Book 1
by @rukyelmuaz
RIKON KAKA ❦
✍️ Written by Rukyelmuaz
RMF PRODUCTION.
CHAPTER 1
YOUNG TALENTED WRITER ASSOCIATION (YOTA
BATSARI LOCAL GOVERNMENT
Da sanyin safiyar ranar asabar,
Gari yayi shiru iska mai daɗi tana kadawa haɗe da sanyi mai shiga jiki a hankali.
daga yanayin garin kaɗai ya isa ya tabbatar maka da cewa wannan lokacin damuna ne duk da kasancewar goma na safe yayi amma ka ɗauka karfe takwas din safiya ne.
Gida ne irin ginin kauye jar ƙasa daga waje amma daga ciki kallo ɗaya zaka masa kasan cewa ko a ƙauyen wannan gidan bana yaku bayi bane don daga tsarin cikin gidan kasan cewa Alhamdulillah masu rayuwa a cikin shi tabbas ra'ayin zaman ƙauyen sukayi.
Dattijuwa ce da bata wuce shekara saba'in ba a duniya ke kai kawo da gani kasan irin jikin su na mutan da ne ga kuma hutu daya samu kallo ɗaya zaka mata kasan tana cikin kwanciyar hankali da wadatar rayuwa domin kai komo take batareda gazawa ko nauyin jiki irin na mutan zamanin nan namu ba.
ƙara'r gudu da hayaniyar yara ta karaɗe gidan tun daga soro kafin su iso inda take tsaye yanda kasan sunayi ne a gabanta alhali ko cikin gidan basu kaiga shigowa ba.
Muryoyinsu suka karaɗe ko ina a cikin gidan da hayaniya.
fitowar ta kitchen yayi daidai da isowar su gaban ta. ta kalle su cikin mamaki kafin ta ce,
“Lafiya dai?
"Me ya faru kuke wannan ihu haka kuna kirana tun daga soro bazaku bari ku ƙaraso ba lafiya?”
Suka tsaya suna maida numfashi suna kallon ta haki kawai suke saboda tsakanin gudun da sukayi. bayan ɗan lokaci, ɗaya daga cikinsu ya ce cikin firgici,
“Kaka malam bala mai zikiri ya kama haisu.
ya hana ta dawowa gida tana can a cikin gona yaki bari ta taho gida".
Fuskar kaka hasatu ta canza cikin rashin jin dadin abinda suka faɗa ma ta, ta ce.
me haisu ta yi masa?
kallon juna sukayi kafin wani ya amsa ma ta abinda takeson ji.
"Wai saboda haisu ta hau bishiya ta katso mana mangoro shine ya shigo gonar yasa aka tsareta ya rike ta yaki bari ta taho gida .”
Ya karasa faɗar maganar yana kallon sauran yaran dake bayan shi suma kai suka ɗaga a tare alamar gaskiya ya faɗi,
girgiza kai tayi cikin damuwa da tashin hankali domin tunanin ta ɗaya kar a sabauta mata yar tsoka ɗaya amiya yar gudaliyarta.
“To, ku dakata. bari in saka mayafi, mu je mu ji abin da ya faru ta faɗa tareda faɗawa cikin ɗakin ta da yayi tsaf dashi komi zaune yake a inda ya dace kamar ba ɗakin dattijuwa ba.
ɗauko mayafinta, tayi ta yafa a kanta, sannan ta fito ganin ta fito sanye da mayafi ne yasa yaran duka suka juya da gudu suma, bayan su tabi domin zuwa ta ganema idon ta abinda ke faruwa.
Ba da"ɗewa suka isa gonar inda korayen ciyawu da da sauran anfanin gona sukayi gore sharr alamar damuna tayi albarka kunya suka fara tsallekewa kafin su Isa inda bishiyar mangoro din take.
Bishiya ce babba wacce ya'yan mangoro sunyi sama da ganyen cikin ta sosai wanda in ba kasa doguwar sanda ko ka hau sama ba babu yanda za'ayi ka ciro ɗaya daga cikin ƴaƴ'an cikin ta.
Magidanci ne babba sanye yake da riga yar shara da wani tsohon wando wanda daganin kayan jikin shi zakaba kanka amsar cewa shine malam bala mai zikiri, mutum ne wanda baifi shekaru hamsin, ba da kallon fuskan shi kawai zakasan yana cikin bacin rai.
Rike yake da hannun yar budurwan da batafi karfin shekaru goma sha biyar ba. fara ce wacce yanayin jikin ta kawai zakace bata cin abinci don kuwa irin yaran nan ne da koda ace suna cin abinda to ba lallai yana musu aiki yanda ya dace ba saboda dan jikin su da baifi.....ba.
Cika take tana batsewa tana karkaɗa ƙafa ita a dole yan mata anyi mata abinda bataso ga yanayin shagwaɓa na ɗawainiya da ita kanta a ƙasa don babu damuwar komi a fuskanta bace ɓacin rai na anci ma ta fuska.
Yara ne suka fara isa inda take cikin hada baki sukace "haisu yar larabawa".
Sai a wannan lokacin ta dago da fuskan ta. karamar fuskan ta da manyan idanun ta suka sauka akan wanda suka kira sunanta kafin su ƙara wata magana. kaka ta karaso gurin da suke cikin ɓacin rai ta ce.
“Malam bala, ko mene ne haisu ta yi, ai ka sanar da ni, ba wai ka tsare ta ba. me ya sa ka tsare ta haka?”
Mutumin da aka kira da malam bala ya nuna haisu da yatsa cikin fushin daya bayyana ƙara'ra a fuska dinshi ya ce.
“Kaka hasatu, wannan yarinyar ba ƙaramin tashin hankali ba ce a cikin kauyen nan da gonakin mutane ' kalli abin da ta jawo mini".
ya ƙarasa maganar yana nuna kasan gonar da ƴa'ƴan mangoron da bai gama nunaba duk ya fado birjit a kasa ya cigaba da magana cikin fada
"Ta kawo mini yaran sun taru a gonata, suna jifan juna da duwatsu, suna hawa bishiyoyi suna karya rassan mangoro Ita ce ta jagoran ce su wallahi ba zan ƙyale wannan abin ba.”
Haisu ta ɗago kanta cikin shagwaɓa ta kalli kaka a maraice kamar zatayi Kuka cikin salon shagwaɓa da kware'wa a sarrafa kalami ta ce.
“Kaka... ai mangoro ne ya biya mana rai, Kuma ba za mu cutar da kan mu ba shi ya sa muka tsinka kaɗan. ai har ladan yara zai samu saboda ya ciyar da musulmai.”
Kaka ta saki yi murmushi a hankali.
“rabu da shi ke, haisu.”
Juyawa tayi ta kalli malam bala da tuni ya sake baki yana kallon ikon Allah sangarta da la'lacewa ta wannan yarinyar maganar kaka ce ta dawo dashi daga tunanin daya ɗauke mishi hankali.
Cikin halin ko in kula take magana.
“Malam bala, ko haƙƙin maƙwabta ba ka saukewa, amma ka tsare marainiyar Allah saboda mangoro?”
Haisu ta kasa ɓoye murmushinta domin ta san indai akwai kaka a gari, to ba ta da damuwar komai.
fa kaitar idon kaka tayi ta ɗan yi wa malam bala gwalo, abin da ya ƙara hura masa wutar fushin da yake ciki na ɓarnar da suka yi masa.
Malam bala ya girgiza kai ya kalli kaka da ta gama sauke mishi hadda akan bin bayan ƙarya.
“Yanzu kaka hasatu, abin da za ki faɗa kenan duk ɓarnar da wannan shaiɗaniyar tayi min ya tafi a banza kenan?”
Ya ɗaga murya cikin fushi wanda ita kanta sarkin "barnar ta tsorata.
“Wallahi sai kun biya ni kuɗin mangoron da ta la'lata. Idan ba haka ba, zan kai ta gaban mai gari.”
Fuskar kaka ta sauya da jin furucin da malam bala mai zikiri ya yi akan jikarta, wadda ta fi so, take jin za ta iya kona garin batsari akanta zata iya faɗa da kowa har liman bataki ya mutu ba akan jikarta ta rayu ba.
Cikin ɓacin rai da furucin da ya yi, ta ce,
“Saboda mangoro za ka kai haisu gaban mai gari? wannan kam ba zai yiwu ba.”
Malam bala bai sauya matsayarsa ba.
“to ku biya kuɗin ɓarnar da tayi. Idan ba haka ba, ba zan fasa kai ta wurin mai gari ba.”
Kaka hasatu ta sauke numfashi a zuciyar ta ta ce inda kasan kudin kake so aida baka tsareta ba in akazo kace tayima ɓarna a biyaka ma biyanka zansa ayi a fili kuma ta ce..
“To, shikenan. ka saketa yanzu ka tafi anjima idan mahaifinta ya kira, zan sa ya turo kuɗin mangoron.
haisu zata ta kawo maka, ko kuma kai da kanka ka zo gida ka karɓa.”
Malam bala ya yi shiru na ɗan lokaci daga ƙarshe ya ce,
“wallahi, ki ja mata kunne kar na sake ganin ƙafarta a gonata tunda ba mutuniyar arziki bace.”
Yana kai nan a maganar shi, ya juya ya fice daga gonar, ya bar bakin kaka a buɗe tana kallon bayan shi.
Yara suka fara tsalle da murna saboda an saki haisu.
Kaka ta kalli haisu ta ce,
“Don Allah, hafsatu, yaushe za ki girma? hawan bishiya ba na mata ba ne.”
Cikin shagwaɓa ta turo baki tace
“Ni fa, ya biya mana rai ne, kuma ba zan bar ƴan tawaga ta su ga abu suna so, ban yi musu ba.”
rufe bakin ta ke da wuya, yara suka fasa ihu da murna.
Sai haisu, ƴar larabawa, “Yeeeeeeeeeeee!” cikin farin ciki da kirarin da suka mata, ta ce,
“Yara, ku faɗa ku ƙara, nice ɗaya tilo duk fadin batsari babu wata ƴar larabawa sai ni!”
Duk faɗin garin batsari, da gani , babu wata. nice nan ’ƴar larabawa. don haka yau dole ku ci kifin Isiya me dala’ilu.
Cikin gwarin gwui"war ta, na sangarta ta ce,
“ku je"
Yanzu za mu je gida da Kaka. yunwa nake ji zan samo kuɗin kifin, mu haɗu a dandalin.
Yaran na jin haka suka ƙara fasa ihu na farin ciki. masu ta ya suka ɗauka, suka gara, duka suka fita gonar da gudu.
Kaka ta ja hannun jikarta, ta fita da ita.
amma da kafiya irin ta haisu, sai da ta ɗauko mangoro huɗu, ta sa a hijab, tana tafe tana mutsu"mutsu. kaka ce ta ji tana mutsu-mutsu.
Cikin rashin yarda ta ce,
“hafsatu, me kika ɗauko?
Baki ta turo cikin shagwaɓar da aka raine ta a ciki, ta ce.
“Hakki na'ne na ɗauko.”
dogon salati kaka ta ja, sannan ta ce,
“Kin san Allah ki watsar da su ko na yi maganin ki.”
“Allah, ba zan watsar ba,” ta ba kaka amsa cikin sangarta.
Amsar da ta bata ne ya bata damar juyawa ta kalli fuskarta duk kasancewar tasan zata iya aikata abinda yafi wannan ba sabon abu bane a gurin haisu.
Kallonta tayi batare da ta ce komi ba ƙara rike hannun ta tayi sosai cikin nata yanda kasan an ce wani zai zagayo ta baya ya amshe ma ta ita.