Miji goma(ba uba goma ba ne)

Chapter 4

by @sadiyaabdulrazak954

PAGE 4


   Yana shigowa gidan ya shiga ɗakin Gwaggo, da yake Maryam ta ji sallamarsa sai ta tashi ta fito, ta je ta laɓe tana sauraron su, Gwaggo tana ta tsara masa son ranta kamar a gabanta aka yi, sai da ta ji ya ce"Ki yi haƙuri don Allah Gwaggo bari na je na same ta". Sannan ta yi wuff ta shige ɗakinta, ta haɗe rai tana jiran ta ga ta inda zai fara, ya shigo da sallama, ransa a ɓace yake da abin da ta yi, amma sai ya kasa karaɓus saboda yana son Maryam, ya zauna a sanyaye ya ce"Maryam don Allah ki rufa mini asiri ki fita daga harkar yarinyar nan".

Ta ce"Na fita daga harkarta fa ka ce, kamar dai wata sa'ata, yarinyar da a haihuwar kaji na haife ta amma ta yi yunƙurin zagina..."

Ya katse ta da faɗin"To kin ji ke ma yunƙuri kika ce, ba ta zage ki ba, a kan me za ki dakar musu ƴa?"

Ta ce"To shi yunƙurin ba raini ba ne? Ai wallahi inda ta zage ni sai bakinta ya yi jini, kuma ni fa ban dake ta ba, sharri ne kawai ta so ƙullawa, kuma sai dai ya ƙare a kanku don yau zan bar muku gidan".

Ya yi murmushi ya ce"A haba, da wasa kike yi, babu inda za ki tafi ki bar ni".

Ta ce"Wallahi Nazifi da gaske nake, ba zan iya ba, bari na faɗa maka gaskiya inda na san haka zan samu gidanka da ban aureka ba, a ce daga aure sai saka ni ɓacin rai ake yi?"

Ya ce"Ki yi haƙuri don Allah! Komai zai daidaita in sha Allah, kuma ke ma fa har da laifinki, kin ƙi kwantar da hankalinki, yau da wuri zan shigo mu sha shagalinmu amaryata".

Ta taɓe baki, don ba ta da lokacin ɓatawa wajen nuna masa dole yau za ta tafi gida.

Ya ce"Kin yi girki? Na aiko cefane za ki iya yi mata tuwon yau ko sai gobe? Kin ga cikinta ita kaɗai ne ko kaɗan ne kin ji Sweety".

Takaici ya kamata, ta kwanta tana cewa"Don Allah ka tafi harkarka".

Shi ma ya kwanta kusa da ita yana cewa"Ba zan tafi ba, kin ga yi haƙuri tashi mu shiga kitchen ɗin tare sai na taya ki".

Ta ce"Wallahi Nazifi ba zan yi tuwon nan ba".

Zai yi magana suka ji Gwaggo tana ƙwala masa kira, ya tashi ya fita jiki a mace.

Gwaggo ta ce"Nazifi tun da ka zaɓi matarka ta huta ni na wahala to mu je ka koya min yadda ake kunna gas ɗin, sai na ɗora".

Ya ce"Haba Gwaggo za ta yi, duk fa ba yadda kike tunani ba ne, kin san Maryam tana da aljanu shiyasa wani abun sai an yi mata uzuri".

Gwaggo ta ce"Allah Ya sa tsamiya ce a kanta, wa za ta faɗawa aljanu? Ni da nake da guda saba'in a kaina na gado, zaman gidan nan fa idan ba zai yiwu ba tun wuri ka faɗa min na koma inda na fito".

Inda za ta koma ɗin tabbas da zai ji daɗin hakan, amma ba zai iya nuna mata yana so ta tafi ba, don haka ya ce"Ki yi haƙuri Gwaggo, bari na samo miki tuwon, gobe sai ta dafa miki".

Bai jira cewarta ba ya fita daga gidan. Ya siyo mata tuwon ya kawo ya koma kasuwarsa, ba tare da ya sake shiga ɗakin Maryam ba.

   Can da magriba Maryam tana sallayar da ta idar da sallah ta jiyo hayaniyar Gwaggo tana cewa"Wallahi Yasmin idan fitina za ki yi sai ki bar gidan nan, ga tuwo ki ce sai kin yi girki, alhalin ba iya kunna gas ɗin kika yi ba?"

Yasmin ta ce"Wallahi na ga yadda ake kunnawa, idan na kunna sai ki dafa min indomin don Allah, idan kuma so kike na kwana da yunwa shikenan".

Gwaggo ta ce"Rufa min asiri na mutu babu hakkin kowa a kaina, ungo siyo ashanar, don wannan matar ƙila ɓoyeta ta yi".

Maryam ra ƙufula, sanda ta fito Yasmin har ta fice, tana dosar kitchen ɗin ta fara jiyo ƙarar gas ɗin shuuuu alamar ta kunna shi, kuma wai ta tafi siyo ashana, a ranta ta ayyana lallai dole dai ta bar gidan nan, don ba ta shirya mutuwa ba, ta kashe gas ɗin ta fito ta ja ta tsaya a ƙofar kitchen ɗin.

Sai ga Yasmin ra dawo da saurinta, ta yi turus ganin Maryam a ƙofar kitchen, ta haɗe rai ta shiga ɗaki, sai ga Gwaggo ta fito tana gyara ɗaurin zani, Maryam ta ɗauke kai kamar ba ta ganta ba, Gwaggo ta ce"Baiwar Allah za ki iya ba mu waje ko?"

Ta ce"Gwaggo ba zai yiwu a kunna gas yanzu ba, ya kamata ku fara sanin yadda abun yake kafin ku fara amfani da shi, wallahi yanzu idan aka kunna gas ɗin nan gobara ce za ra tashi gagaruma ku mutu, don haka ko za a kunna shi a yau dole sai warin iskar nan da ya fita ya baje".

Ta ce"Ke Yasmin daga yau kar ki sake gwada kunna gas ko a wani wajen, ba haka ake yi ba".

Gwaggo ta tafi ɗaki tana cewa"Oh! Ni kam Nazifi wa ya auro ne? Yau ni za a faɗawa zamani? An hana ni abinci kuma an hana ni dafawa? Ba laifinki ba ne".

Maryam ta ce"A'a Gwaggo ku zo ku kunna, sai dai na ce Allah Ya ji ƙanku, don ni yanzu zan bar muku gidanku ma".

Daga haka ta shige ɗaki, ta ɗauki akwatinta ta saka wayarta a jakar hannu ta fice, Gwaggo ta bi ta da kallon mamaki, sai kuma jikinta ya yi sanyi, ita dai ba ta ga abin da aka yi da zai saka ta yi yaji ba, "Daga kunna gas? Allah Ya kyauta" Ta faɗa tana shigewa ɗakinta.

 A ɓangaren Maryam ranta fess ta ƙarasa gida, duk da tana ɗan fargabar abin da Baba zai ce, faɗa ne ta saba da shi musamman ta wajen shi, kuma shi Baba yana da wani hali wanda yake burge ta, idan ya yi maka faɗa da nasiha a kan abu, ka ƙi yarda ko ka ƙi dainawa, shikenan sai ya ce ka fi ƙarfinsa ya zare hannu a tafiyarka, sam ba zai takura maka ka yi dole ba, shiyasa take ganin ba zai takura sai ta koma gidan Nazifi ba.

 Ai kuwa da Baban ta fara cin karo, a ƙofar gida ta same shi, suna tattaunawa da wani maƙocinsu, dama gaida manyan unguwa ba ɗabi'arta ba ce, don haka kanta tsaye ta wuce su ta shiga gidan, Baba da ya gane ta sai da gabansa ya faɗi, ya bita da kallo.

Tana shiga da sallama Uwani ta tare ta ta rungume tana cewa"Sannu da zuwa, maza shige ɗaki, ai ba neman kai muke yi da ke ba" Ta yi maganar tana jan akwatin zuwa ɗaki.

Maryam ta shiga ta ajiye hijjabinta, ta kwanta a gado, Uwani ta shigo tana cewa"Kuma Nazifin yana kallo kika taho?"

Ta ce"A'a ba ya nan, sai dai ya dawo ya ga wayam".

Uwani za ta yi magana suka ji sallamar Baba, ya ɗaga labulen ɗakin yana cewa"Wace ta shigo yanzu kamar Maryam?"

Uwani ta ce"Ita ce, zama ya ƙi daɗi, tun a daren da aka kaita suke ƙunsa mata baƙinciki ba ta huta ba".

Baba ya ce"Ban gane zama ya ƙi daɗi ba, amma dai kin manta kwana biyu da kaita gidan miji ko? Da har za ta kwaso ƙafa ta dawo ta shimfiɗa miki ƙarairayi ki yarda. Ke ta shi ki fice ki koma gidanki".

Uwani ta rafka salati har da tafa hannu kafin ta ce"Wallahi Malam irinku ne masu siyar da ƴarsu a gidan auren, ta yi ta bauta da sunan zaman aure, ai aƙalla ka tsaya ka ji me ya dawo da ita tukunna kafin ka kore ta".

Ya ce"Wane irin rashin haƙuri ne zai sa ta dawo gida kwana biyu da aure?"

Ta shiga tsara masa ƙarya da kashi-kashi, har da cewa yau ɗin Gwaggon har marinta ta yi a gaban shi bai ce komai ba, ga shi kullum sai ta yi mata tuwo, ga jikarta tana zaginta. Baba ya yi shiru yana nazari kafin ya ce"Uwani duk da hakan wannan bai kai ta taho gida, ko waya ce sai ta yi wani ya je a sasanta yanzu idan aka fahimci har ta zo gida me duniya za ta ce?"

Uwani ta ce"Ita fa rayuwa indai za ka biyewa duniya za ka ƙare a wahala ne, ina ruwanka da duniya ko mutanen cikinta, yadda za su yi suka don ta dawo haka za su yi idan miji da uwarsa sun kassara ta".

Tsaki Baba kawai ya yi, don ba ya iya doguwar ja in ja, ya fice daga gidan.

Uwani ta ce"Maryam dole fa ki buɗe baki ki ƙwatarwa kanki ƴancinki, idan ba haka ba wallahi kwasarki zai yi ya maida ki, ƙarama da ke da ƙuruciya ki ƙare a wahala da uwar miji? Duk yadda za a yi ki ce ba za ki koma ba, kar ki sake ki sare, don auren kwana biyu mene ne marabarki da buduruwa? Yanzu wani saurayin zai aure ki wanda ya fi shi komai, Allah Ya sa dai bai ɗora miki idda ba".

Ta tsare ta da ido tana jiran amsarta, Maryam ta ce"Sai dai kar a kuma".

Uwani ta ce"Ya cuce ki! Allah Ya saka miki".

Nazifi yana komawa gida ya tarar an karo ƙofar ɗakin Maryam, ga shi dai ba lokacin sanyi ba ballantana ya ce shiyasa ta rufe, sai ya raya a ransa ko bacci ta yi da wuri, duk da sai yanzu ake kiraye-kirayen sallar isha'i, ya fara shiga ɗakin Gwaggo da sallama, ta amsa ya shiga ya zauna yana yi mata sannu, ta ce"Ni kam Nazifi matarka wace iri ce? Daga magana a kan kunna gas shikenan ta haɗa kaya ta bar gidan?"

Gabansa ya faɗi ya ce"Ta bar gidan kuma?"

Gwaggo ta ce"Ka ga Nazifi ni kam zan bar gidan nan, na tabbata Auduwa bai saka ƴan haya a gidanmu ba, ka taimaka ka yi masa magana na koma, idan na mutu ni kaɗai shikenan, ko na kumbura babu wanda ya sani duk tsiya dai kafin na fashe na ishi duniya da wari wani zai shigo ya gan ni".

Nazifi ya ce"Haba Gwaggo wannan wace irin magana ce kike yi?"

Ta ce"Ka ga ka je ka dawo da matarka, gobe zan bar gidan nan, yanzun ma don dare ya yi ne, ka faɗa mata ta yi haƙuri ni ba baƙuwar zafi ba ce".

 Nazifi ya tashi ya fita jiki a mace, a ƙofar gida ya tsaya ya kira lambar Maryam, ta ɗaga ya ce"Maryam kina ina?"

Ta ce"Gidanmu".

Ya ce"Don Allah me yasa za ki yi mini haka? Me ya yi zafi?"

Tsaki kawai ta yi ta kashe wayar, ya bi wayar da kallon mamaki, bai taɓa zaton da gaske za ta iya yin yaji a kwana biyu da aurensu ba, ya mayar da wayar aljihu ya kama hanyar gidansu.

 Yana ƙarasawa yayanta Sunusi ya zo shiga gidan, suka gaisa yana ce masa"Ya Maryam ɗin? Ko wani abun za ka karɓar mata?"

Nazifi ya yi yaƙe ya ce"Ai tana ciki ma, zuwa na yi mu tafi".

Sunusi ya zaro ido ya ce"Kamar ya tana ciki? Uban me ta zo yi?"

Nazifi ya fara kame-kame kafin ya ce"Ba wata matsala ba ce, za mu sasanta".

Sunusi ya shiga gidan ransa a ɓace, ya fara ƙwalawa Maryam kira, ta tashi zaune tana harare-harare, Uwani da ta fito daga banɗaki ta ajiye buta a fusace ta ce"To Allah Ya dawo da kai! Lafiya kake yi mata kiran mafarauta? Uwar me ta kashe maka?"

Ya ce"Yanzu na ga mijinta a ƙofar gida, wai babarmu uban me ya dawo da ita tun yau?"

Ta yi masa daƙuwa ta ce"Ubanka ne! Kuma wa ya sako ka a wannan rigimar?"

Da mamaki ya ce"Rigima fa kika ce? Lallai, kenan nufinki waje za ki ba ta ta zauna? Ke Maryam!"

Ya ƙarasa yana shiga ɗakin, kamar zai dake ta ya ce"Uban me ya haɗa ku da shi, da har kika kwaso jiki kika dawo?"

Ta yi banza da shi, tana turo baki, ya ce"Ai dama na san zai yi wuya ki zauna wallahi, idan na ce da motsi a kanki sai a ce ba haka ba, to ga shi dai an fara gani, sai ki wuce ga shi can yana jiranki a ƙofar gida".

Uwani ta ce"Kai Sunusi ka kiyaye ni fa! Ka fita daga idona na rufe, ina ruwanka da zancen nan wai?"

Ya ce"Allah Ya kyauta". Ya shiga ɗakinsa.

Uwani ta saka hijjabi ta fita, ta samu Nazifi tsaye yana jira, ya tsuguna ya gaishe ta, sannan ta ce"Ka shigo daga ciki, magana ai ta wuce ƙofar gida".

Ya bi bayanta yana sunne kai ƙasa irin na surukai.

 A tsakar gida ta shimfiɗa tabarma, ya zauna sannan ta shiga ɗaki ta ce da Maryam"Ki fito, kuma saura ya yi miki kallon soyayya ki haƙura, shi fa aure irin wannan da ya fara da matsala wallahi matsalar nan ba ta taɓa ƙarewa, sai dai ta yi ta girmama, ki tsufa a haka kina shaƙar baƙinciki, idan kuma kin ji kin gani to sai ki bi shi ki koma".

Maryam ta tashi ta fito, suka zauna aka ƙara gaisawa, Uwani ta fara magana"Nazifi ka ba ni mamaki, ka yi mana bazata! Ashe kai uwarka ka aurowa ƴata ba ka yi bayani ba? Ta ya za ku rufar mata da bauta ba ta da hutu ta ko'ina? Ka ga a gidan nan ma da na saka Maryam aiki gara na yi, saboda ba na so ta wahala, a gaskiya wannan zama naku ba mai yiwuwa ba ne, tun da abun har ya kai ta fara dukanta to kawai ka sake ta kowa ya huta tun ba ku fara tara zuri'a ba".

Gabansa ya faɗi ya ce"Duka kuma? Maryam Gwaggon ce ta dake ki?"

Ta ɓata rai ta kau da kai gefe.

Uwani ta ce"To ƙarya za ta yi mata kenan?"

Ya ce"A'a kawai dai na yi mamaki ne, saboda ita Gwaggon ba ta ce mini an yi haka ba".

Ta taɓe baki ta ce"Dama mutum zai yi ya ce ya yi ne? Nazifi don Allah salun-alun ka furta mata kalmar saki, ba sai ka wahalar da shari'a ba".

Ya ce"Haba Umma wannan ai ƙaramar matsala ce wacce za a magance ta, abun bai kai na rabuwa ba".

Ta ce"Ban ga alama ba! Uwarka ce fa, ba za ka taɓa canzata ba, don haka ita ya kamata ka zaɓa ba matarka ba, yanzu idan ta kwashe maka albarka kana ganin zan bar ƴata ta ci gaba da zama da kai da rashin albarkar uwa? A'a ba zai yiwu ba, ka rabu da ita kawai shi ne maslaha".

Nazifi ya ce"A yi haƙuri don Allah, indai babata ce ta ce ma gobe za ta bar gidan, shikenan babu wani abu da zai sake tasowa kuma in sha Allah".

Uwani ta ce"To ai gata nan, idan za ta koma shikenan!" Ta tashi ta shiga ɗaki.

Ya kalli Maryam ya ce"Haba Maryam, yanzu wannan har ya kai ki taho gida? Wannan ƴar matsalar da za mu daidaita a tsakaninmu?"

Ta ce"Kai kake mata kallon ƙaramar matsala, ni kam babba ce a wajena".

Ya ce"Wannan ma ai abun kunya ne a ce har kin yi yaji, ki rufa mini asiri ki zo mu koma".

Ta ce"Abun kunya ya wuce na zuwan uwa ta zaune a gidan yara?"

Maganar ta dake shi sosai, ya ji haushi amma ya dake ya ce"To ki tashi dai mu tafi".

Ta ce"Nazifi wai da wane yaren ake yi maka bayani? Aka ce maka wannan auren ba mai yiwuwa ba ne ba fa! Don haka ka sallame ni kawai".

Ya ce"Ba dai Gwaggo ba ce? Za ta tafi ai na faɗa miki".

Ta ce"Ni ko ta tafi na fasa auren, ka sallame ni idan kana son zaman lafiya".

Nazifi ya ce"Shikenan bari na tafi, zuwa gobe idan kika huce na dawo mu yi magana".

Ta ce"Nu babu wata hucewa da zan yi, za dai ka ɓatawa kanka lokaci".

Ya fice daga gidan yana jin ransa babu daɗi.