17
by @gureenjoh
AL'AJABIN SO
(heart touching story)
بسم لله الرحمن الرحيم
FATIMA MUHAMMAD GURIN.
(Gureenjo)
ADABI WRITERS ASSOCIATION
Marubuciyar:
*Zuhraa*
*Hamrah*
*Igiyar Rayuwa*
*Noor Iman*
*Ruwan Sama..*
*Lelewal*
*GAMON JINI paid*
*Kowa Ya ga zabuwa..*
*Diddigar ƙaya... Paid*
*Rubutu a kan ruwa... Paid*
And now..
*AL'AJABIN SO*
*BOOK 1*
*Page Seventeen*
"Me kuka aikata Nawwaz? Akan me zaku yi raping yarinya alhali kun bar yammata sama da hamsin waenda suke shirye da tayin ku? Why? Why??"
Gabaɗaya hankalin shi ya tashi irin yadda ba'a zato, su karan kansu sun shiga mamaki, sun ga dae har a ƙasar da ma ya fi Nigeria tsaro da komai yayi raping yarinya wanda ma sanadiyar zamanshi prison kenan har aka kore shi ya dawo Nigeria da karatu, to me zai dame shi anan da ma ba lallai a bi diddigi ba ko ma an bi suna da kuɗi wadda sun tabbatar a ƙasar nan zai musu maganin komai.
Ganin suna kokarin tursasashi maida komai ba komai bane yasa ya daka wa smart tsawar ya tsayar da motar kuma su fitar mai daga cikin mota, haka ya baɗe idanunshi da toka sai da suka fita ya zagaya ya figi motar kaman baya son ranshi, har lokacin wani irin tension yake ji a cikin jikinshi gidanshi ya ƙarasa a parlor ya zube, ya rasa ma kalar tunanin da zai yi me yaran nan suka aikata haka?
Bai san iya adadin lokutan da ya ɗauka a haka ba, a hankali ya buɗe idanunshi da suka sake shanyewa wayanshi ya zaro ya duba sai ya ga biyu saura, contact ɗin shi ya shiga ya samo Layin Maami ya zubawa idanu, a hankali abinda be taɓa zaton ze yi ba a rayuwarshi tun tashin shi wato hawaye ya cika idanunshi, damuwar da yake ciki yana son jin ko da muryarta ne kila ya samu sassauci, kira ya danna mata ya zubawa wayan idanu ba lallai ta ɗauka ba, dab zai tsinke ta ɗaga, a hankali ya sa a kunnen shi ya ji muryarta cikin bacci tana furta
"Assalamu Alaikum warahmatullah Mukhtar? Lafiya?"
Idanunshi ya runtse hawayenshi suka zubo, a hankali yace
"Wa'alaikissalam warahmatullah Maami..."
Sai yayi shiru ya rasa ma me zai ce mata, bayan duk abubuwan da ya mata a rayuwa ya kuwa chanchanci ta taya shi shiga damuwa saboda damuwar shi?
"Uhmm ya aka yi? Menene?"
Uwa kenan, ya faɗa a ranshi yana sake jin wasu sabbin hawayen sharr, zuciyarshi na wani irin chunkushewa cikin tsananin damuwa da karaya, gaɓɓan jikinshi duk sun yi sanyi saboda rashin natsuwa da bashi dashi gabaɗaya kwanakin, har zafi zafi yake ji a cikin jikinshi kaman me masassara.
"Maami ina cikin damuwa ne, na kasa bacci, na kasa samun natsuwar zuciya na rasa abin da zan yi na ji daaɗi, ki taimake ni please"
Wani abu taji ya tsarga mata har cikin ranta, Allah sarki uwa bata san ta miƙe zaune ba, a hankali tace
"baka da lafiya ne? Ka je asibiti?"
Girgiza kai yayi
"Maami lafiyata ƙalau kawai komai ne baya min daaɗi Maami"
Shiru tayi na seconds kan a hankali cikin son tabbatarwa tace
"ka sha wani abu ne da ya fi karfin ka ko?"
Da karfi ya runtse idanunshi dama ya san zata yi tunanin hakan, kuma ya ji a jikinshi ba zasu taɓa fahimtar nadama da tuban shi a kusa ba, yayi mamaki ma da ta saurare shi, a hankali yace
"Maami wallahil azeem rabona da in sha wani abu tun ranar da muka zauna gaban baba"
Nannauyar ajiyar zuciya da har ya ji daga inda yake ta sauƙe.
"Ka je kayi alwala ka faɗawa Allah matsalolinka in shaa Allah zaka samu natsuwa"
Kai ya gyaɗa kaman karamin yaro kan yayi mata godiya suka kashe wayan a tare, Miƙewa yayi ya nufi ɗakinshi har ya shiga sai kuma ya tsaya kaman me nazari, wardrobe nashi ya nufa ya duba ya ɗauki three quater da wani armless Black shirt tare da sabon towel ya fice daga ɗakin don be yarda da ɗakin ba har wani kyamar ɗakin yake ji.
Ɗakin Alaya ya shiga lumshe idanu yayi yana sake jin sabon hawayen tausayinta, anan ya mayar da ita prisoner a cikin wannan ɗakin ya shigo ya jata gaban abokai ya ɗura mata abin maye ba tare da ya damu da cewa ita ɗin tsarkakkekkiya ba ce, bayin ta ya nufa yayi wanka ya sanya kayan ya zo ya tsaya kan sallaya, a hankali ya ji Muryarta a sadda take ce mai a lokacin da ya ɗauketa daga asibiti zuwa Hotel zai yi sallah.
"Ya Mukhtar namiji fa daga cibiyar shi zuwa guiwowinshine al'auranshi, Kaga zaka yi sallah kuma wandon be kai guiwa ba be kamata ba"
Yana iya tuna yadda take mai magana a lokacin ma cike da tsoro.
Ɗakinshi ya koma jallabiyar nan da Dr ya taɓa bashi kyauta ya ɗauka ya saka kan kayan ya dawo ɗakin ya kabbara sallah cike da Fatan Allah ya amsa ya sassauta mishi abin da yake ji yana damunshi.
***
"Ki buɗe"
Abin da taji kenan da ya sanya gabanta dokawa.
Cikin rawar murya tace
"Abba? Lafiya?"
A harzuke yace chan ƙasa
"na ce ki bude kofar nan"
Hannunta na rawa ta buɗe da sauri ta ja baya ganin ya afko ya rufe
"ke! wace irin mutum ce ke? Dama Alhassan ya min gargadi duk inda kuke babu alkhairi a tare daku musamman ma ke, kin san me kike shirin aikatawa?"
Girgiza kai tayi tana jin tashin hankali na bijiro mata.
"Zaki kashe auren macen da ta taimake ki ta taimaki mahaifiyarki ta so ki tsakani da Allah, kin mata adalci kenan? Kin san me uban su ya fi tsana? To babu abin da ya ƙi jini a duniya irin saki, barin ma na ƴar cikinshi, me kike tunanin zata fuskanta ta koma ga mahaifinta tsofai-tsofai da ita da takardar saki?"
Zuwa wannan gaɓar tuni hawaye ya wankewa Alaya fuska, sai ta ji murnar karatunta ya koma ciki, in tayi wa Maami haka bata kyauta ba, sai dae ina zasu je? Ya zata yi da ummin ta?
Kaman ya shiga zuciyarta yace
"Zan ba ki makudan kudade da zai ishe ku rayuwa, kuyi nesa da mu da rayuwarmu dama Mukhtar ba soyayya tsakaninku zan sa shi sakin ki a gobe ku yi nesa da mu na har abada"
Kanta ta mayar ƙasa hawaye ya silalo mata.
"Kin amince?"
Kai ta gyaɗa a sanyaye
"daga yau bana so ki sake kwanar min cikin gida a gobe zan sallame ki"
Yana kai nan ya juya ya buɗe kofa ya fita, a wurin da ya barta ta sulale ta zauna tare da fashewa da kuka, sake tura kofan da aka yi ne yasa tayi saurin ɗagowa a firgice ta miƙe tsaye!
****
Mahaifin wannan yarinya da aka yiwa fyade ne ya riƙe hannun Yayanta dake kuka kaman ranshi, a hankali cikin lullube tsananin tashin hankalin shi yace
"karka taɓa ta Bashir, barta bari na ƙira dan uwana"
Cousin nashi ne comissioner of Police iyayensu mata sun haɗa uba, kuma kusan kaman abokai suka tashi Dukda tazarar arzikin ubanninsu ya banbanta nesa ba kusa ba, ringing uku ya dauka
"Ɗan Uwana yau kuma da mu aka tuna?"
Hawaye ya sirnanowa dattijon cikin karaya yace
"Ɗan Uwana wannan kiran na neman agaji ne, ka taimakeni ina da da bukatar ka a yanzu, an wulakanta ni an tozarta rayuwar ƴata an illata min yarinya"
Hankalinshi ya dugunzuma ya tashi jin dattijon na kuka sossai, tabbacin gashi nan ya bashi da ambulance bayan jin mummunan ta'asar da aka yi mata.
Ba'a fi awa ɗaya ba sai gasu har lokacin daga baba har Bashir an rasa me ba wani haƙuri sai kuka suke yi, da ambulance da wasu polisawa aka zo, Allah sarki yarinya abin tausayi haka aka ɗaga ta zuwa motar asibiti da wasu Police mata ya haɗa su inda ya tsaya gun ɗan uwanshi don jin kanun zancen.
Be ɓoye mishi komai ba duk ya faɗamai har da plate number ɗin, kwarai ya jinjina kokarin baban a take a daren suka soma bin hanyoyin da duk za'a bi don gane me wannan motar, abin ka da comissioner of Police ne ke ciki tsundum ba'a kira assalatu ba sai da aka gano motar Mukhtar ce, su ba ɓoyayyun mutane bane, don haka a take ya bada umarnin a je a kamo mishi Mukhtar dama kuma yana da ajiyayyen record a interpol, me hali ba zai taɓa fasa hali ba, maza maza a kawo shi.
Makara yayi, a sadda ya buɗe idanunshi yaji ana sallama a masallaci, da sauri ya miƙe be tsaya wanka ba yayi alwala ya taho ya zo yayi sallah, anan ya zauna duk wasu Adu'o'i ba wai ya iya bane tunda karatun islamiyyar shi na je ka na yi ka ne yayi, zafin mahaifinshi yake ji har ranshi, yana tuna a lokacin in an bugeshi ya ce ba zai kara zuwa ba Maami na masifa haka Abba zai baɗe idanunshi da toka ya bashi goyon baya kuma ya hana shi sake zuwa sai ranar da ya ga dama, yana tuna har a gida an sha kawo malamai musamman don shi yana korarsu da sharri kala kala Abba be taɓa cewa hakan ba daidai bane, be taɓa gyara mishi ba, be taɓa tsawatar mishi ba...
Door bell ake ta dannawa wanda hakan ya sa ya miƙe yana duba time, shidda ma be cika ba lafiya?"
Yana isa ya buɗe sai idanunshi suka sauƙa kan polisawa kusan guda biyar dake tsatsaye gaban kofan parlorn they are even armed gasu manya manya, murmushin takaici yayi dama ya san hakan na iya faruwa, sai dae kuma gabanshi dake ta faɗuwa da tsoron halin da zai jefa Maami da Alayah idan maganan ya riske su, karamin ciki ne da ita idan yayi sanadin shi fa? Sai yanzu yake jin wani irin son abun cikin nata na shiganshi, bakin Police ɗin ya zubawa idanu a sadda yake cewa
"Mukhtar hammad you are under arrest for the suspect of rape, u have the right to keep quit as anything you utter will be Proof against you in d court"
Hannayenshi ya dunkule ya miƙa musu suka sanya ankwa, sai da suka fito ya ga ashe akwai wasu zagaye da motar da ya dawo dashi jiya, daga shi har motar aka ja sai Police station.
*Kuyi hakuri da Page na yau, ban wani zauna bane. Thank you*