5STARS CHRONICLE Book 2 FREEYA

CHAPTER 6

by @xayyeesherthulhumaerath

bata gama watsakewa da rayuwar gidan Adam ba. Kissing dinta Zahra ta yi kafin ta ce, "gud gurl byeebyee zan tafi skul yanzu Anty Suhana za ta zo ku kwanta, ki lura da Anitha in ta tashi kinji ko byeebyee." Tana dariya ta daga mata hannu ita ma tana mata byeebyee din. Zahra na isa night School Study Center har an fara masu karatu, Imam yana masu karatu amman sai duba kofa yake ya ga inda Zahra zata fito. Sai ko gata suna haɗa ido kamar kullum ta yi kasa da kanta amman sai sam shi ya kasa daga idonshi akanta daga karshe ma cewa ya yi, "Ma Sha Allah." Sai ya kalli sauran daliban ya ce, "Ina fatan kuna

sane da cewa in Mutum ya ga abun da ya masa kyau maimakon ihu ko wani abu *MA SHA ALLAH* ya kamata ya ce." Dukan su dariya suka yi kawai domin sun lura da kallon Zahra yake. Ita kuwa wucewa tayi kawai ta zauna. Tana kokarin ciro littafanta. Karatu ya ci gaba da yi masu,sannan ya koya masu sallah a aikace ba karamin dadi Zahra ta ji ba,nan ta fahimci cewa ashe da kawai wasa take ba ibada ba,yanzu ne zata fara asalin ibada. Lokacin tashi na yi kamar kullum ya ce, "Yau addu'ar da zan baku ta neman Soyayyar Allah ce, Addu'ar na da matukar kyau da kuma inganci ku Kasance masu yinta Aduk Lokacin da kuka samu dama,

Bismillahir-Rahmanir-Rahim *Allahumma Inni As aluka hubbak,Wa Hubba man yuhibbuk, Wal-Amal al-ladhi Yuballighuni hubbak*." Sai da masu Sosai ya tabbatar za su iya koda da gyara ma kadanne kafin aka tashi. Da farinciki Zahra ta bar cikin makarantar fiye da kowacce rana,amman tana cikin tafiya tayi karo da abun da ya mugun daga mata hankali. Yarinyace bata zarce 'Yar kimanin shekara tara ba yashe a gefen titi jini na kwaranya daga gabanta, cikin dimuwa Zahra ta karasa gareta ban da hawaye ba bu abun da ke ambaliya a fuskar wannan yarinyar domin ko sautin kukan bata iya fiddawa. Kokarin daukanta ta fara yi amman sam ta kasa, taran masu tazi ta fara tana kuka su taimaka amman da kyar wani ya

yarda ta shigar da yarinyar suka tafi asibiti.... ★★ Suna isa asibitin cikin sauri aka zo aka shigar da ita, ganin halin da take ciki yasa aka bukaci hukuma. A ruɗe Zahra ta fita offishin yan sanda mafi kusa da asibitin ta je ta sanar da su. Gaɓadaya kin kulata suka yi kowa na harkar gabansa a ƙarshe ma wani ce mata ya yi, "ko me miye ita ta so kuma ta kai kanta,zai fi kyau ki barta a inda kika tsinceta tunda ba ki san dalili ba,waya sani ma ko kisan kai tayi." Nan take Zahra ta ji zuciyarta ta harzuƙe cikin fushi ta fara magana, "wai me kuka mai da mata ne? Saboda rauninmu sai mu zam abun

wulakantawa? Na Tabbata wannan yarinyar ba za ta taɓa aikata mummunan abu ba a yanayin da take sai dai a aikata mata,me yasa ba kwa da imanine bare tausayin 'ya'ya mata? Me yasa kuka zaɓi son kan ku fiye da kowa? Mene ne ribarku a wulakanta 'Ya mace? Shin ba ka san cewa Asararran mutum ke wulakanta mace ba? What Ever abu ɗaya na ke da bukata mu je ku sa mun hannu asamu damar taba yarinyar nan a taimaka mata,ni nasan rayuwar cutarwa na ɗan ɗana na ji ta bana fata ko burin na ga wani ko wata ciki, ba don ni ba,don Allah." Ta karasa maganar tana kuka tare da durkusawa gaban wani dan sanda Jikinsa ne ya

yi sanyi ya tashi ya bita yasa hannu sai da aka fara dubata kafin ya bar asibitin. Nan take likitoci suka hau kanta domin yin abun da ya dace. har aka gama yin Treating Yarinyar Zahra na tsaye a ƙofar ɗakin da aka shigar da ita, tana kai kawo, gabadaya hango rayuwarta kawai take, Mussamman ranarta ta farko a gidan Adams, wanda ya yi mata komai son ransa,hawayen da ke idanunta ta share a zuciyarta tana fadin, "ba zan bari ba,in sha Allah in dai ina raye ba zan bari rayuwar wata 'Ya mace ya wulakanta ba,ban fidda rai kan cewa zan iya taimako ba,kamar yadda ake taimaka mun a yanzu." fitowar likitan ya tsaida mata zancen zuci, ta je

gareshi da hanzari, ya buƙaci ganinta a ofishinsa, bayani ya yi mata kan cewa fyade aka yi wa yarinyar ba da son ranta wanda har hakan ya kusa zame mata matsala wanda da ba azo Asibiti kan Lokaci ba za ta iya kamuwa da cutar yoyon fitsari. Jim Zahra ta yi tana matukar jin radadin aranta Likitan ne ya kara katseta da fadin, "Yanzu zan baki takarda kije pharmacy ki karbo mata magani, suma tayi kuma anyi mata allurai da ta farka in ta ci abinci za ta dawo hayyacinta sai da yan raunuka da basu warke mata ba,zata fuskanci zafi don haka tana buƙatar kulawa ta mussaman." Karba Zahra ta yi, tana fita ta duba kudin hannunta ta duka

wanda ta ajiye akan za ta siyawa Anitha madarar da ake bata. Murmurshi ta yi kawai ta nufi pharmacy din,ta basu takardar suka fada mata kudin sannan ta biya suka bata maganin. A hankali ta tura ƙofar ɗakin ta shiga, bacci take yi har lokacin, banɗaki ta shiga ta ɗauro alwala ta gabatar da sallah raka'a biyu,bayan ta idar ta yi ƴan addu'o'in da ta iya sannan ta fara maraji'an karatun Al-qur'ani, motsin da ta ga yarinyar na yi ne ya sa ta tashi ta ƙarasa gareta. Temaka mata ta yi ta tashi zaune sannu ta yi mata, idanunta ta ɗago ta kalli Zahra, kawai sai ta fashe da kuka me tsuma zuciya, tausayinta ne ya ƙara lulluɓe Zahra, yanayin

kukan da take yi kamar ranta ze fita ne ya sa cikin karyewar zuciya murya a sanyaye Zahra ta fara lallashinta tare da fadin, "na ganki yashe a gefen titi hakan yasa na kawo ki asibiti,ki yi hakuri ki daina kuka,ki fada mun abun da ya faru in sha Allah ba zan cutar da ke ba ni kam kinji ko?" da ƙyar cikin muryan sheshsheƙa ta ce, "Wajen aiki nake,Mamana , Babana basa da kudin da za su ciyar da mu ni yan Uwana, sunana Husnah a ƙauye muke da zama, shi ne wata mata taje neman ma'aikata akan za a dunga biyan babana duk karshen wata shi ne aka turoni nan nake aikin share-share a wani company da ke

nan, mu takwas ne yara kamar ni, a kullum Oganmu cikin wasa yake da jikinmu sai ya sa mu duka mu tuɓe yana shafa mana gabanmu yana lashewa,muma ya ce sai mun sha gabansa in ba mu sha ba kuma ya ce zai kore mu, a kullum cikin dare abun da yake yi da mu kenan bama barci, mu tsirara shi tsirara haka zai haɗa mu waje guda kowacce da inda zai nuna mata ta yi, duk aciki ni ce kawai ban taɓa bari ya kusance ni ba, in ya zo sai in fara kuka ina rokonsa in ya ce in sha gabansa na sha Shikenan sai ya Barni, jiya kuma ya ce shi ba wannan yake so ba kamar

yadda yake shigan sauran ya zama lallai nima sai ya shigeni, na yi kokarin guduwa na kasa, sauran yan uwana yasa suka danneni har sai da ya yi abun da yake so, ban kara sanin inda nake ba sai yanzu da na ganni anan." Kara fashewa ta yi da kuka mai taɓa zuciya. Zahra ta rungumeta tana fadin, "ki daina kuka kin ji,ki daina,kina so a daukan miki mataki? Kina so a kwatan miki 'Yancinki?" Girgiza kai Husnah ta yi kafin ta ce, "Ba ma ni kadai ba har da yan uwana na cen,kullum cikin kuka muke saboda ba ma so,muna tsoron fada ya kore mu kauye kuma in mun koma kauye ba za a yarda ba ,za ace karya

muke a karshe iyayenu su watsar da mu,burinsu kawai mu nemo masu kudi abasu ba su da mu da ya muke anan din ba." Zahra ta ce, "Shikenan zuwa safiya za mu je offishin yan sanda sannan za mu je har garinku,za mu shigar da mutumin nan kara kuma sai na Tabbataar iyayenku sun fahimci gaskiya, yanzu ga cake nan da Drink ki sha sai ki sha magungunan nan na ki." ★★ Gaɓadaya hankalin madam Zuby ya tashi domin ta kira wayar Zahra baya shiga ga shi har safiya ta yi. Zahra kuwa suna tashi bayan an sallamesu suka nufi offishin yan sanda. Kara ta shigar akan Alhassan Ogan su Husnah. Mamaki ne ya kama dan sanda yadda Zahra ke

abu da kwarin gwiwa ya ce, "kin san wa kika shigar kara kuwa? Kin san da wa kike kuwa? Babban dan kasuwa ne mai companyn Petrol a kasar Indonesia, ba na jin kin dauko abun da za ki iya." Murmurshi Zahra ta yi ta ce, "bana da kudin karawa da shi,amman tabbaas ina da zuciyar karawa da shi,kuma ban fidda tsammanin cin nasara ba a ko ina kuma a ko yaushe ko da shi waye kuwa indai zai yi ba daidai ina da damar karawa da shi,indai zan ga kyawun da ke cikin karamar flower tabbas ba zan fidda tsammani ba." Ya ce, "Ok fatan alkairi." Zahra ta ce, "Na gode sosai yanzu zan je da ita, zamu dawo kafin

ku neme mu in sha Allah." Zahra ta karasa maganar tare da sanya numberta da signing. Suna fita gidan abincin madame zuby suka fara bi saboda ta mata bayani,kuma ta duba su Anitha. Suna zuwa Madame zuby ta ce, "Lafiya kuwa duk hankalinmu ya tashi ga Anitha nata kuka ta ma ƙi shan madaran gwanda Anushka tana guna muna tare tunda na ce mata zaki dawo tayi shiru." Zahra ta ce, "Madam ba komai wallahi ina cikin tafiya zan dawo kawai na yi karo da wannan yarinyar cikin wani yanayi." Ta ƙarasa maganar da nuna Husnah. Kafin ta ci gaba, "Fyaɗe aka yi mata wanda har ya kusa zamto mata matsala, mun je asibiti har ofishin yan sanda munje na

shigar da kara yanzu za mu je ƙauyensu ne inyi magana da iyayenta akwai matsala sosai a Rayuwar nan Madam." Numfasawa Madam Zuby ta yi ta ce, "Ba abun da zan ce da ke sai fatan alkairi, Allah ba ki Nasara adukkan lamuran da za ki sa gaba." Zahra ta ce, "Amin na gode sosai Madam zan dau Anitha kawai tunda taki daina kukan muje kauyen tare." Madam ta dauko wani dan canjin kudi ta mikawa Zahra tana, "Ga shi nan, kuyi ko da kudin mota ne nasan ba kudi a hannunki." Zahra ta karba tana Godiya ta goya Anitha suka fice tare da Husnah. Kauyen su Husnah suka nufa kai tsaye. ★★★Khalil na barci kamar a cikin mafarki Noor

ya zo yana sa masa abu a kunne. Motsawa ya yi,ya juya yana tsaki. Noor ya kara lallaɓawa yana kara tura abu cikin kunnen. Khaleel yasa hannu ya toshe kunnuwansa ya ci gaba da barci. Noor ya ce, "Dad ka tashi, na ce ka tashi yunwa na ke ji,i need food oh oh." Cikin magagin barci Khaleel ya ce, "Noor ka bar ni in huta mana." "Aa aa Dad ka tashi." Noor ya fada. Tashi zaune Khaleel ya yi yana murza ido. Noor ya ce, "Alhamdulillahil-lazi Ahyana ba'adama amatana wa'illaihin nushur." Murmurshi khaleel ya yi kafin shi ma ya maimaita. Tare suka sauko akan gadon da kayan barcinsu iri ɗaya suka nufi toilet,zasu shiga tare suka furta, "Allahummah Inni a

uzu bika minal khubusi wal khaba'isi." Tukun suka shige ciki. brush Noor ya dauko masu Ya mikawa khaleel yana, "Oya Dad brush ur teeth, ko in wanke ma? Kamar ma ba ka iya wankewan ba." Karba khaleel ya yana, "Noor Surutun ka kullum yawa yake,see ur mouth,yaushe ka fara iya yiwa kan ka bare ka mun barni inyi abun da ke gabana." Sai da suka yi brush Khaleel yama Noor wanka kafin shi ma ya yi. Khaleel na fitowa ya ga Noor ya fito masa da kaya takalmi da komai wanda zai sa. Shi ma ya ciro nasa irin na Khaleel sak. Noor ya ce, "Dad su za mu sa ko?" Khaleel na goge jiki da towel ya ce, "Yes

boo zaɓinka shi ne nawa." Kayan suka sa dukan su,ba karamin kyau su ka yi ba, Mussamman Noor yadda kayan ya yi daidai da jikinsa. Turare ya dauko ya fesawa Khaleel tukun ya mika masa ya ce, "Dad nima fesa mun." Fesa masa Khaleel ya yi yana, "Good boy." Noor ya ce, "Good Dad." Dukansu suka yi dariya a tare. ★★ ★★Suna isa kauyen Zahra ta yi ma iyayen Husnah bayanin komai har ma iyayen sauran yara bakwai din Amman ta sanar da su cewa kada su fitar da maganar kada kowa ya ji, za a dawo masu da yaransu gida kuma za karba masu 'yancinsu. Zahra ta kara da cewa, "Babu amfani ga nuna son rudin duniya fiye da

inganta rayuwar 'Ya'yanku ada ina kallon cewa Yaran da basu da galihu da tsayayyen dangi ne suke fuskantar hakan ashe harda masu iyaye? Bai wajaba kan yayanku kan cewa su nemo su baku ba, muddin kuna da karfin neman ,ko da maxa ne bare kuma mata? Ku zauna da mazajenku Amman ku tura yaranku neman kudi? Shin kun san abun da za su fuskanta acen? Wannan ba rashi bane son zuciyane kawai,ko da zaku nemi kudi ku nema kuna tare da yaranku indai kuna da imani kan cewa Allah zai buɗa maku,babu shakka za ku samu da taimakon Allah da kuma jajircewarku, ko da wasa ka da dukiya ta sa idanunku su rufe ku miƙa jininku zuwa ga rayuwar karnuka,

ku ta shi tsaye ku nema da kanku ku inga rayuwar ku da ta yaranku domin gobenku ta yi kyau." Gaɓadayan su jikinsu ya yi sanyi,sun rasa abun fada har da masu hawaye, hankalinsu ya tashi matuka Mussamman sauran iyayen da suke tunanin ko wani hali ma yaren nasu ke ciki oho. Duka sun amince da kudirin Zahra kuma suna goyon bayanta dari bisa ɗari. Suna komawa station aka sanar da su ankira wo shi kuma ya tabbatar da cewa Kazafi shi ake masa don abata masa suna, don haka zai daukaka kara zuwa kotu. Zahra na jin hakan gabanta ya yi mummunan faduwa, amman kuma sai ta ji zuciyarta da tunatar da ita cewa, "ka da ki taɓa sarewa

adukkan aiyukankan Alkairi da za ki sa agaba, in dai baki fidda rai da tsammani ba tabbas zaki tsammaci abun da baki yi tsammani ba." Dariyar da yan sandan offishin ke mata na keta ne yasa ta saurin dagowa. Hawayen da ya ke kokarin sauko mata a idanunta tayi saurin gogewa nan take ta tsinci kanta da sakin wani Murmushi wanda ita ma bata sam dalilin sa ba. Wani ne acikinsu ya ce, "kar ki damu za a kawo miki sammaci har gida,tunda har sai da kika taro abun da yafi karfinki kike jin dadi." Murmushin ta kara sakewa tare da rike hannun Husnah ta ce, "Eheen hakan shi ne mafita ya fi sauki ai, Allah kawo ku lafiya, nasara

ta na ga wanda ya dogara da gaskiya da Ubangiji ai." Cikin kwarin gwiwa take fadin hakan har ta fice a offishin. Gidan abinci suka wuce domin ta riga ta sanar da iyayen husna za su zauna tare har sai komai ya daidaita. Tana zuwa tayi wanka ta huta,tayi sallah suka ci abinci duka. Ta kara ba Madam Zuby labarin kauyen Su husna da kuma offishin yan sanda. Wayarta ta dauko tana dannawa tunani yazo mata kan cewa dole fa sai sun dauki lawyer, aranta ta ce, "wa na sani? Wa zan dauka kuma a ina zan samu kudaden wannan aikin?" Kauda kai kawai ta yi ta ce, "Allah kawo mana mafita," nan ta kunna datarta ta shiga shafin Instagram.

Kwatsam ta ci karo da wani posting wanda Ibrahim Khalil ya yi. "STRUGGLE MAKES YOU, YOU STRONGER Imagine if you got what you want every time,no struggle,no hard working,no challenge,no HARD WORK required. Some of you are saying that would be great, YOU WOULD BE WEAK. And then when something hard come across you up in your life you wouldn't know how to handle it, because you never gone thought anything, that STRENGTHENS you, You can't GROW without STRUGGLE, You can not develop STRENGTH without RESISTANCE, without CHALLENGING YOURSELF, without STRUGGLE,Pain is your friend,maybe not in the moment,but for the evolution of your soul,for the LONG TRAM benefit of YOU,as a STRONGER human being, PAIN is Your friend. If you

didn't have FAILURES If you didn't have STRUGGLES If you didn't have DISAPPOINTMENTS You could have STRENGTH no COURAGE,no COMPASSION How could you? These Qualities are made from your PAIN and STRUGGLE. You were given pain because you are strong enough to handle it. You were given this life because you are strong enough to live it. Fair is only for fictional movie. But Reality is the struggle." Tana karantawa sai take ji tamkar da ita yake ko kuma don ita ya yi. Nan take Zahra ta yi following dinsa tare da reply kamar haka. "Some days i struggle, Some days i cry, Some days I'm holding onto all the pieces just so i can feel whole,On the days where

i feel like I can't go on i remain myself, that I've made it, through everything,that was meant to break me." Khaleel na ganin comments dinta tunda ya karanta yake wasi wasi aransa, "Tabbas daga jin wannan batun kai tsaye daga zuciyarta take furtawa har can ciki, na tabbata tana da tabo mai girma a rayuwa amman ba ta gaza ba ta ci gaba da jajircewa, wannan tana ɗaya daga cikin Mutanen da nake nema, tafiyar mu za tai daidai kuma za ta iya bada ma'ana, saura mutane Uku." Da haka ya katse tunanin sa,shi ma ya yi following dinta, sai da ya je ya duba dukkanin bayanan da ta daura ya kara jin karfin gwiwar kasancewa da ita kafin