Rabi, kana ta kauda kai bai matsa mata ba shima sai ya ƙafa kai ya ƙarashe Shanyewa ya Miƙe ya maida komai inda ya Ɗauko kafin ya Dawo Agabanta ya Ƙara Zama wannan karon gwiwowinsa yana Gugan nata, Lokaci Ɗaya ya Riƙo Hannnayeta yana Faɗin "Kinga kalleni.." Ɗagowa tayi tana kallonsa Cikin kunya ganin yadda yake mata wani kallo yace "Ki saki jiki dani mana Mufeeda bana son Abunda ki kemin kinji..." Gyaɗa kai tayi tana Faɗin "Bazan ƙara ba.." Hannunta ya Sumbata yana Faɗin "In kika ƙara sai na Hukuntaki.." Jikinta ya mutu cikin Sanyinta ta langwaɓar da kai tana Faɗin "Allah bazan ƙara ba.."

Yana yar Dariya yace "Naƙi wayon..? Hukunci ne baki so ko..? Ta gyaɗa kai bazato ba Tsammani taji ya kama kanta ya Ɗora Leɓensa bisa nata ya Fara Tsotsa Lokaci Ɗaya taji jikinta ya ɗau kyarma jin Baƙon lamari ya Daɗe yana Tsotsan Leɓenta Cikin Fitan hayyaci ta saki Bakin nata har ya kama harshenta, cikin ƙwarewa yake Sumbatar ta lokaci Ɗaya yana maida Numfashi sun Ɗauki Tsawon Lokaci kafin ya saketa ya koma kuma ya Kwantar da kanshi Bisa Ƙirjinta yana maida Numfashi Itama jikin gado ta maida kanta tana Sauke Numfashi Cikin Shakewar Murya Tahir yace "Koda irin wannan Hukuncin ne Mufee..?

Ba tayi magana ba illah Runtse ido Datayi wani yanayi na Shigarta Jinsa Acikin Jikinta, bai ɗago ba sai da ya Daidaita kansa kana ya Tashi Lokaci Ɗaya ya Ɗagota Suka miƙe tare Hijabin jikinta ya Cire mata yana Faɗin "Ki saka Rigar barcin Mufee, I need u bazan miki ƙarya ba karki jamin Rai plz.." Ya faɗa yana ƙura mata Lumsassun idanuwansa Da Suka Fara Chanza Launi, Rigar barcin ya Ɗauko ya miƙa mata Shi kuma ya Buɗe Wardrope ya Ɗauki wata jallabiyarsa ya Shiga Toilet saboda ya bata daman Shiryawa, cikin Sauri ko ta kwaɓe tana yi tana kallon kofar Bedroom d'in, Tana ƙoƙarin Saka Hijabi ya Buɗe ƙofa ya Fito da Sauri ya ƙaraso yana Riƙo Hijabin Cikin Wani narkakken kallo yake Faɗin "A'a bana so.."

Ya faɗa yana marairaice Fuska jin haka yasa Jikinta ya Mutu ta sakar mai tana kare Ƙirjinta Tunda pant ta bari kaɗai hatta bra sai da ta cire, Nonuwanta da Suka cika da ruwa sunyi ɓul ɓul dasu Bai tsaya Sauraranta ba ya rungumota ta baya ya saka hannu ya Cire Hannayenta Daga kan Ƙirjinta ya Ɗora nashi Lokaci Ɗaya yaja Numfashi Cikin Shinshinar Wuyanta lokaci Daya kuma yana Shafa Ƙirjinta Zuwa Wuyanta Cikin Lokaci kaɗan ya Rikita kansa kuma ya Rikita ta Domin Mufeeda Haka Ta saki jikinta Sosai Tun Suna Tsaye Har Suka Danganta Da kan gado Cikin Dubara Tahir ya saka hannu ya kashe Wutar Ɗakin ya Kunna Dum light.

Cikin ƙwarewa Yake Sarrafa Mufeeda Ƙirjinta Su sukafi Jan Hankalinsa kuma suke Rikitashi, Itama banƙaro mai ƙirji kawai take tana jin Wani Daɗi na Tsirga mata Har ya Saɓule Rigar barcin bata sani ba kai Tahir ƙarshe ne ya kai makura wajen iya Sarrafa mace, Domin ko'ina na Jikin Mufeeda sai ya amsa Domin babu inda bai bi ya lashe da Harshensa ba Mufeeda ta Haukace sosai Lokacin da Bakin Tahir ya kai ƙasanta Haka ta Riƙe kanshi tana kukan da batasan ko na mene ne ba, Ya gama Rikita ta Shima ya Rikita kansa bata yi Aune ba Taji ya Sunkuyo da kansa yana karanta addu'ar Saduwa da iyali ya haɗe bakinsu Waje Ɗaya, kafin ya Danna kai sai Lokacin Mufeeda ta dawo Hayyacinta jin Azaba na cinta ta Shiga Tureshi amma Ina ta makara domin da ƙarfinsa ya Danna kai cikin magagi Tahir yace "Ya salam..." jinshi Tsundum cikin ƙoramar Daya Daɗe yana mafarki bai tsaya wasa ba ya Shiga Haƙarta cikin Zaucewa da Fitar Hayyaci, Kuka Mufeeda keyi Domin tasha gyara ta koma ta Haɗe duk da Azaban bai kai na Farko ba amma ta Ɗanɗana.

Sai da ya shafe minti Arba'in yana Abu Ɗaya kafin ya ƙanƙameta yana Sakin Numfashi, Haka ya ƙanƙame Mufeeda yana Kwarara mata albarka Tana kuka tana komai ya Ɗauketa suka Shiga Toilet ya gasata kana sukayi wankan Tsarki Suka Fito Domin Tun Mufeeda najin kunyarsa har ta ware Domin karatun Daddyn nata ya Girmi Shekarunta Naɗota yayi Cikin Towel Suka koma Suka kwanta Ya Rungumeta Yana mai Jin Wani farin ciki sosai, Barci Tuni ya sace ta Shima Daga baya barcin ya Tafi dashi mai Daɗi.

*****
Da Asuba ma tare sukayi wanka Mufeeda sai Zille zille take, Shiko ko Ajikinsa, wajen wanka ma sai da ya ƙara morewa son Ranshi kafin suyi wankan Su Fito, Ya barta shi kuma ya saka kaya agurguje zuwa masallaci yau ɗin ko Tsayawa Ma Sauraran Wa'azin da akeyima kullum Safiya bai tsaya ba jiki na rawa ya Dawo gida Mufeeda na cikin bargo ko kaya bata saka ba Tunda bata da kaya a ɗakin ya Sake Ƙwaƙumarta Mufeeda taga ta kanta Domin Duk Kukanta sai Da Tahir ya sake, Sai Da ya samu natsuwa sosai kana ya Rungumeta yana lallashinta ita ko Tana tamai Taɓaran Shagwaɓa Yana biye mata Abun na ƙara Rikitashi, kwanciya sukayi Daga nan kuma sai barci Sai Wajen 9 suka tashi, wannan karon kuwa Mufeeda taga Abun Da ya isheta Cikin Jazucci haka yake lasanta kamar zai Cinyeta Ɗayan Cikin Kunya da Nauyi tace "Kai Daddy..."

Yana wasa da Boobs Dinta da Suka Sake cika Yake fadin "U better stop calling me ur Dad...Ni ba babanki bane.." Cikin Tura baki tace "Kai Babana ne.." Bai bata amsa ba sai da ya Tsotsi bakinta kana yace "Babanki bazai miki irin Abun da nake miki ba.." Ya faɗa yana kashe mata ido Ɗaya ƙirjinsa ta faɗa tana mai Dukan wasa Da ƙyar yayi wankan Tsarki ya fice ya barta bayan ya gama latsata son Ranshi gasa kanta tayi kafin tayi wankan Tsarki ta Fito, Jin Nonuwanta nata Zuba ne yasa ta gane Su Airah sun tashi suna kuka Tahir ta kallah wanda ke murza Hulan kansa tace "Daddy su Airah sun tashi..?

Yana Ɗaure agogon Hannunsa yace "Eh Suna wajen my Farida karki damu muje.." Hijabi tasaka Bayan Towel na Daure Ajikinta Suka Fice Daga Ɗakin, Suna Zuwa Falo suka iske Farida na goye da Airah, Ayman na Hannunta tana ta Faman Jijjigashi yana kuka Tahir ne ya samu daman ƙarasowa gareta ta gaisheshi ya amsa yana karɓan Ayman Cikin Kauda kai Mufeeda ta gaida Farida ta amsa itama bata kalleta ba da Sauri ta Shige ɗakinta Sauri Sauri ta saka wata Riga da Zani na les cikin kayan Tariyar da Tahir yayi mata ne, Ta Fito Zata karɓi Ayman Farida ta Hana tace su Fara karyawa Tukunnah gidan babu kowa Sun Tafi makaranta Harda Naila itama an saka ta Iya ce kaɗai ke Kichen tana Wanke wanke, shi kuma ya kama Hannun Mufeeda suka Nufi Dinning d'in tana ta Zillewa amma Tahir yaƙi sakinta Farida Sau Ɗaya ta kallesu ta juya kanta tana ta Jijjiga Ayman dake Hannunta, Idanuwanta suna Fitar da Ƙwallah domin Daga yanayinsu ta san komai ya sake Faruwa Saurin koran Sheɗan Tayi.

Ko wajen cin Abinci Haka Tahir ya dinga tsokanar Mufeeda ita kuma kunya Duk ya kamata, Farida Data ga Haka sai ta koma sama kawai abunta bata son ganin Abunda zai sa Aga Rauninta, Tana Tafiya Mufeeda ta marairace tana Faɗin "Don Allah Daddy ka bari kaga Momy taji ba Daɗi har ta koma sama.." Shuru yayi kafin yace "Hakane...Bazan ƙara ba Cutie.." Ya faɗa yana lakace mata hanci Dariya tayi Suka Cigaba da cin Abincin nasu cike da ƙauna Lokaci Ɗaya suna aikama juna kallon Soyayyah da ƙauna mara yankewa.

Haka rayuwar gidan Tahir ya cigaba da kasancewa cikin Murna da Farin ciki da Zaman lafiya Abun sai wanda ya gani, duk wacce keda miji zasu haɗu suyi girki tare komai nasu gwanin ban sha'awa Wahalan Renon su Airah kuwa Farida ne da Iya Tsakaninsu da Mufeeda kuwa sai in zata basu Nono Farida na bala'in so wad'annan 'ya'yan gashi ita kuma Haihuwa Shuru Duk da taje Asibiti An buɗe mata bakin Mahaifa amma kuma Har Zuwa Wani Lokaci Shiru sai ta maida Hankalinta wajen Kula da Su Airah kamar ta lashesu Saboda yadda Take bala'in sonsu.

Zamansu gwanin ban sha'awa ko Su Umma suna alfahari da Chanzawar Farida, hakama chan Ɗanbatta Hakimi hankalinsa ya kwanta ganin Walwalar Ɗansa ta Dawo Awajen Aiki kuwa Ishaq sai ma Tahir Tsiya yake wai yaji daɗin Mata sai kiɓa yake yana Tumbi kuma da gaske ne Domin Tahir ya samu kwanciyar Hankali sosai, Duka matan nashi suna ƙoƙarin kyautata mai shima kuma yana ƙoƙarin kwatanta Adalci Baya nuna wanda yafi Wani Afili sai dai ya bar kanshi kawai Ɓangaren Mufeeda kuwa dama Akwai ɓoyayyiyar soyayyar Daddynta Cikin Lokaci ta Fito Dashi, Bata mai gardama komai ya keso shi take mai shiyasa Cikin Lokaci ƙanƙani ta mamaye mai Zuciya, gashi baya gajiya da ita kamar yadda itama bata gajiya dashi Farida kuwa Tana da matsayi sosai amatsayin ta na Uwargida kuma uwar 'ya'yansa Uwa uba kuma Dalilin ta ne Zaman lafiya ya Zauna a gidan Tahir Yanzu Zumuncinsu ya Dawo Sabo da Zahra matar Ishaq, Bilkisu har gida tazo tana Zugata wai ta zama baiwar Mufeeda ta zama mai mata rainon 'ya'ya, nan tayi mata Fata fata ta koreta Ta watsar kuma da duka ƙawayen banza ta riƙe Mufeeda da Zahra kawai domin Samun Sukunin Zuciya Tana ƙoƙarin Ɓoye Kishinta Saboda Tahir na kwatanta Adalci a tsakaninsu...

*******

*AFTER 5 YEARS*

Bayan Shekara Biyar Abubuwa Da dama sun Faru na Farin ciki da Akasinsa amma Aciki na Farin cikin yafi yawa Domin A shekarar Data gabata ne Iyalan Tahir suka tattara suka koma Lagos a Victoria Island, Inda ya gina wani katafaren gida Haɗe da katafaren Kamfani mai Taken *ƊANBATTA MOTORS LIMITED* da guminsa, Bayan ya barma Ishaq wanchan kamafanin na Abba a Kaduna yana kula Dashi, saboda amanarsa da Hazaƙarsa Duk da Dukkansu Cigaba ne ya Samesu amma Sunyi baƙin cikin Rabuwa da Juna.

A waɗannan Shekarun Tahir ya ƙara zama magidanci domin Arziki yaci uban nada, Baga iyalansa kaɗai ba Hatta ga iyayensa ma suna yabansa, Garinsa ko Ɗanbatta basu da abun alfahari sama dashi, yana ƙoƙarin Biya musu Buƙatunsu, ya gina musu Rijiyoyi da kuma Bohol, hadda k'aramin Asibiti ya gina musu mai suna MANSUR CLINIC, Abun sai wanda ya gani Ashe kuwa Yanzu ta zama Hajiya Aisha Tuni Tahir yayi ma Mijinta hanya ya samu aiki a kamfanin Abba Dake Kaduna in da ya bari suna aiki tate da Ishaq, Sun bar garin Ɗanbatta Tuni suka koma Kaduna da zama, Baba Hakimi babu Abunda ke Shiga Tskaninsa da Tahir sai godiya da Fatan Alheri, haka su goggo Komai na Jin Daɗin Rayuwa ya mallaka musu, Duk Da Baba Hakimi ya Tsufa amma yana gudanar da Sha'anin mulkinsa Domin ya Jiƙu da Hutu da Jin Daɗi Tuni Tahir ya maida Garzali makaranta yana Ɗaukan Nauyin karatunsa, Rayuwa tayi kyau Abun sai wanda ya gani.


Su Airah nada wata goma sha Biyar Mufeeda ta sake samun Wani Cikin Farida ta karɓi su Airah ta yayesu ita kuma Mufeeda ta cigaba da kula da rainon cikinta, Lokacin har ta yi Jsce ta koma Makaranta,Sai da cikin ta ya Tsufa kana ta daina Zuwa Makaranta lokacin tana Ss2 ne Achan ko garin Ɗanbatta kowa Ɗauka yake cikin jikin Mufeeda Shine na Farko su Airah kuma Farida Ta Haifesu Tunda ba wanda ya sani sai su kansu da komai ya Faru suna nan, Hajiya Iya kuwa 'yan'uwanta sun so su Ɗauketa amma Tahir ya hana yace Ai Iya Ta Riga ta zama tamu Dole suka yi Haƙuri Suka ƙyaleta.

Na ƙara Haihuwan mace Ta ci Sunan Goggo Abu muna kiranta Ayda, tana da Wata Takwas na ƙara Samun wani cikin wanda nayi ta kuka Farida ko da Tahir nata Murna ta karɓi Ayda ta yayeta Lokacin su Airah suna Ɗanbatta wajen Innaro, cikina na wata Bakwai suka Tafi Aikin Hajji Dukkansu, Goggo Abu, Innaro Ashe, Iya, Tahir, Ishaq, Zahra, Farida, sai Abba da Umma da Baba Hakimi, Ashe da Mijinta da su Basma.
Ni Kaɗai kawai aka bari agida sai Maman Lantana ita ta Zauna dani har Suka Dawo Wacce nake Kallo tamkar mahaifiyata Lantana ma tana Kano abunta muna waya sosai itama, ta cigaba da karatu, Lokacin da suka Dawo Cikina yayi girma kwana goma da dawowarsu na Haifi Santalelen yarona Namiji wanda yaci sunan mahaifina muna kiransa Walid, Duka 'ya'yana Ba zaka ce ni na Haifesu ba Domin komai nasu yana Ɗakin Farida ne, itace uwarsu, Tsakani na Dasu Aunty Mufeeda ne kaɗai, in ka kalleni bazakace nine keda 'ya'ya Har Huɗu ba saboda yanayin Jikina, Bayan na Haihu da wata uku Ciki ya Ɓulla a jikin Farida Murnan da mukayi ba kama Hannun yaro bamu tafi Hajji ba Nida Tahir sai da mukayi Jarabawar WAEC da NECO lokacin Walid nada wata goma Sha Uku Na yayeshi na Damkama Farida da Iya, Bamu samu Tafiya ba sai da mukayi Walimar Buɗe kamfanin Tahir da kuma Tariyarmu Asabon Gidanmu kana Muka Tafi Ni dashi, kwananmu Talatin agarin Makka muka Wuce England, Mukayi kwana goma, sai muka Dira a India saboda nacema Tahir ina son garin mune Har America munsha yawo, Honey Moon da bamuyi abaya ba muke Ramawashi yanzu, Sai da muka Shafe wata biyu da wani Abu kana muka dawo Gida, koda na Dawo na kwaso Tsaraban Honey Moon, Munyi kiɓa munyi jajir alamun munsha Hutu Sosai Farida da yaran sukaje Filin Jirgi Suka Ɗauko mu Lokacin Cikinta Har ya Fito, Duka duka kwanan mu goma ne da Dawowa Duka yaran da Suka Tattara suka Tafi Ɗanbatta Hutu suda Iya da Maman Lantana, Su kuma Basma da Bassam Dama Suna chan Tun bayan Tafiyarmu Farida kuma ta tafi Kano Duba jikin Abba Nida Tahir kaɗai suka bari agida naso na Bita Amma Laulayin Ciki ya Hanani Sukuni Dole na Zauna agida.
 
Tun muna India na Nuna ma Daaddy ina son na Cigaba da karatu na, nan ko ya nuna bai yarda ba kuma bazai taba yarda ba ya tambayeni a faɗin Duniya mai na rasa nace mai babu yace toh matuƙar ban rasa komai na Duniya ba maganar karatu na barta Karatuna kenan na Zauna na kula da mijina Haɗe da 'ya'yana Lokacin Kuma ina Cigaba da Zazzage mai kwansa A duniya.

Maganar gaskiya ban Rasa komai na Duniya ba, Ilimin nan dai-dai gwargwado ina dashi waye wa ma Haka domin yanzu na zama babbar mace babu Abunda wata macen zata Nuna min game da Namiji Daddy ya riga ya gama Zama malami na kuma bango na Shi ɗin da gaske garkuwa ne agareni bai taɓa bari nayi kukan maraici ba ko sau ɗaya Koda yaushe Cikin bani kulawa yake, Yana tattalina kowani Jin Dadin na Duniya yana bani ni kuwa mai Zan je na Tsinta in na cigaba da karatun mijina na sona, iyayensa naji dani kamar su lashe ni ina da 'ya'ya Me zan nema nan Duniya wanda Allah bai bani ba..? Babu domin Bayan Iyayena da suka kawoni Duniya Bani da kamar Daddy shine Mijina, kuma bango na kana kuma Shi ɗin wata Garkuwa ne agareni.


*****

Ina Zaune Ina Sauke Numfashi Bisa makeken gadonmu Tahir Dake kwance cikin blanket na Mintsina ina Sakin Kukan Shagwaɓa Cikin barci ya Buɗe ido yana kallona Hankalinsa tashe ya Miƙe yana Faɗin "Cutie wai lafiya kike ta ƙananun kuka Tun Ɗazu..?

Ya faɗa idanuwansa da barci, Kan Jikinsa na Sulale ina Faɗin "Toh ba cikin ka bane ke Wahalar dani ba...Komai naci baya zama sai na amayar dashi.." Murmushi ya saki yana gyara min kwanciya Lokaci Ɗaya yana wasa da gashin kaina yace "Umh..Wato na gane so kike kawai Dai na Taɓaki ko..? Ya faɗa yana Kallonta Kwaɓe Fuska tayi kafin tace "Ni..Yaushe nace kai dai Daddy kace zaka min wayau da ka saba.." Bata ankara ba taji ya maidata ƙasanshi yana Faɗin "Ni Wlh ke kemin wayau koda yaushe cikin amshe min Kuzarina kike, ke ɗin fa da ba domin ina ƙarawa da maganin ƙarfin maza ba da Tuni kinfi ƙarfina.." Ya faɗa yana mata Dariya baki ta Buɗe Tana Kallonsa Lokaci Ɗaya ta fara Tureshi tana sakin mai kukan Shagwaɓa Shi kuma yana dariya Lokaci Ɗaya ya Kama bakinta yana Faɗin "Muyi aikin lada Cutie bayan mun gama nayi lallashin Gaba ɗaya.." Ya faɗa yana haɗe bakinsu waje Ɗaya, cikin Sauri itama ta tallabi kanshi, Suka Fara Sumbatar juna cikin ƙwarewa Lokaci Ɗaya suna ƙara Rikita juna da Salon da kowanne yasan yana Kunno Ɗan'uwanshi Sai da Suka Ɗauki Tsawon Lokaci kafin Tahir ya saki bakinta yana kallon Cikin idanuwanta yace "Cutie ina Sonki...Ina ƙaunarki ƙaddarar Data Haɗamu ta Alheri ce..Allah yayi miki albarka.." Ya faɗa cikin Sanyin Murna Rungumeshi tayi tana Faɗin "Alhamdulillah...Kai ne garkuwata..Mijina Abun alfaharina..Ina matuƙar Sonka..."

Ta faɗa Lokaci Ɗaya tana Haɗe bakinsu Waje Ɗaya, Cikin Zalama kowannensu ke aikama da Ɗan'uwansa Saƙo.

          
        *ƘARSHE...*


*ALHAMDULILLAH...*

*Tammat bihamdullah...godiyata ta tabbata ga Allah ( SWA) Wanda yabamu ikon Fara wannan Littafin kuma ya bamu ikon gamawa lafiya..Muna fatan Kuskuran da mukayi Allah ya yafe mana...Laadan da muka samu Allah yayi ma Tarraya damu daku waɗanda sukayi ta jimirin bin wannan labarin Ameen.*



*Janafty*
*Aisha Alto*